《SHIN SO DAYA NE? (Complete)》PART 2:CHAPTER FIVE
Advertisement
*💘
"Fadima I have to take us back,sabida yana da matuk'ar muhimmanci kiji labarin Zeey Maleek d'ita,jin labarin ne ze saka kisan yadda akai naji sha'awar son na aureki,amma kafin na cigaba da baki labarin pls let's eat first don yunwa nakeji sosae...." Ya fadi hakan tare da rik'e cikinsa kamar da gaske,so yake kawai ta d'an tab'a wani abin.
"Ni bana jin yunwa,kaci abinka kawai,kuma ka min sauri........ " na fada atakaice ina meh hura hanci.Da mamaki naga ya bini da kallo,kana yace"Saurin meh kike ne baby doll? Remember from now on,we hav the whole moment to spend together for the rest of our lives,Fadima ina son ki sani cewar aurena dake Insha Allah mutu ka raba ne...... "
Naso tanka masa amma kuma se naga idan na biye mishi zamu ta jan magana ne gwara kawai nayi shiru na bishi ahankali donna samu ya warware min zaren daya sak'a.
"Ki sakko muci idan ba haka ba nima baxan ci ba kuma bazan baki labarin komai ba,kinji nace wallahi... " yanayinsa ya nuna sam babu alamun wasa atattare dashi,hakan ya sa ba tare da na tsaya wani dogon tunani ba na sakko sabida na k'osa naji takun basajar daya k'ulla.Shi da kansa ya firfito mana da abubuwan dake shak'e cikin k'atuwar ledar daya shigo da ita.
"Baby doll wanne zakici aciki? Pizza ko garnished chicken🐓? Or u will like to take all?? "
"Lallai guy din nan ya mugun raina min wayau ba kadan ba,wai ni yakeso ya yaudara da salon soyayyarsa ko meh?hadda wani *'ba damuwa duk kayi ka gama xan bika asannu don mu wanye lafiya."
Hura min idanuwa naji yayi wanda hakan ya maidoni daga duniyar tunanin dana lula xuwa duniyar da muke ciki.
"Matar Mahmood ya naga kinyi shiru? Ko so kike na baki abaki? Iyyeh fada min karki ji kunyata am ur husband.... " ya fadi hakan tare da kashe min one eyes.
Dan guntun tsaki naja,nace"Bannaso ai nima ina da hannun da xan iya ciyar da kaina,garnished chicken🐓 din kawai xan iya ci.... "
Murmushi naga yayi yace"An gama my all,bari na dauko plate" ya mik'e tsaye,naga ya nufi b'angaren dinning,ata gefen dining din naga ya bud'e wata kofa ya shige ciki,atake na gano nan ne kicin din gidan.Ji nayi kamar na arta aguje nabar gidan kafin ya fito,amma se kuma naga rashin dacewar hakan,sam yin hakan ba class dina bane,kuma ai ina son nasan ta yadda akai ya sami aurena,don haka be kamata na gudu ba,xan bari mu wanye ta salun-alum idan yaso hakan,idan kuma ta tashin hankali da kuma k'eta yakeso arabu,then Fadima Sa'ad is ever ready for that.
Murmushin yaudara na sak'ar masa sanda naga ya nufo inda nake da plate ahannunsa.Cike da kissa da kisissina na mik'e na k'arbi plate din hadda wani duk'awa wanda hakan ba k'aramin mamaki ya bashi ba.
"Dear ya naga plate daya kawai ka dauko? " na fadi hakan ahankali tare da lank'wasa murya.
"Ah plate daya xamuci.... " ya fada yana kallonta cike da mamakin wannan sudden sauyawar tata,daga shiga kicin ya dawo har ta canza ta koma Fadimarta daya sani? Ko dai tunani tayi taga rashin dacewar abinda take masa da kuma maganganun da take ta kwakkwab'a masa? Ko ta haqura ta rungumi kaddararta ne?
Axuciyarsa yace"No Fadima am not getting you at all... I guess you are upto something freakish & very mean... "
Ni kuwa axuciyata nace"Dan iska mamakin canzawata yake,besan cewa so nake na lallab'ashi ya gayan komai sannan nasan nayi ba,hadda wani wai ah plate daya xamuci abinci,shege daga yau sae de kaci abinci ah kwano daya da uwarka ba dai da Fadima Sa'ad kuma ba.... "
Advertisement
Sosae na sake jiki mukaci mukayi Kat! damu,mafi yawanci shi da Kansa yaketa feeding dina,ni kuwa sau uku kawai na bashi abaki ina meh cike da takaicin kaina.
