《SHIN SO DAYA NE? (Complete)》PART 2:CHAPTER NINE
Advertisement
*💘
📖✍*
'''THE PEN OF LOVE😘 HEART TOUCHING ❤ TEARS OF SORROWS 😭 CURDLES 😊 GIGGLES 😁 AND MARRIAGE THINK 💑'''
so da Allah yabar qauna da zumunci
💥💥
*
*
Wuraren 7:10 Fadima ta farka daga nannauyar baccinta,k'arar ruwan wankan Mahmood dake zuba ak'asa ne ya tasheta.Ahankali nake bin dakin da kallo,dakin namiji kenan babu ruwansa da tara kayan k'warmasai,komai tsaf-tsaf dashi,dakin dan gayu kenan,sae wani daddad'ar kamshin turaren daki ne ke tashiwa,gaskia Mahmood akwai tsafta da kuma son gayu.lalubo wayata nayi dake ajje gefen filon da nayi matashi dashi,niyyata na latso Suhaima don ranar da Abba ya maida min da wayata,toh ita kuma aranar ya damk'a mata sabuwar dalleliyar waya.
Ban kai ga latso layin nata ba kawai naji Mahmood na kiciniyar bud'e kofar bathroom.Da sauri na maida wayar na ajje don bana son yaji duk wani abinda zamuyi discussing da ita.idanuwana fes akansa sanda ya fito,daga shi sae 'yar gajeriyar wando wato 'boxers',hannunsa rik'e da wani k'aramin towel yana tsane kansa dashi.Da sauri na runtse idanuwana tare da dauke kallona daga gareshi don tunda nayi wayau ni de ban tab'a ganin namiji balagi ahakan ba.
shi kuwa ya lura da yanayin data shiga,wato dai bata ji dadin ganinsa ahakan ba kenan.Murmushi ya saki tare da jefar da jikakken towel din agefe,Sannu ahankali ya taka sadaf-sadaf cikin sanda xuwa gareta ba tare da ta sani ba don har yanxu idanuwan nata arufe suke.Cak! ya dauketa kamar wata 'yar baby.
Ni kuwa saurin bud'e idanuwa nayi jin wani bak'on al'amari ajikina wato ayau jikina yayi gogayya dana baligin namiji,don sosae ya rungumeni ak'irjinsa kamar wanda baya son ak'wace masa ni.
"Please dear nah meye haka? don Allah ni ka saukeni.... " na fadi hakan kamar xan saki kuka.
Murmushi meh sauti naji ya sake kawai ba tare da yace min uffan ba.Be direni ako'ina ba sae acikin bath tub.
Yace"oya Maza ga ruwan wanka nan na hada miki kiyi,idan kuma so kike ni na miki toh shikenan.... "
Zaro idanuwa waje nayi"sae kace wata 'yar baby? No ka fita pls xanyi da kaina.... "
Ahankali yace"Ai ke din babyn tawa ce.... " ya kashe min ido daya,kana ya juya ya lakuto min maclean akan brush sannan ya miko min,ya janyo min wani dan babban towel dake rataye akan kofar bathroom din tare da azawa saman wata igiya,yace"Ga towel nan idan kin gama sae ki dauro.... "
Kafin nayi wata magana ya fice tare da rufo min kofar,ni kuma mamakinsa nake,taya za'ai nama fita da wannan dan towel din ya ganni ahakan?gaskia nifa bazan iya ba
Wani b'angaran xuciyata yace"Toh wai ba mijinki bane? Idan bazaki iya fitowa ya ganki ahakan ba toh ai se ki kwan aciki..... "
Ah sanyaye na soma wanke bakina ba.Shi kuwa yana fita,dakinta yayi,yaje ya zab'o mata wata 'yar atampa meh red pattern da adon flowers blue,daya daga cikin kayan daya bada aka dindinka mata su kenan anan kanon.Doguwar rigace 'A shape' wacce gabaki dayan gaban an mata kwalliya ne da shining stones.
Komowa dakin yayi ya dire mata shi asaman gado,kayan kuwa yasha guga har wani fidda kyalli yake.Shi kuwa diban kayansa yayi ya nufi dakinta don jin alamun kamar ta gama wankan amma fitowace ya gagareta.Acan yayi shirinsa cikin kananan kaya as usual,kayan sun k'arbeshi sosae.
