《SHIN SO DAYA NE? (Complete)》LAST CHAPTER
Advertisement
*💘
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION*
*{Onward together}*
*{ we give the reader's of ours the best out of the best's,, our inks are melodious And dropping a kinda light's to reader's}*
'''THE PEN OF LOVE 😘 HEART TOUCHING ❤ TEARS OF SORROWS 😭 CURDLES 😊 GIGGLES 😁 AND MARRIAGE THINK 💑'''
*JUST GIVE US FOLLOW.....*✔
*
*
*
*
*
*ra🎉*_
a📱*_
*🌼
Bayan Mahmood ya kammala waya da Momi,cike da tashin hankali ya dubi Fadima wacce tayi matashi da kanta asaman cinyarsa,itama hankalinta tashe ganin yanayin mijinta ya sauya ah sa'ilin da yake waya.
"Dear nah what happened? Wani ne ya mutu?" na fada cike da fargabar amsar da ze biyo baya.
Murmushin leb'en baki kawai yayi yace"Momi ce ta k'irani take fada min cewar Mubarak ya dawo don haka mu hanzarta xuwa kano yanxun nan kuwa,so Zahmood tashi muje ayita ta kare da zazzafin nama........"
Ya fadi hakan tare da mikar da kanta,ya tashi tsaye.Ni kuwa duk wani na'ura meh aiki ajikina ya tsaya cak!,alokaci daya naji duk wani kuzari dake jikina ya kau,idan ka kasa kunnuwa kuma kana iya jiyo yadda xuciyata ke bugawa da sauri da sauri non-stop.
Har ya kusa shiga dakinsa sae jikinsa ya bashi cewar bata biye dashi,da sauri ya waigo,tana nan de inda ya barta,sae binsa take da kallo,kwayar idanuwan nan nata dauke suke da tsantsar tashin hankali.Jikinsa ne yayi sanyi qalau,Sam baya son ganinsu cikin tashin hankali haka,amma kuma toya ya iya?dolene dama su fuskanceta koba jima koba dade,kuma insha Allahu daga yau za'ayi ta ta k'are don ba tsoron Mubarak din yake ba.
Sannu ahankali ya taka xuwa gareta,ya tsugunna tare da dafe gwiwowinta don zaune take saman kujera.
"Zahmood dear nah...... " ya fadi hakan cikin wani irin siga ta salon soyayya.
Ni kuwa kamar dama jira nake ya fadi hakan,sae kawai na rusa masa kuka meh daga hankali.beyi yunkurin hanata ba,seda tayi meh isarta don kanta tayi shiru ta koma 'yar shesshek'a.Can ya janyota ta fado jikinsa,ya lalubo lips dinta ya shiga tsotsarsa don kawai ya dan rage mata damuwar data shiga ciki.
Nima din biye masa nayi cuz I can't hold it back,bazan iya jurewa ba.saida yayi meh isarsa sannan ya cikani,ya riko hannuna tare da mik'ewa yana fadin"Oya let's go..... "
Kokarin magana nake sae naga yayi saurin sanya 'yar yatsarsa saman lips dina,yace"Shhhhhh! Zahmood don't say anything again,Idan har kina sona then ki taho mu tafi muje ayita ta kare yau...... "
Runtse idanuwa nayi ba tare da furta komai ba,banyi aune ba kawai naji ya kinkimeni yayi daki dani,shida kansa ya saka min kaya,don ada daga ni sae wata yar shimi da bone shot ce,shi kuwa threequarter da kuma singlet.ya dan shirya mana wasu kayan acikin wata 'yar karamar akwati wai zamuyi weekend gaba daya ne acan,dayake yau jumma'a ce.Nide jinsa kawai nake da kuma binsa da kallo don gabaki daya hankalina baya jikina.Cikin kankanin lokaci muka kama hanya bayan na k'ira Umma nace mata mun tafi weekend kano,fatar alheri kawai ta mana.
Advertisement
***
_*✨KANO✨*_
Mubeen da Usee,sae kuma Hanan ne kadai xaune afalo,sunyi shiru kamar wasu kurame,Hanan ce kurum ke 'yar shesshekarta.Daya da daya matan ke shigowa ahargitse cikin kuma tashin hankali,kowacce Idan ta shigo sama-sama take gayar dashi sannan ta nufi dakin Momi.Ganin kowacce na shigowa fuska sam babu annuri akai yasa hankalin Mubeen tashiwa.'Yar wasar da suke da yayarsa Meema akodayaushe yau babu ita,hasalima sama-sama ta gaishesa kana ta wuce dakin uwarta da sauri-sauri.