Bayan mun k'are cin abincin,naga ya kasa haqura yace"Baby doll wat happened? Wannan sudden change din nan taki am suprised fa?kodai u're upto something ne? "
Murmushi meh ciwo na sakar masa,kana nace"No ba komai wallahi,ni de kawai kaban labari.... "
Saukar da ajiyar xuciya yayi,kana ya soma bani labarin rayuwar soyayyarsu shida tsohuwar matarsa **,mace meh tsananin sonsa da tattalinsa,mace meh gudun b'acin ransa da son kowa nashi,wani abin nasu da idan ya fadi sae muyi dariya,wani kuma na abin atausaya musu ne yanda wai matar babanta ta sanyata agaba,ashe wai tun tana 'yar karamarta mahaifiyarta ta rasu.Ta taso ne ahannun matar babanta wanda sam ko kadan bata qaunarta,har tayi aure wani lokutan mah takan zo har gida idan baya nan ta lakadawa ita Zaynab din dukan tsiya ita da 'ya'yanta mata,yayun Zeey din.Dakyar da sudin goshi ya taka musu birki ya kuma sanya aka masu iyaka da gidansu.Gashi ita Zeey din tana da haqurin gaske,komai aka mata sae kaji tace"wallahi dear nah na yafe musu har cikin xuciyata. "
Hakan ya saka Zaynab ta sake samun gurbi acikin xuciyarsa,sae ji yake kamar duk duniya babu ta biyun Zeeynsa,baya jin ze iya rayuwa da wata 'ya mace face Zaynab dinsa ko bayan ranta.
"Sae gashi rana daya na k'aryawa Zeey dita alkawarin dana daukar mata,yau gani ga wata 'ya macen amatsayin *' *'Fadima ranar dana soma ganinki alokacin da kuka kawo ta'aziyya kano,aranar se dana danyi jinyar xuciyata,don ganinki ya tuno min da Zaynab dita,everything about you was juz lyk hers,infact! hatta kamanninki da nata yanaso yayi iri daya.Ah yinin ranar na lura sosae na kamu da matsananciyar sonki,why? Because gani nake kamar Zeey dita ce ta dawo.
"Titsitseyar Hanan nayi,na sakata dole ta bayyana min alak'ar dake tsakaninki da Mubarak wanda ko kusa banso hakan ba,naso ace babu alak'ar soyayya atsakaninku,kuma wallahi banso kika bishi wani gun ba,Fadima sam be kamata ace amatsayinki ta 'ya mace musulma, kuma kamilalla kiyi trusting namijin da baki taba sanin halayyarsa,ki yadda dashi kai tsaye har ki bishi for only Allah knows inda zai kaiki ba,wannan abin ba k'aramin sosa xuciyata yayi ba,amma se na batsar nace toh wai ni miye nawa da damuwa akanki? Ai ke kika kai kanki,duk da cewar na yadda da kanina sam ba mazinaci bane,amma ban san meyasa na kasa sakewa da fitarku tare ku biyu kadai ba,ashe de sonki nake ban sani ba,koda naje gida kasa xama nayi,naji kamar na sanya k'iransa na rufeshi da fada akan ya maido dake gida,amma se naga zagewar zatayi yawa and he might get to suspect something."