Ni kuwa na gama wankan harna daura towel din amma fitowace ta gagareni don kunyar had'a idanuwa dashi nake ahakan,towel din ko gwiwata bata gama kaiwa ba.Can de nayi shahada na murd'a kofar bathroom din na bud'e ina dan lek'e-lek'e.Ai kuwa naci sa'a ban ganshi adakin ba.Da sauri-sauri gudu-gudu na fito naje na sanyawa kofar dakin key wato na rufeta don kada ya shigo.
Advertisement
Man shafawa,powder,lipstick,turare,kwalli,underwear,bra da kuma kayan sawa na gani zube asaman gado.Cikin zafin nama na sarrafa komai,na shafa komai ah inda ya kamata na shafa.Can na saka innerwears dina,sannan na warware kayan da zan saka,doguwar rigace meh k'yau sosae kuma kayan ya bani sha'awa.Da sauri na zura,nayi mamaki sosae yadda kayan ya zauna ajikina kuma ya amsheni.Nayi daurin dankwalina meh k'yau,kana na feffeshe duk wani lungu da sako na jikina.
Ni kaina na tsorata da haduwar da nayi,sae jifar kaina nake da Murmushi ta madubi don nasan muddin oga yayi ido hudu da wannan wankan toh tabbas yana iya zaucewa.Zuwa nayi na bud'e kofar dakin,amaimakon na fita waje,a'ah sae dawowa nayi na zauna agefen gado ina wasu 'yan kame-kame kamar wata bak'uwa.Ni da gidana amma na kasa sakewa.
Shi kuwa ya bata lokacine donta shirya dakyau,after like twenty minutes ya nufi kitchen,ya had'o kayan breakfast akan wani tray sannan ya nufo dakin.
Da sallama ya shigo,da sauri na dago kai na zuba masa idanuwa.
"Wowwww! yanxu Mijina ne wannan hadaddan? " na fadi hakan araina,sannu ahankali idanuwana suka sauka akan abinda yake rik'e dashi.
Da hanzari na mik'e na nufeshi,shi kuwa daskarewa yayi awaje d'aya yana kallona ya k'asa furta ko da kalma d'ayace agareni,sae yi yake kamar ze hadiyeni.K'arban tray din hannunsa nayi nazo na ajja ak'asa.
"Wowwww! seriously is diz M.Nakowa's wife?Babyna kinga yadda kika fito sharr! dake kuwa?agaskia ba don za'ace nayi son kai ba toh da kuwa nace matata is the most beautiful creature in this world..... "
Xancen nasa sosae yayi min dadi,kokarin magana nake sae gani nayi ya katse min hanzari ta hanyar sanya 'yar yatsarsa akan leb'ensa"Shhhh! matata pls don't deny,juz believe me ke din k'yakk'yawace.... "
Ahankali na furta"mijina kaima din k'yakk'yawan ne ai.... "
Cike da farin ciki ya furta"Allah da gaske kike matata ina da k'yau?"
"Har mah ka fini,fari ne de kawai xan nuna maka.... "
B'ata fuska yayi sosae yace"Ki dena cewa na fiki k'yau don ba gaskia kika fada ba.... "
Zan musa masa yace"Shhhh! it's okay let's have breakfast am hungry my wife.... "
Nace"shine baka tadani na hada mana ba kai kayi da kanka? " na fadi hakan ina d'an bubbuga kafafuwana akasa.Kallona yake dauke da sha'awata ak'wayar idanuwansa.
Yace"Yanzu shikenan saina tada sarauniya tana baccinta meh dadi? Ni idan mah zaki yadda zan fison ace na dunga miki bauta,naki kawai kici,kisha,kiyi ibada,kwanciya,ki kula da mijinki ta b'angaren hakkinsa,sannan kuma sae haifa mana k'yakk'yawan 'ya'ya kamarki,naki kenan...... "
Cike da kunyar jin maganganunsa na duk'ar da kai kasa,russunawa nayi har kasa nace"Mijina ina kwana? Ya jikin naka? "
Matsowa kusa dani yayi,ya russuna kamar yadda nayi yace"Bazan amsa ba,yanxu ne gari ya waye mana har kika ganni? "
"Kayi haquri don............... "
Wani irin k'arar bubbuga kofa muka jiyo,kofar da zata sadaka da sashin namu.Bugu ake bana wasa ba wanda hakan ba k'aramin razanamu yayi ba musamman ni wacce saurin mik'ewa nayi jiki na karkarwa kamar wacce ruwan Sama yai wa dan banzar duka.