Akalla yanxu an shafe kusan mintuna talatin kenan da zamarsa anan wurin yana jiran momi,amma shiru-shiru taki fitowa suyi maganar datace zasuyi,sae ganin yan'uwansa mata dake ta shigowa yake wanda hakan ya bashi tabbacin lallai an buga an sanar musu da dawowarsa ne shine suka taso suka zo,kuma yanayinsu ya tabbatar masa da cewar lallai babu lafiya,dakwai abinda ke kasa wanda suke tsoron gaya masa Kai tsaye.ya yanke shawarar k'ara mata wasu mintuna talatin din,wanda ze kama 1hr kenan,Idan har kuwa 1hr din ya cika kuma bata fito ba,toh kuwa shi zeje ya sameta ta gaya masa abinda ke faruwa.
shesshek'ar da Hanan keyi sosae ya soma isarsa,afusace ya dubi inda take yace"Wai zaki yiwa mutane shiru ne ko kuwa? Kin de san arayuwata na tsani kananan koke-koken banza ba tare da dalili bako?tukunna mah de meh aka miki kike kuka? Huh gaya man? "
At once ta tsaida shesshek'ar,ta shiga jifarsa da kallon mamakin wannan sauyawarsa daga dawowa wai kuma duk akan Fadima wacce bema san cewar wansa ya aureta ba,yanxu muddin ya sani kuwa toh abin ze ninka wannan ninkin ba ninkin kuwa,wani dan marayan kuka ne taji yana nemar kubce mata don ita arayuwarta ta tsani ganin Mijinta cikin tashin hankali.
Murmushin leb'en baki kurum ya sakar mata ganin tana shirin sakin wani kukan,shi kansa yasan he's harsh on her wanda har ya lura mamakin hakan take,he juz have to act so don Momi ta tsorata da yanayinsa har ta bari ya auri Zahransa.
"Jiddanah pls stop crying lyk little Jasmin owkay?" Ya fadi hakan cikin muryar lallashi.
Gyad'a masa kai tayi da sauri-sauri tamk'ar wata 'yar yarinya,alokaci daya ta hadiye kukan.
Kallonsa ya dauke daga gareta ya maida xuwa ga Usee wanda ya rafka uban tagumi da dukkan hannayensa,yayi nisa sosae cikin tunani don ko abinda Mubeen ya gayawa Hanan beji ba.
"Lil fada min,anyi mutuwa ne shine kuka kasa fada min sae inda-inda kuke tayi?huh?"
Wannan tambayar ta Mubeen shine ya dawo da Usee cikin hayyacinsa,gabansa ne yaji ya bada rasss!,axuciyarsa yace"Ina ganin dama mutuwar ce akayi da zefi sauki akan wannan tashin hankalin da ake shirin fuskanta..... "
Kafin yakai ga bashi amsa sae ganinsu Baba Mu'azzam sukayi da matarsa da kuma goggo Ladidi wacce ya biya ya daukota sun fado dakin hankali tashe,hijab din goggo ladidi mah bata sakashi dede ba.Abin kamar hadin baki sae gasu Momi dasu Meema suma sun fito don sunga shigowarsu cikin gidan ta window.
Advertisement
Yanayinsu ya saka hankalin Mubeen kara tashiwa akan nada,sama-sama ya gaishesu suka amsa masa,kana kowa ya samu wuri ya zauna.
"Toh kode wani ya mutun ne? Ina brother Mahmood yake?tunda abin yaga na taron dangi ne,toh Ina shi yake?" Tambayar da xuciyarsa tayi masa kenan,kafin ya sake yin wani tunani yaji kawai Baba ya katse masa hanxari.
"Mubarak ina son ka bani aron hankalinka da kuma tunaninka anan,ina son ka natsu ka saurari jawabina...... "
Ji yayi gabansa ya yanke ya fadi,amma se ya daure yace"Na ara maka su duka Abba.... "
Yace"Madallah nagode,wato Mubarak tabbas kowanni dan'adam akwai irin jarabawar da Allah ubangiji madaukakin sarki yake yi masa domin gwada cikar imaninsa,ba kuma dan Allahn shi be sani bane yayi masa wannan jarabawar,a'ah Allah yasan komai,se de shi Allah yana yin jarabawar ne domin mu da bamu san abinda ze faru nan gaba ba.Haka kuma Allah madaukakin sarki yana yin jarabawar ne domin k'arama bawa da kuma kaishi wani matsayin da ayyukansa na ibada baze kaishi ba har abada,amma ta wannan jarabawar,idan bawa ya cinyesa,sae akaishi matsayin da ayyukansa be isa ya kaishi ba,wannan jarabawar fa dolece,don Allah madaukakin sarki yana cewa acikin alqur'aninsa meh girma acikin suratul Ankabut,yace_*"
Dakatawa yayi yana duban Mubarak wanda ya nutsu sosae yana sauraren jawabinsa,kuma ya lura duk jikinsa asanyaye yake,kila zece wai meh tsohon nan yake shirin gaya min ne da har yake min wannan tunatarwar?
