《SHIN SO DAYA NE? (Complete)》PART 2:CHAPTER EIGHT
Advertisement
*💘
*{Onward together}*
please kindly touch the little star to vote me before you start reading_
🌼
Kaina naji yana wani irin mugun sara min,babu shiri na tsaida kukana completely tamk'ar anyi ruwa an dauke.Daukar k'aramar filon wata two seater nayi,ahankali na sauko na kwanta ah k'asa tare da yin matashi da filon.Duk tunane-tunanen Mahmood ne yabi ya addabi xuciyata da kuma tsananin son sanin halin da yake ciki ahalin yanxu.
Ban wani jima da kwanciya ba wani nannauyar bacci yayi awon gaba dani.
_*"Fadima Zahra'u kinki ki rungumi kaddararki amatsayinki ta 'ya musulma kamar yadda aka koyar daku karban kaddara mai kyau ko mara kyau,amma ke kinki karbar taki kaddarar,nayi miki baiwa da kuma ni'imar da bah kowacce 'ya macece zata sami hakan ba,amma ke kin butulce min,kinci mutuncin mijinki tare da yi masa illa bayan kin san cewa babu abinda yakai Miji daraja agun duk wata d'iya mace,d'a namiji shine shugaba kuma shine jagoranki xuwa aljanna idan har yaso,adalilin sab'a masa da kikayi ya sanya na yanke miki hukuncin shiga wutar jahannama.......... "*_
Ah firgice na farka daga wannan mummunan mafarki tare da fashewa da kuka,atsoroce nake fadin"Yah Allah wallahi na tuba ka yafemin,Wlhy na k'arbi kaddarata,na haqura xan xauna da mijina,zamuyi zaman lafiya kuma xanyi masa biyayya har xuwa k'arshen rayuwata dashi aduniya,bazan sake ci masa mutunci ko kuma na sab'a masa ba,Yah Allah ka yafe min *'
Ji nayi an d'an tab'oni ta baya,ai kuwa da k'arfi na sake ihu tare da waigowa babu b'ata lokaci,jikina sae karkarwa yake tamk'ar meh jin sanyi.Mahmood ne,banji shigowarsa ba sae de kawai naji saukar hannunsa ajikina.Shi kuwa ya dawo alokacin tana baccin mamakin nata,kafin yakai ga zama akan kujera yaji kawai ta tashi afirgice tana wannan sambatun nata,atake ya gane cewar mummunar mafarki tayi,kuma ze iya bugar k'irji yace bilhaqqi yaji dadin wannan mafarkin nata don kamar hakan ya sanya ta haqura ta rungumi *'
Haba my baby doll,da salati da kuma addu'a abaki ya kamata ki tashi dashi ba wai da ihu ba..... " ya fadi hakan ahankali kamar ze had'iyeta don so.
Sae ayanxu na tuna cewar salati da kuma addu'a ya kamata ace nayi ba wai ihu da kuma sambatu ba.Shi ya soma karanto min addu'oi,yana yi ina k'arba masa kamar wata meh koyon k'aratu koh tilawa.
Can hankalina ya dawo jikina,da hanzari na mik'e ina dubansa,cike da fuskar tausayi nace"Mahmood dina are you okay? Ka samu an wanke maka ciwon? "
Na fadi hakan ina dube-duben kan nasa,ina neman inda naji masa raunin don harna manta wurin,fes! idanuwana suka sauka kan k'atoton plaster din da aka lik'a masa awajen.
Wani d'an marayan kuka ne naji ya sub'uce min,hannu nakai na tab'a wurin,sannu ahankali na shiga shafa wajen,nace"Mijina don Allah ka yafe min hak'ika ko kadan ban k'yauta maka ba,amma ayanxu ina meh farin cikin shaida maka cewar Lallai na haqura xan xauna dakai amatsayin Mijina kuma ina sonka sosae Mahmudanah...... "
Advertisement
Shi kuwa wani irin dadi ne yaji ya tsikareshi tun daga tsakiyar kansa har xuwa babbar yatsar kafarsa,he can't juz believe wai Fadima ta haqura kuma zata xauna dashi har xuwa k'arshen rayuwarsu kafin meh duka ya raba.
Beyi wata-wata ba ya rungumota yana meh jin wani irin sabuwar soyayyarta na kai masa mugun cafka acikin xuciyarsa.