Ji mukayi ance"Mahmooda kana iya?Maza ka hanzarta bud'e mana k'ofa..... " da k'arfi aka fadi hakan.
Arayuwata na duniya harna mutu baxan tab'a manta meh muryar nan ba,muryar *' kenan.
Atsorace nace"Mahmood ba muryar hajiyarka nake ji ba? "
Cike da tashin hankali yace"Wallahi kuwa itace..... "
Kuka na fashe dashi nace"Mahmood kaga abinda nake ta jiye mana amma kai kaki ka gane ko? Yanxu na tabbata taji labarin auranmu ne shine tazo da wannan tashin hankalin,wai kai azatonka zancen aure yana b'oyuwa ne?toh ni dai gaskia banzo da shirin fuskantar tashin hankali agidan aurena ba,dududu mah yau kwanana daya rak! da tarewa shine har zan soma fuskantar.......... "
Advertisement
Karar girgiza k'ofar da ake ne ya katse min maganata,can aka ce"wai Mahmood baya jina ne ko kuwa so kake na sanya spare key na shigo? "
Agigice nace"Look Mahmood dear u juz hav to do something Cuz am not going out there to face her & her humiliations..... "
Yace"okay abinda nake so dake kawai ki tsaya anan,ina fita kiyi saurin sanya key ki rufe k'ofar..... "
"Okay" kawai na furta.Ya juya ya fice,ni kuwa fadawa kan gado nayi,wani dan marayan kuka ne naji yana nemar kufce min,ai kuwa da sauri na sanya hannu na rufe bakina har da matseshi sosai wai don kada kukan yayi nasarar kufcewa.
Ahankali na furta"Yah salam! meke shirin faruwa dani ne?"
Shi kuwa Mahmood yana bud'e kofa,babu b'ata lokaci Momi ta tureshi gefe,suka samu suka shige ciki gaba d'ayansu.
Cike da fargaba Mahmood yace"Momi........... "
Da sauri ta daga hannunta tace"You are not allowed to utter any word,you hav the right to remain silent till am done with my investigation........ "
Da k'arfi tace"Khairat wai meh kuke jira ne? Let the investigation commence immediately,ku bincika min duk wani lungu da sako na cikin dakunan gidannan,idan har kuka ga wani abinda be dace ba toh ina son ku hanxarta fitar min dashi nan,ina fatar kun gane abinda nake nufi? "
Khairat da Labeebah ne kawai suka amsa mata da "Mun gane Momi.... "
Ita kuwa Meema samun wuri tayi ta xauna,dama shi Usee tuni ya nemi gu ya zauna.Khairat ce ta nufi hanyar ainihin dakin Fadima,ita kuwa Labeebah dakin Mahmood ta nufa inda anan ne Fadimar take.
Dundu Momi ta saukarwa Meema agadon baya tana fadin"Shegia zaki tashi ne kiyi abinda nace ko kuwa sae naci ubanki? Banza kawai mara kishin uwarta..... "
Da sauri Meema ta mik'e tana turo baki gaba cike da haushin wannan bak'on halin na uwarta.hanyar wani daki ita kuma ta nufo don yin bincikenta.
"A'ah Labee dakata anan,karki kuskura ki shiga wannan dakin,na yarje muku da ku binciki kowanne amma banda wannan duk da cewar ban san abinda kuke bincike akai ba amma karde ashiga wannan...... "
Haka suka ji Mahmood ya fad'a babu alamun wasa atattare dashi.