Goggo Ladidi itace ta soma nata jawabin"wato sae ka yarda da kaddara meh k'yau ko mara k'yau,ka yarda da cewar duk abinda ya sameka daga Allah ne,asannan ne zaka zamo mumini meh imani,toh ni Kam nace,idan har komai ya zama daga Allah ne,meh k'yau ko mara k'yau,meh dadi da mara dadi,kuka da dariya,samu da kuma rashi,nasara da kuma akasinta,toh kuwa komai abin godewa ne,abin karba ne sannan kuma abin alfahari ne,sae mu amsheshi muyi farin ciki,muyi godiya ga Allah,sae mu amsa k'iran Allah(SWT) da manzonsa(SAW),muyi haquri mu kuma sallama mu mika duka lamuranmu ga Allah madaukakin sarki,Yah Allah ka bamu ikon cinye duk wani jarabawar da zaka mana,da wanda kake mana da kuma wanda kayi mana,ka temakemu karmu fadi jarabawar don alfarman gwaninka annabi Muhammad........ "
Gabaki daya kowa ya amsa da"Sallallahu alaihi wa sallam.... "
ahankali Mubeen ya budi baki ya soma magana"Abba wai duk meya kawo wannan tunatarwar ne?ku fada min ko wani nawa ne ya rasu shine kuke tunanin idan har kuka gaya min toh ina iya tada hankalina shine kukayi tunanin kwara ku soma da min tunatarwa?Yah Mahmood ne ko kuwa Zahrata? "
Babu wanda beji gabansa ya fadi ba jin cewar direct ya ambaci sunayen culprits din nasa,shiru akayi na tsawon wani lokaci,shi kuwa ya baza kunnuwa yana bin kowa da kallo daya bayan daya,yana meh jiran yaji wani ya budi baki ya bashi amsar tambayarsa.
Runtse idanuwansa yayi yana meh tunano abinda Hanan ta gaya masa dazu,maganar tata ce take masa kuwwa akunne,ji yake kamar yanxu take masa maganar.
_*"Haba mijin hauwa'u yanxu har xuwa wannan lokacin baka cire Zahra aranka ba?aganina ya kamata ka shafeta acikin rayuwarka because I think Zahra ta maka nisa ba kadan ba........"*_
Karde hakan na nufin Zahra ta jima da mutuwa shine ta gaya masa hakan?kode dalilin daya saka dan'uwan nasa yake ta raina masa hankali kenan har kuma ya dena daga k'iransa kawai don kada atada masa hankali ko ya shiga cikin wani hali?
**
Seda muka soma biyawa gidanmu muka ajje akwatinmu sannan muka kamo hanya xuwa family house.seda kuma Mahmood yayi da gaske kafin ya samu na shiga gidan,ganin ransa ya soma bacewa ne ya saka kawai nayi shahada muka shige.
Gabana ne ya hau dukan chalugude asa'ilin da muka kusanto entrance door.Cak! na tsaya,naki gaba haka kuma naki baya,Mahmood ne ya juyo yana dubana,yace"Zahmood yadai?"
"Dear nah am not ready to face Mubeen,idan na shiga ince masa meh?ni matar wansa ce? Wallahi I can't........ "
Axuciye yace"Shikenan Fadima tunda ban isa na saki abu kiyi ba,ba damuwa kina iya yin duk abinda ranki ya keso...... " ya shige ciki abinsa ya barta nan tsaye.
Da hanxari na take masa baya,adaidai lokacin kuma Mubeen ya bude idanuwansa yana fadin"No! No! No!!! Fadima Zahra tana nan araye bata mutu ba....... "
Kowa ya bishi da kallon mamaki jin furucin daya fito daga bakinsa,jin shigowar mutane ne ya maida hankulansu ga kofar shigowa.
Babu wanda beji gabansa ya tsananta faduwa ba ah sa'ilin da kallonsa ya sauka kan halittun da suka shigo.Zumbur! Mubeen ya mik'e ya nufesu,cike da farin ciki yake fadin"I knew it,wallahi na fada zahrata bazata tab'a tafiya ta barni yanxu ba........ "
Rungumar Mahmood yayi yana murna,yace"Brother an k'ira an fada maka na dawo shine kayi min wannan big surprise din ta hanyar kawo min my Zahra ko?tank u very much amma meyasa ka dena daga call dina Idan na k'ira? "
Shi kuwa Mahmood wani uban d'aci ne yaji aransa ah sa'ilin da mubeen ya k'ira Zahmood dinsa da 'Zahransa',ai yanxu Fadima tasa ce shi d'aya.