Jan gwauron numfashi yayi kana yace "Na takaice miki labari,dawowa nayi na xauna jiran dawowarku awaje,ita Hanan duk ta tsure duk aganinta tashin hankali xan haifar sanin da tayi na cewar mahaifiyarmu bata qaunar wani acikinmu yayi tunanin qara matar aure,aganin ita Hanan din xan taya Mummy hukunta Mubarak ne,na nuna mata cewar karta damu ba wani tashin hankali xan haifar ba kawai Fadimar ta min kama da wata wacce na sani ne.Kamawa daga wulaqancin da mummy tayi wa 'yan'uwanki,da korosu waje da tayi duk akan idanuwana ne,koda naje ina bata haquri zageni tayi tass! ta ajje agefe wai har ni ina da bakin magana? Ai gwara Mubarak din tunda shi yayi tunanin qaro aure amma ni fa? dayar mah na gagara ajjewa ina nan kamar wanda aljana ta aure,sae kace kaina farau aka soma yiwa mutuwa. Maganarta daya fi sosa min rai har ya saka na dan zubda kwalla shine wai,da alamu haka xan k'arashe rayuwata babu magaji,wanda ze dunga daga hannu sama yana min addu'ar samun rahamar ubangiji,sae de nata daukar 'ya'yan abokaina ina sha'awarsu,hakan data fada shi ya k'ara min kaimi da kuma k'warin gwiwar gwada sa'ata awurinki,ban damu da cewar ke din budurwar kanina bace,burina kawai nasan ta yadda xan bullo miki har na samu shiga awajenki,because nima ina buqatar asake sona,I want to share dat love again with someone,Fadima I really want to see my own children,kuma ke kadai ce naga kamar Kinfi dacewa da rayuwata shiyasa nayi tunanin xuwa gareki,nabi bayanku don nasan gidanku,koda naga motarku ta lalace,sae na samu wuri nayi parking adan nesa daku don Kar nayi saurin tunkaranku ku d'ago wani abin.Sae dana dan ja lokaci kuma na tabbatarwa Kaina lallai bazaku dago ba sannan na tunkareku."
Advertisement
Anan Mahmood ya baiwa Fadima labarin komai na yadda akai yata fama da xuciyarsa da kuma kokarin son ya yakice soyayyarta acikin xuciyarsa,amma hakan ya faskara,akan dole yabi son xuciyarsa,ya kudura aransa cewar dolene ya baiwa xuciyar abinta takeso.
Yace"A.B.U Zaria ta dade tana aiko min da request akan suna matuk'ar buqatar nazo na dunga aiki dasu,don suna da labarina yadda nake da basira da kuma fasahar sarrafa na'ura meh k'wak'walwa,I hav turned down their requests on several occasion,ganinki ya saka ni da kaina na aika musu da sak'on amincewata da offer dinsu,wanda tsananin murnar hakan ya saka suka bani k'yautar wata madaidaiciyar gida don nuna godiyarsu agareni.Ni kuwa gani nayi rayuwata xata dawo sabuwa dal kamar an ciro daga kwali,xuciyata fes! raina yayi haske ganin nayi close dake,wani abin dadin dadawar kuma,wai kema A.B.U kike schooling, hakan yasa naci alwashin bazan tab'a wahala wajen shigar da kaina gareki ba,xanyi kokari naga na koya miki yadda zaki soni,sannan daga baya na aureki kota halin k'ak'a. "
Ya bata labarin yadda sukai tayi da Mubeen,yadda Mubeen din keta nemarta awaya baya samunta da kuma yadda yayi masa karyar wai sabuwar wayace take jira,da kuma hana masa xuwa Zaria da yayi don dubata,da kuma wucewarsa India da dramar da kullum suke sha awaya.
Yace"Wallahi ko jiya mah se daya k'ira amma naki dagawa.... "
Afusace na mik'e nace"Agaskia Mahmood kaci amanar Mubarak ba kadan ba,Allah sarki bawan Allah inata tunanin kila dama can yaudarata yake baya qaunata shiyasa be damu yasan halin da nake ciki ba,ashe abinda ban sani ba,kai kana can kana shuka masa bishiyar k'arya har tayi nasarar tasiri da kuma girma acikin xuciyarsa,why? Because ya yadda dakai,yasan bazaka tab'a masa k'arya ba,Mahmood meyasa zaka ci amanar Mubarak? Why? Meh yayi maka arayuwa da har zakayi tunanin ramuwar gayya irin wannan? Kamar yadda kake ikrarin kana sona,toh wallahi Mubarak ya fika sona sau dubun dubanni,ka kuwa san irin tashin hankalin da kake kokarin haifarwa acikin zuri'arku? Ka tab'a tunanin cewar anya xuciyarka ta maka adalci wajen sona kuwa? Tukunna mah de gaya min wanene *'agareka,sannan kuma ina family dinka suke da akayi wannan auran?"