"Dan kutumar ubanka har kai ka isa na bada umarni sannan kai ka take ka hana?yaushe aka haifeka? Ko mantawa ne kayi da wacce take tsaye agabanka take kuma bada wannan umarnin?idan kuwa mantuwar ce kayi toh ina meh tunatar dakai cewar Haj.Fatima Binta Mu'azu mahaifiyarka ce........."
Ta juya ga Labeebah wacce duk ta gama tsorata da yanayin yayan nata shiyasa taki gaba"Maza Labeebah shige ciki ki min bincike ko kuma ni nazo nayi da kaina...... "
Saukar da ajiyar xuciya yayi bayan ya tuna cewar ai ya sanya Fadima ta rufe k'ofar.
Ni kuwa ina daki ina jin duk wani abin dake wakana afalon,jikina sae rawa yake don tsananin tsoro,xuciyata kuma kamar zata fasa k'irjina ta fad'o waje don fargaba.Ina jin umarnin da aka baiwa Labeebah,da zafin nama na mik'e don tunawa nayi da cewar ban rufe k'ofar ba kamar yadda ya umarceni da nayi.
Ban kai ka isa k'ofar ba sae gani nayi ta fad'o dakin,fuska sam babu ko digon annuri akansa.Da mamaki take nuna ni tace"Fadima you?budurwar Yah Mubarak? Meh kike anan? "
Cike da fargaba na daure nace"Ni ba budurwar Mubarak bace.... Am *'matar *'
Cike da tashin hankali tace"Shut the hell up!! karya kike,taya za'ai ki zama matar Yah Mahmo?kuma....."
"Malama investigation aka sanyaki kiyi ba interrogation ba,don haka you have no right to question me,nice nan abinda be dace ba abincikenku,so kindly arrest me,tambayoyi kuma oganki ce keda right ta min bake ba.... Let's go...... "
Na lura sosai jikinta yayi sanyi da kalamaina,shige gaba nayi na batta tsaye kamar gunki tana bina da kallo.
Shi kuwa Mahmood yana ganin Labeebah tayi nasarar shigewa dakin,ya furta "Yah salami! Shikenan ta faru ta k'are,ruwa ya k'arewa dan kada...... "
Wuf! Momi tayi ta Mik'e ah sa'ilin da tayi ido hudu da Fadima sa'ad,ita kuwa Fadimar 'yar kissa sae jifar Momin take da Murmushi.
Russunawa har k'asa nayi nace"Momi kune da sassafe haka? Sannunku da xuwa,ina kwana? "
Cike da mamaki Momi tace"Ke saurara min nan!!.... Meya kawoki gidan nan kuma meh kikeyi acikinsa? "
Fuskar mamaki nima na shimfid'a mata kana nace"Momi Kamar ya meh nake yi agidan nan? mace da gidan mijinta kuma har sae an tambayeta abinda take acikinsa?....... "
Kafin Momi tayi wata magana Khairat ta k'arbe wacce fitowarta kenan daga dakin Fadima kuma duk taji abinda ake fada tace"Wai ni ban gane xancen da ake ba anan,dodon kunnuwana sunki su yadda cewar wai Fadima budurwar Yah Mubarak ce matar Yah Mahmoh..... " (duk sun shaidata don gabaki dayansu an kaita wajensu sun gaisa alokacin da suka kai ta'aziyyar rasuwar mahaifinsu).
Momi ce tace"Ban san meh yarinyar nan tayiwa ya'yana Maza ba da har suke rawar kafa akanta,Mubarak ya wulakanta 'yan'uwansa akanta,yanxun kuma wansa ya aure masa wacce yake haukar akanta,wannan cin amanar da meh yayi kama?"
Juyawa tayi ga Mahmood tace"Munafiki,ashe da gaske din ne kayi aure shine ka b'oye min har baban Zali ya shige maka gaba,Mahmood meh na maka da har ka zab'i ka b'oye min al'amari meh girma haka?"