"Brother say something mana,wai meyasa Kowa ya maidani mahaukaci ne?tun dazu naketa tambaya amma Kowa ya maidani shashasha,wai meke faruwa ne da har ake b'oye min?"
Cikashi yayi ya nufi Fadima wacce take tsaye bayan Mahmood dukkan ilahirin jikinsa rawa yake tamkar wacce ake kad'awa gangi.
"Zahrata nasan ke kadaice zaki iya fada min abinda ke faruwa,sabida irin son da kike min shi ze saka bazaki iya b'oye min komai ba,so now tell min wat's happening? "
Baba shine ya taso ya kamo hannun Mubeen ya mai dashi mazauninsa yace"Mubarak zauna ayi magana ta fahimta... "
Ya dubi inda su Mahmood ke tsaye yace"Mahmooda kuma kuzo ku sami wuri ku zauna...... " suka bi umarninsa.
Advertisement
- In Serial34 Chapters
Chimera
A chimera slowly regains memories of its past life as a human in a nonmagical world. While he is in part James Borland, temp office worker who was on the verge of being converted to permanent, he is also a savage beast who gains strength by consuming flesh of various creatures. The more he remembers, the larger the effect his old persona has on his actions, which is often at odds with his instincts as a beast that seeks only to consume prey to become stronger. Updates: Chimera will updatetwo to three times each week. Disord server: https://discord.gg/WT4J9hg
8 178 - In Serial12 Chapters
Honor of the Dead
Necromancy is forbidden. He knew this, and yet he allowed himself to be raised from the dead. He agreed to a deal without knowing the terms, all for the hope of seeing those most important to him. Who knows if he ever will?
8 266 - In Serial9 Chapters
Gameworld
Twenty years ago something had happened. The land and everything in it had changed. Magic was real and Technology was limited. New Races arose from the old and everyone was brought to an even playing field. Everyone starts at level 1 and levels up from there. Most folks will choose their class by level 5 and begin to grind out higher levels as they struggle to survive. Omachiw was different, half human and half elf he had been raised by the Elves he had once hunted. With no class and no family, he has become a jack of all trades, trying to survive in a world that had turned into a game. Based in part in the city of Regina in the Province of Saskatchewan Canada. This is a gritty urban fantasy story with horror elements set in a game world.
8 237 - In Serial19 Chapters
Emotiv
New Adult | Dystopia | Speculative | Slipstream | Science Fiction Kyla has finally broken into the Worker class of Skycross. But when she is cast aside by society and witnesses the plight of the Abandoned, she must make a choice between her own future, and the wellbeing of thousands, before she loses her grip on reality. Author's Note: Serial Novel, new parts to release every Wednesday -- I'm writing this as I post, so I'd love to hear your feedback and thoughts on where the story might lead! I have a vague plan in mind but I'm excited to try out this process of posting as I go :)
8 155 - In Serial250 Chapters
Advent of the Mindfire Mage: A Challenger's Return Story
Updates MWF, 6PM EST! Not so long ago, a story was posted on Webnovel, one that fired my imagination unlike almost anything before or since. It was known as The Challenger's Return: Rebirth of the Rainbow Mage. However, 150 chapters in, the author NightWind, who I'd personally interacted with and begun to consider a true friend, vanished from the internet without a trace. And so, I have acted upon my fervent desire to pick up his torch, to refuse to let his world that stirred such passion in me die. Read below about my own take on The Challenger's Return. Was Lheticus summoned to the Tower by chance, or by choice? Either way, with the new power he wins, he won't hesitate to burn anyone who seeks to keep him from his true love to cinders, and with a unique ability of the highest potential, he may just succeed, but he's just as likely to burn himself down. And as it turns out, the latter case may be woven into his very destiny...can that destiny be changed? And if it is, what will be the repercussions for the Tower? (You may want to read a fair amount of the original Challenger's Return before starting this, as, particularly in the early chapters, many things that are laid out in it are glossed over in this story.)
8 226 - In Serial31 Chapters
To Heaven Hell and back. (WolfxVampxHybrid boyxboyxboy)
Benji- vamp Luke- wolfJamie- hybrid Benji and Jamie are mates. Jamie meets Luke, Luke is mates with Jamie, and with Benji. Luke only ones one mate, Jamie. Luke wants to get rid of Benji but can't kill him as it will kill Jamie and him aswell. Now Luke wants to mate him. Will everything Benji went through hold him back from his mate. And will his physical and mental changes he had to adapt from his life under the dictation be too much for his two mates and him. Or will he accept Luke and mate him for life."Trust takes seconds to brake, years to build, and forever to repair"-unknown
8 118