Jikin Mahmood ne yayi sanyi qalau kamar kankara,ahankali ya bud'i baki ya cigaba da mata bayani"Baba Mu'azzam shima family dina ne ba hayarsa nayi ba kamar yadda kike tunani,k'anin mahaifina ne,shak'ikinsa kuwa,ma'ana ciki daya suka fito da mahaifina,matarsa daya itace Haj.Fa'iza wacce akafi sani da 'Mami',ya'yansu biyar kuma duk mata,Zaliha itace ta farko wacce take kusan sa'ar Maryam (Meema) qanwata,nasan kin ganeta don da aka kawoki mah tana gidan,tana auran wani dan sanda ne anan kanon,sae Zaineema meh bi mata,ita kuwa sa'ar Usman kaninmu ne,ita kuwa tana aurene ah katsina,ita bata zo bikin ba amma nasan yan'uwanta sun gaya mata,sae meh sunan Kaka rigima wacce ake k'ira da 'Afreen',ita kuwa sa'arki ce,sae Hafeezah sa'ar Suhaima,sannan auta Rafi'ah.Sanda kika fada min cewar ai mahaifinki shine chief justice ta yankin federal high court Zaria,sosae nayi murna don na sanshi da dadewa,Baba Mu'azzam ya tab'a zuwa dani wurinsa sau daya ah office dinsa,mahaifinki abokin baba ne sosae don ta sanadiyyarsa ya samu aikin alk'alanci,lokaci daya sukaje nemar aikin,se akace mutum daya kawai za'a dauka,anso daukar Baba ne amma se kuma yaga kamar abokinsa Sa'ad ya fishi buqatar aikin,se ya haqura ya bar masa,shi kuma ya tafi ya soma kasuwancinsa kadan da kadan har Allah ya sanya albarqa,ya tallafa masa ya habbak'a kasuwancin nasa ta man fetur.Sosae justice ke ganin mutunci da kuma darajar Baba don aganinsa ya taimaki rayuwarsa ba kadan ba,sati daya da soma aikina ah A.B.U naje office din mahaifinki,sosae yayi murnar ganina don ya shaidani,bayan yan gaishe-gaishe,na gabatar masa da kaina amatsayin meh sonki da aure,dan Jim yayi yana tunani."
(Alokacin tunani yake akan Haidar kada ya watsa musu k'asa ah ido don bazai iya hana dan Baba Mu'azzam auran 'yarsa ba,kawai zeyi tunani akan hakan)
"Ni kuwa gani nayi kamar bazan samu abinda nakeso ba,atake anan naji gwiwowina sunyi kasa,can ya karbi lambar wayata tare da ce min zeyi tunani akai. "
(Bayan kwana uku da ganawarsa da Mahmood,shine al'amarin su Fadima ya bullo,ya danyi murna da hakan,kenan ai Haidar bazai ce an watsa mishi kasa ah ido ba,yanxu yana da damar baiwa dan Alh. Mu'azzam auren Fadimar don kwarai ya yaba da hankalin Mahmood).
"Bayan kwana biyu sae ga k'iran Baba Mu'azzam wai yana son ganina,koda naje sosae ya nuna min murnarsa na samo 'yar gidan mutunci da tarbiyya amatsayin wacce nakeson na aura,wai justice na musamman ya kirashi ya labarta masa komai tare da bada go ahead din aturo,toh anan ne na rokeshi kan don Allah kada asanar da mahaifiyata don bata qaunar yarinyar,sannan kuma kada ayi wata gayyata don kada maganar ta bazu har ya isa kunnanta,sosae yayi mamaki da zancena har yace shi baze goya min baya nayin auran nan ba har se naje na nemo izinin mahaifiyata da kaina,rok'ansa nake tayi harda kuka akan ya taimaka ya shige min gaba na samu na aureki Insha Allah bayan auran sae asanar da mahaifiyar tawa,dakyar da sudin goshi ya amince ya shige min gaba don shi kansa yana bala'in son wannan hadin har ransa,toh kinji-kinji yadda akai na sami auranki,sannan ko daya acikin yan'uwana babu wanda yasan da wannan auran hatta shi Mubarak din........ "
Kallonsa nake cike da tsanarsa da kuma k'yamar hanyar daya bi ya aureni ba tare da samun albarqan mahaifiya akan wannan auran ba,hawaye sae bulbulowa suke saman kuncina babu gaggautawa,kuma ko kadan ban damu nasa hannu na sharce su ba...............📝
A/N
Ga alqawarinku nan na cika,Insha Allah zaku dunga ganin update kullum as frm now on!!!