Murmushin takaici tayi,kana ta cigaba"Koda yake da gani ba yin kanka bane,asiri ce tayi tasiri akanku daga kai har dan'uwan naka...... "
Afusace nace"Mahmood why are u silent?why can't u open ur mouth and defend me? Meyasa bazaka fad'a musu ta yadda akayi ka aureni ba? Ka tsaya kurum ana zagina alhalin am innocent?shin haka mukayi dakai?..... "
Khairat tace"Labeebah wai meh muke jira ne da bazamu soma cin ubanta ba? "
"Ahir dinku! kada wata 'yar iska acikinku tayi gangancin tab'a matata,idan kuwa hakan ta faru toh wallahi sae na lahira yafi yarinya jindadi.... "
Tasss! Kakeji Momi ta wanke masa fuska da mari,tace"Ai dole ka fadi hakan tunda asiri ya gama cinka,Shima baba Mu'azzam din yanzun nan zanje naji dalilin daya saka ya shige maka gaba Sannan naci masa mutunci daga shi har zuri'arsa,ku kuma ku jira dawowata akaro na biyu don ban gama daku ba....... "
Ta juya gasu Khairat tace"Ku taho mu tafi..... "
Ta fice abinta,Khairat tace"U are welcome to Nakowa's family,duk wani tashin hankali is awaiting you in diz family..... "
Labeebah kuwa cewa tayi"will soon be coming back for you,a betrayer kawai..... "
Mahmood yayi wani mahaukacin taku biyu zai damkosu,ai kuwa da hanzari suka fice da gudu.Ita kuwa Meema meh k'aryayyan xuciya kamarni nan Hafnan har ta soma xubar da kwalla.
Tace"Yah Mahmo,Anty Fadima don Allah kuyi haquri,ga shawara idan zaku k'arbeta,kawai ku biyomu gidan Baba Mu'azzam din ayita ta k'are... "
"Nifa idan zasu bi ta tawa kawai subar garin if not wallahi yanzu kuwa suka soma ganin tashin hankali"acewar Usee.Wani uban harara Meema ta kwasheshi dashi tace"Kai dai wallahi baka da correct thinking of a man,shiyasa Momi ke kiranka da *'
Kafin yakai ga bata amsa kawai yaji Momi na kwala masa k'ira,da sauri ya fice yana meh cike da jin haushin abinda yayar tasa ta fad'a masa.
Mahmood ya saukar da ajiyar xuciya yace"Meema jeki gamu nan tahowa.... "
Da gudu-gudu ta fice don kada taci ubanta ahannun Momi.
Ni kuwa kuka nake sosae kamar raina ze fita,yanxu atunaninsu asiri nayiwa Mahmood kenan ya aureni ko meh?
"Fadimata pls tashi mubi bayansu... " haka naji ya fad'a yana meh kokarin yafa min mayafi ajiki.
Axuciye nace"babu inda zani,ni kawai ka bani takaddar sakina...."
Dakyar da sudin goshi da kuma wasu 'yan dabaru nasa ya samu ya lallasheta har ta haqura ta yarda zata bishi gidansu baba Mu'azzam din................ 📝
A/N
Yanzu meh kuma ze faru gidan baba Mu'azzam? Ku biyo
Sorry for the late post,wallahi was kinda busy ne yau!!
*
Advertisement
- In Serial131 Chapters
Wandering The Multiverse! Saving The God?
“Ah, when did things get mixed up this much. Damn that Deaf God couldn't even send me to the right world. Why was I even reincarnated in a world that I have no understanding of?! I asked him to reincarnate me on a TV show which I actually knew about and was a fan of! Damn, now how will I live in this world? All I do is wander in Multiverse. Mostly Anime Worlds I heard, but I never watched. Now I have to visit all of those worlds, with my intelligent system, named The Crow. He guides me and helps me, but there is more to it. When I was getting stronger, all of the sudden I targeted by a group called Templars. As I later found out they also traveled from other world and come to the same world to learn strong techniques, so their God, can be more efficient in the next Annual Universal God Tournament. I was at beginning of my journey and oblivious to the worlds I visit. My intelligent system was keeping me in dark. Do I also get stronger for the God reincarnated me? Am I chosen?" This is mostly an anime fan-fiction novel. The MC is oblivious to the Anime Worlds he jumps into. The story jumps from one world to other. Some of the popular novel worlds also part of the story. The MC first went to the Naruto World but is presently in the One Piece world. But, he will be back! Next Anime World will be Hunter x Hunter !!