Ahankali yace"Babyna da gaske kin haqura?da gaske kike kin k'arbeni amatsayin mijin aurenki?sannan kuma da gaske kike kin soma jin sona aranki? "
Tsagaitar da kukana nayi,na koma yin 'yar shesshek'a,cike da sanyin murya nace"Yes!!! Mahmood wallahi xan xauna dakai dear nah ina qaunarka har cikin raina.... "
Cike da farin ciki ya cikani yana kallona eyes into eyes,kafin yace"Kenan hakan na nufin u will surely make me to feel being loved once again? "
Gyad'a kai nayi ina meh xubar da 'yan kwalla cike da jindadin ganin tsantsar farin cikin daya shiga.
Yace"And will u be strong,bold & face any family problem dat will be coming soon? "
Cike da fargaba na daure na amsa da"Yeah I promise to be strong & bold for you & I also promise to withstand any obstacles dat will come our way...."
Banyi aune ba kawai naji ya sunkuceni,ya soma yawo dani acikin makeken falon cike da murnar jin kalaman da suka fito daga bakina.
"Dear nah saukeni mana kada kasa mu fama ciwonka.... " na fadi hakan ashagwab'ance,k'ok'arin sauka nake don awuyansa ya daurani,sae ji nayi na dad'a k'ankame kafafuwana.
Yace"Baby ki bari na saukeki da kaina kada ki fad'o ki min asarar wani abin..... "
Dundu na kai masa ta baya,ya b'ank'are bayar,yace"ouhhh!! wallahi dundun ya shiga sosae kuma asannu zan rama idan kika manta..... "
Be direni ako'ina ba sae awani dakin bacci.Yace"Oya matata taso muje mu dauro alwala mu gabatar da sallah don nuna godiyarmu ga Ubangiji daya nuna mana wannan ranar ta kasancewa ma'aurata,ina rok'an Allah daya sanya mana albarqarsa acikin wannan auran,ya kauda duk wata fitintinu,rigingimu da kuma bala'i acikin rayuwar auranmu,ak'arshe kuma Allah ya axurtamu da 'ya'ya na gari,mahaddatan alqur'ani meh girma,masu tsananin tausayin iyayensu da al'ummar musulmi gabaki d'aya....... "
Ahankali nace"Ameen Mijina..... " na fadi hakan sanda nake sharce dan guntun hawayen daya xubo min saman kunci.Tashiwa nayi don cika umarninsa,amma kafin nan sae daya kaini dakina yace na soma yin wanka sannan na dauro alwala nazo na sameshi anashi dakin inda muka baro kenan.Shi da kansa ya zab'o min wata night gown meh k'yau daga cikin wata sif,ya watsa minsu saman gado,riga da wando ce.Sannan shi ya koma dakin nasa don wanka da daura alwala.
Ban dau wani tsawon lokaci ba na cimmasa adakin baccin nasa.Shi ya jamu sallar,Muna sallamewa,ya daga hannuwa sama ya shiga kwararo addu'o'i babu gaggautawa da kuma yiwa Allah k'irari,ban tab'a sanin cewar ilimin arabi ya ratsa Mahmood haka ba sae yau.Yadda yake wani lank'wasa harshe yana baiwa kowacce harafi hakkinta mah wani abin birgewa da sha'awa ne.
Can kuma naga ya d'an juyo tare da dafa kaina,ya shiga kwararo min addu'o'i tare da shi min albarka mara iyaka wanda hakan ya sanya har se dana d'an xubda kwalla tare da jin wani soyayyarsa na fizgata.Yayi mana addu'ar samun zamar lafiya tare da samun zuria d'ayyaba.
Advertisement
Muna idawarwa naji wani sabon bacci yayi min sallama,ashe Mahmood na lure da yadda naketa gyangyad'i tun awajen sallah,yace"Babyna goan sleep naga tun awurin sallah kike ta gyangyad'i kamar wata kaza,oya you ghatta sleep... "
Ya manna min wata peck agoshi wanda na jishi har cikin jinin jikina.Bed dinsa ya nuna min alamun anan xan kwanta,shi kuma naga ya dau pillow ya kwanta ya akasa.ba tare da wata gaddama ba na isa kan gadon na kwanta.
"Goodnite my lovely Wife.... " na tsinkayo maganarsa.