*
Advertisement
- In Serial14 Chapters
Blue Hills
Nothing had ever felt quite right for Alexander Adamson. He'd worked his way up to a job he could tolerate, a few casual friends, and even a nice little apartment that he could call his own, though it really wasn't. The problem was that none of it was satisfying. It was as though he were going through the motions of a life, rather than having one of his own. Of course, it didn't exactly feel right when he woke up in a strange bed in the middle of nowhere. Nor when he was told that he was now the proud owner and operator of a local farm. A farm that had belonged to a late uncle he'd never known. But with the first train out of town a full 'season' away, he had plenty of time to get used to the idea. Plenty of time, perhaps, to even get to like the strange little town of Blue Hills. I have a discord now. Marvel at my ability to somehow still be antisocial on the other side of a screen! Back from hiatus along with my other fiction. Chapters are on a Thurs/Sun schedule until book 3 of that fiction is completed, at which point I'll be updating this daily. At which point uh.... I dunno what I'm going to do.
8 229 - In Serial287 Chapters
Owlnother World
In a hospital bed somewhere on Earth, I breathed my last breath. Or at least I thought I did. Then suddenly, I was flying through a void of nothing. As I landed in a new world, my life as an owl had started. Follow this girl on her journey in a new world, with a new life as she explores cultures, peoples, magic and herself. What mysteries does the world hold? Where does the magic come from? And what does she want to do with her new lease on life? This is my first story and I want to use it to explore writing people, character development, environments, relationships and all the other things a good story should have. I would be happy if you give it a chance and for me, feedback as well as criticism.
8 504 - In Serial19 Chapters
Headpat Bot!!!
Erika Saito is a first year highschool student who just moved to a new city and due to her shyness is having trouble making friends. On her way to school she becomes unlikely allies with a robot named Byte who is as stoic as they come, but the only way he can keep his fuel cells charged, is through headpats!
8 190 - In Serial6 Chapters
Realm of Fantasy Online
The launch of the first ever VR MMO is underway. Grey gets ready to enter the game and start his life over again. By unforseen trajedy he is forced to become a nercromancer and all the friends he has wanted his whole life shun him. If only he could log out. City building, Crazy magic, death and despair, necromancer, this book will have it all. I hope you love it. Authors note: Hey everyone, this is my first book and I hope you like it. I will be going back and redoing the first two chapters with blue boxes for the system messages. I was going to rewrite it in 3rd person but my two favorite LitRPG's are "Ascend Online" and "Life Reset" both are written in first person so I am sticking with it. -Hammy Schedule: Currently I am able to write a chapter a day but I need time to edit and live my life so I am aiming for 3-4 days per upload. This is a hobby afterall. [participant in the Royal Road Writathon challenge]
8 208 - In Serial83 Chapters
Last Man
Nikodemus is the Last Man on a planet that resembles earth. He spends his days being hauled from female tribe-to-female tribe, as they fight over him in an effort to preserve the human race. All female tribes worth their salt have at least one mutant at beck-and-call, who are the smartest creatures on the planet and are used to program robots who assist in capturing the Last Man. The tribes aren't the only thing to fear in the desert; there are also viscous scorpion creatures lurking out on the sands. Perhaps the only thing more deadly then then the demons living in the Wasteland, are the demons living inside Nikodemus. Can he fight them off and see the worth in humanity after experiencing the worst of it for all forty-five years of his life?
8 111 - In Serial33 Chapters
The Betrayed Pilot (Titanfall x RWBY)
Five years of servitude to the IMC, five long years until I decided to leave them for a better life. But instead of what you would of expect of other pilots, where they would of joined the Frontier Militia, I had the chance to join the Apex Predator, so i took the chance and joined them. And my first assignment is under Kuben Blisk, to protect the IMC's new fold weapon. Let's hope everything goes to plan.I don't own anything, but my own characters, Titanfall is owned by EA, and Rooster Teeth owns RWBY, and the cover is by Sanderson on Pixiv, I hope you enjoy this story, and if you have any problems, then just tell me and I'll address them immediately.(#1 pilot 12/16/2020))(#3 titanfall2 (12/16/2020))(#1 rubyrose (1/4/2021))(#2 velvet (4/6/2021))
8 192