8 92 - In Serial99 Chapters
The Mortal Acts
The Mortal Acts is an epic progression fantasy with a lower focus on training aspects and a great focus on discovering new ways of using powers intelligently. I've always been drawn to stories where characters use their powers creatively to overcome opponents and obstacles, and I think all the possibilities can provide a great playground for twists and turns. It's inspired by a variety of media, including Will Wight's Cradle, Hunter x Hunter, and Bioshock, so if you like the creative power use elements from those, come check it out. This is my first serial, and please feel free to leave comments and feedback. For backstory, behind-the-scenes, and other fun stuff, come chat on my discord! Become a patron to read up to 20 chapters ahead here! Blurb: Riven Morell cuts short his regular life at school and home when his mother falls terminally ill. Desperate to find a cure, he travels to Severance Frontier, a desolate land haunted by hordes of ghosts, witches, and demons collectively called the Deathless. But a miraculous cure doesn’t magically fall into his hands. Things are worse in Severance Frontier than Riven had assumed. Ghosts are banding together into armies, demons are kidnapping anyone who strays out of settlements, and witches are enslaving everyone left and right. Riven, of course, gets embroiled in the mess. Missions to curb the Deathless activity are one thing, but when it starts to look like this is just the beginning of a war that extends beyond the mortal realm, Riven has a hard time focusing on why he came to Severance Frontier in the first place. His mother is inching towards death with every passing day, but if he doesn’t face down the Deathless, what little civilization the Frontier holds will be overrun and destroyed. Thankfully, it looked like the Deathless might just hold the secret of the elusive cure.
8 256 - In Serial13 Chapters
The Choice
‘Should we be loyal to an unjust ruler?’ This is the dilemma before the citizens of Magadha . They ask themselves - ‘Is it safe to be a fence sitter?’ ‘Is it prudent to emigrate?’ ‘Is it time to rise in revolt?’ No citizen is immune, each must make a choice! Disclaimer: All events, people and some places in this novel are fictitious. Though the novel is set in 5th Century AD , India, the life presented is an amalgamation of different eras and imagination. Infact , much of the understanding of the society at that point of time has been gained from Kautilya’s Arthashastra which was first written seven centuries earlier.
8 81 - In Serial7 Chapters
Geneseed
Farnezian only wished to perfect his slaves, but Princess Darva, Grand Wizard of Space, required the superior blood of genetically enhanced beings, and only Farnezian, Grand Wizard of Slavery, could give her what she wanted. As a loyal subject of the Dark Empire of Zabulen, Farnezian couldn't go against the Princess, and so, he had no choice but to aid her.In the deep, dark, and warm caves of the Empire, an unholy ritual was performed, but Darva's folly led her experiment to end in catastrophic failure, dragging Farnezian into the fallout.When he came to be, he found himself in another world along with a half-dozen naked people, but his slaves and Darva were not among them. Men and women in antiquated armor or flimsy magical robes knelt before the naked, confused group, hailing them as the saviors of their people.But the only people Farnezian ever saved were the slaves he bought and engineered into perfect beings.--What to expect: villainous lead that does disgusting things to disgusting people. VERY SLOW pace, but not as slow as Rupegia. Male/female, female/female, and rarely male/male sex scenes.Update frequency: rarely as this is my backup story, so I'll only write for it when I have time and energy.
8 130 - In Serial78 Chapters
War of The Disciples
In a world of races with the gift of controlling the elements, a war rages between the races of light, the luxcians, and the dark, the tenebrage. In the midst of this a young tenebrage recruit, Umbren, is eager to fight for his people, but after a small mistake leads to his whole unit being wiped out, his world gets pulled into chaos. Umbren is enlisted, by Lord Mortis, as part of a group to hunt down the men who butchered his unit, but he still struggles with guilt over what happened. Now Umbren must find the reason why he fights, be it revenge or for his own glory. Though this journey is not what it initially seems as he can't appear to ever escape his own misfortune when he is taken in by a luxcian household when he becomes injured. Follow Umbren's struggle as he uncovers the truths within himself and the world he thought he once knew.
8 192 - In Serial7 Chapters
Zhanyi Xianwang Oneshots
Oneshots. Irregular updates.No smut.May contain mpreg.
8 230