Dan murmusawa nayi nace"Nite too dear nah..... "
_*💞 ya naku first night din ya banbanta dana sauran ma'aurata?*_
**
Suhaima ita kuma bayan an kaita b'angarenta,Reedah ce ta xauna da ita suke ta hira awannan yinin ranar,sae wuraren karfe goma na dare tayi mata sallama ta tafi,Shima din uban gayyar ne ya k'irata awaya yake ce mata"Toh! auta akyalemun amarya hakan ta huta da surutunki,ki tafi bangaranku don ina nan tafe yanxu da abokaina xuwa ga amarya..... "
Murmushi kawai tayi kana tace"kai big brother wai zumudin meh kake haka bayan from now on you have the whole moments to spend together with *'SuhaiLeedar'*?"
"Ni dai na gaya maki Karki sake na iso na iskeki anan.... " ya fadi hakan in a playful manner.
Haka Reedah tabar b'angaren Suhaima wacce dakyar ta barta ta tafi,wai hadda cewa ta kwana.
Dariya sosae Reedah tayi tace"Iyyeh! ashe so kike Yah Haidar ya min dan iskan duka yau acikin gidan nan kenan sabida yadda mah naga yake rawar k'afa akanki,toh kuwa idan aka kuskura aka kawo masa wargi ze iya lallatsa mutum,am so sorry bestie kiyi haquri ki bari ku durje first night dinku don hakan shi ake k'ira da *'Bye gudnite..... "
Tayi gaba tabar Suhaima da binta da kallo.Ansha barkwanci da wasanni daga angwaye,daga k'arshe sukayi musu addu'ar samun zaman lafiya da kuma samun zuri'a d'ayyaba,sannan sukayi musu sallama suka fito.Har wajen motocinsu Leedar ya rakosu yana dad'a musu godiya.
Fresh ne ya jawoshi gefe bayan sauran duk sun shiga cikin motar,ya d'an daki kafadarsa yace"Shege abokina yau an zama babban mutum,dan iska kuma kabi yarinyar mutane asannu sabida yadda naga kake rawar kafa akanta kar ka...... "
Dunkule hannu yayi ze kai masa dundu abaya,da sauri Fresh yayi wajen motarsu yana dariya,Leedar yace"Bakai wai dan iska ba? Dont worry zaka ci ubanka ne.... "
Haka de aka rabu cike da farin ciki da wasanni.Shima juz lyk kamar yadda su Mahmood sukayi,haka suma din sukayi.Wato gabatar da sallah don nuna godiyarsu ga Allah da kuma addu'ar samun zaman lfy da zuria ta gari.Sae de su nasu kwanciyar ya banbanta,don tare suka kwanta,ni kuwa ganin lamarin nasu na nemar sauya zani ya saka nayi saurin barin dakin don kam naga kamar suna matuk'ar buqatar sirri.
_*Nice one SuhaiLeedar💞... Asubahi ta gari....*_
***
*4
_*"innalillahi wa'inna ilaihi raji'un,Allahumma ajirni fi musibati wa akhlifni khairan minha...."*_....... Wannan k'aron da salati na farka da ita bayan wani mummunar mafarkin danayi akan Suhaima da Leedar,wai jinns dinsu Rukky sun halak'asu kamar yadda suka dau alqawari.
Kuka na fashe dashi wanda hakan ya sanya Mahmood farkawa agigice,ambaton sunan Allah ya soma yi kafin ya nufo inda nake,ya kunna dim light,haske yadan bayyana kadan adakin.
"Baby doll wat happened? Mummunar mafarki kikai ko? "
Agigice nace"Eh.... Dama.... "
Da sauri ya katseni yace"No baby doll ba'a bada labarin mafarki,kawai addu'a ya kamata kiyi kinji ko? "
Ahankali nace"okay nagode dear nah.... " addu'o'i na soma xubawa acikin xuciyata babu gaggautawa,ji nake kamar na latso su Leedar din amma kuma bana son Mahmood yasan halin da ake ciki.
(Hahahah! Fadima ta sanya abin aranta ne shiyasa tayi mafarki da hakan! If not *'nanan lafiya qalau,sharar baccinsu mah suke ahalin yanxu,shi Leedar dinma ya manta da batunsu don ya rik'e addu'a sosae).
Daga ni har shi bamu sake komawa bacci ba,Muna nan xaune kamar wasu kurame har aka soma k'iraye-k'irayen sallar asubahi.Ya umarceni dana tashi mu gabatar da sallah.Koda muka idar mun dad'e zaune yana zuba mana addu'o'i,can muka shafa,komawa gado nayi na kwanta don wani bacci-bacci ke idanuwana.babu b'ata lokaci baccin yayi awon gaba dani.
Mahmood kuwa sae daya dan karanci alqur'ani,shidda tana yi ya mik'e ya shiga kitchen don had'a musu abinda zasu ji.Arish ya soya musu da kwai,sannan yayi warming ragowar pizza din jiya da kuma garnished chicken.sae kuma ruwan zafin daya dafa ya zuba aflask wanda zasu sha shayi da ita.
6:58am ya kammala komai don ba wuya,still de magajiyar tana nan kwance tana sharar baccinta,kuma ko kadan baya da niyyar tashinta,hasalima wankansa ya shige.
**
Khairat yar bala'i tun shidda da rabi ta iso family house,Labeeba kuwa sae 7:15,Anty Meema ita kuwa sae data b'ata musu lokaci sosae don sae takwas Saura ta iso gidan,Momi kamar zata kifeta da duka don haushi. Haka suka fito suka dunguma gidan Mahmood tare da taimakon Usee (usman) as the driver. (Hahaha! Inyi muku irinta momi,tace"*
Hanan taso binsu amma se ta tuna cewar yau Dr.Basira zatazo dubata kuma da sassafe take dako sammako................ 📝
A/N
*Ohh! My God!! Mahmood Nakowa kayi ne! Ka cika jarumin jarumai,rana daya,tashin farko Kasan yadda kayi ka cusawa Fadima sonka harta haqura ta xauna dakai,koda yake dama can ta soma sonka amma ita bata san da hakan bane.... Job Weldon to you M.Nakowa....First mission completed & succeeded,now let's watch & see if you will succeed in ur second mission (The family problem).
Ohhh! My God! Nakowa's family are on their way..... Ghen!ghen!ghen!! Fire on the mountain🔥🔥🔥🔥🔥
*sorry guys nasan da yawanku sun aza ko awannan episode din za'ai bala'in,sorry dearies I want to follow each step one by one without skipping!!
*
Advertisement
- In Serial229 Chapters
HUNTED
One late-night run changed Aila’s life forever after getting caught up in a battle between werewolves and hunters. She is suddenly kidnapped by said hunters and finds out secrets about her past and her future as she embarks on a journey to find out who or what she truly is.
8 4068 - In Serial42 Chapters
Kairos: A Greek Myth LitRPG
Available for purchase on Kindle Unlimited and Audible! It has been centuries since mortals unlocked the secrets of the Fate System and overthrew Mount Olympus. The old gods are dead, and their thrones are empty. Kairos, a young pirate with the ability to speak with animals, has an ambition: to ascend as the newest deity of a flooded world. But divine power is not given. It is taken.Now Kairos must sail the endless sea, tame fearsome monsters, and conquer new lands. The challenges are many, but he will face them all. For Kairos is a cunning [Rogue] indeed... Cover by Vitaly S. Alexius.
8 514 - In Serial35 Chapters
Hell's Gate
As an adopted girl from Japan, Celeste remembered vivid details of connecting with the spirit world that existed beyond our own. After years of therapy, she convinced herself that it was simply the product of a young girl's imagination. That is, until her life slowly shatters around her. Her family has kept something so shocking from her that it not only could destroy her life, but the worlds. With allies by her side and enemies at her heels, Celeste must fight her way through the secrets and lies that pave the roads of the world’s future.
8 242 - In Serial18 Chapters
The Calm Death God
In the Year 2084, the most brutal and inhumane crime of all time occurred. The perpetrator? John Sixth, a ten years old boy.He entered the maximum security prison cell at the age of ten. And he absorbed all kinds of information inside his mind and made it as his own by reading books given by his cell guards.Now, after ten years, is his execution day.Mainly Inspired by DN and the Good Reaper
8 210 - In Serial12 Chapters
The Warrior on the Bridge
This is a story about the Warrior who was ordered to guard the kingdom's one and only bridge. The kingdom is surrounded by mountains so that bridge is the only way you get inside the kingdom. The mountains magically prevents flying monsters and dragon riders from flying over it which was a blessing to the kingdom. The kingdom was impregnable but one day... The king went out on a campaign. He took everyone except the Warrior on the Bridge. The king never came back. A lot of people and monsters came to attack the kingdom but the Warrior stood firm for years. Will he still be able to guard the bridge on his own? Or can he accept the help of others to protect his beloved kingdom?
8 135 - In Serial160 Chapters
Ashtray/Javon imagines
"i'm just trying to stack my cash,pay off our mortgage,so what the fuck you want?"✿ - NO SEXUALISING, HE IS A MINOR.
8 201

