《SHIN SO DAYA NE? (Complete)》CHAPTER SIXTEN
Advertisement
💘SHIN SO DAYA NE?💝
TARE DA ALKALAMIN
📝
HAFSAT AL-MUSTAPHA
_Watpadd:Hafnancy_
🌼BABI NA GOMA SHA SHIDDA🌼
Page 75-80
Wasa-wasa zazzabi ya rufe Hanan.Jikinta duk ya d'au zafi, da alamun hannun nan ne ya saukar mata da zazzabin.Sai da Mubeen yai mata allurai har uku tare da sanya mata drip bayan ta samu ta danci abinci.Sai aikin bacci take ta Zubawa bana wasa bah.Duk hankalin Mubeen ba'a kwance yake bah sabida duk Hanan ta bi ta rud'ashi, gashi yana son ya k'ira Fad'ima amma bai samu damar hakan bah, and again fushin da Mummy tayi akansa bah karamin damunsa yake bah.
Kanwarsa Labeebah ce tayi masa waya take fad'a masa cewar gata akofar gidansu, don haka yazo ya bud'e mata.Cikin sanda ya fice daga d'akin gudun kada ya tashi Hanan.
Yana gama bud'e gate d'in, Labeebah tace"Wai ni Yaya sai yaushe zaku soma barin kofar gidanku abud'e ne? Wai ace kullum gida baka taba samunsa abud'e sai dai koh wani lokaci akulle... sai kace wani gidan kurkuku? "
"Yo! don sarkin garinku so kike ko wani gardi ya shigo gidan unexpected ya gane mini mata anyhow right? "
Murmushi tayi tare da rik'e hab'a, tace"Hmm! Ina ruwansu brother kakannin kishi kenan..."
"Tukunna dai..... Meya fito dake da goshin magrib d'in nan wanda kamata yayi ace warhaka kina d'akin mijinki? " yayi mata wannan tambayar, wannan karon babu alamun wasa tattare dashi. (watanta shidda kenan da aure).
Tace"Daga Na'ibawa muke.... Shine Mummy tace mu taimaka mu kawo Jasmine tunda duk kusan unguwa d'aya muke daku...... " Ta fad'i hakan tare da nuna Mus'ab mijinta wanda rike yake da hannun Jasmine suna kokarin karasowa inda suke.
Musabaha sukai da Mus'ab d'in, suka gaisa amutunce with due respect.
Jasmine ce ta saki hannun Mus'ab, da gudunta ta rugo ta rungume Mubeen, ayayin da shi kuma ya dagata sama.
Tace"Daddy I really missed you.... amma ina fushi dakai hadda mummy tunda kukai tahowarku jiya kuka banni acan gidansu granny inata kuka.... "
"Sorry babyna bazan k'ara bah kinji... " ya fad'i hakan tare da marairaicewa kamar zai saki kuka.
Juyowa yayi ga su Labeebah wanda suka shagala ga kallon soyayya irinta d'a da mahaifi, yace"Mus'ab bismillah mana ku shigo... "
Duk Jasmine tabi ta dameshi da surutu.
"Daddy kaga Uncle ya siyamin tsirei da youghourt akan hanyarmu ta zuwa nan...ga bag d'in kayanmu ni da mummy can ahannun Anty wanda ta manta dashi acan jiya.... "
"Laah! Lallai wannan uncle d'in yana son 'yar babyn nan tasa... Hope dai kince masa thank you? "
Da sauri tace"sosai mah... Lodi lodi mah Kuwa... "
Aka fashe da dariyar maganarta wanda adaidai lokacin suka shigo cikin falon.Jasmine sai tambayarsa inda Mummynta take.
Advertisement
Yace"Baby mummynki bata da lafiya... she's in the bedroom sleeping, so don't wake her up okay? "
Ahankali ta daga kanta alamar taji maganarsa.
Labeebah tace"Ayyah! brother ya jikin Anty Hanan d'in? Mummy ta fad'a mana cewar bata jin dadi and again taji rauni ahannunta..... "
Da sauri yace"Eh!! tsautsayice ta afka mata... ta yanke ne da wani glass amma da sauki yanzu.... "
Mus'ab yayi masa jaje tare da tambayarsa mai jikin.
Labeebah tace"Bari na d'an dubota.Ta mike zatayi d'akin Hanan d'in, da sauri yace"No, tana dakina.... "
Jin hakan ya sanyata Juyawa ta nufi direction d'in d'akin nasa.
Tana zuwa kuwa taga Hanan d'in har lokacin baccinta take abinta.
Ahankali Labeebah tace"idan banda abin namiji... Mai mace kamar Hanan ta nema ta rasa, yarinya gata dai k'yakkyawa, mai hakuri da kuma godiyar Allah... She has everything da duk wanda yake jin shi d'in classic man ne zai so atare da Ita... Toh mai zaisa yaya yayi tunanin karo wani aure? "
Girgiza kanta tayi, ta juya ta fice daga dakin zuwa falo.
Tana isa falon tace"Brother please I want to have a talk with u... "
Gabansa ne ya fad'i, ba tare da tunanin komai bah ya mike yana cewa "ok".
Wani karamin falo suka je.Zama sukai akan kujeru daban-daban.
Yace"ina sauraronki.... Kuma kiyi sauri kada Mus'ab ya gaji da jiranki... "
Tace"Yaya Mubarak why? Mai ya shiga cikin kwakwalwarka ne yau da har ka iya tsayawa ka fuskanci mummy ka fad'a mata maganganu son ranka abinda koh amafarki idan akace kayi shi, am very sure bazaka taba iyawa bah? Matar data nuna mana so na tsakani da Allah tamkar ita ta haifemu..... Wai itace ayau kake mata tuni da cewar bah ita ta haifeka bah?...
"The most suprising part shine da aka fada min cewar ka had'a k'ashi da wanka... Wai duk akan wannan shegiyar kake neman b'atawa da family dinka.......? "
Cikin zafin nama ya mik'e ya isa gareta, babu wani b'ata lokaci ya dauketa da wani zazzafar Mari.
Nan da nan ta fashe da kuka don azaba, tace"Yaya ni zaka mara don na fada maka gaskiya? "
Sake dauketa da mari yayi, yana huci yace"An mareki din... Har ke kin isa ki taso kizo har cikin gidana kina min nasiha...har nawa kike Labeebah da har zaki sanyani agaba kina min fada? Iyyeh?.... Okay I understand.... Mantuwa kikai koh waye babba tsakanin ni dake.... toh Lemme remind u...Ni Mubarak nine 'wa' ayayin da kuma ke Labeebah kece 'kanwa'....... "
Afusace ta mike tana fad'in"Yaya Mubarak godiya nake kwarai da gaske.... Amma ina son ka sani cewar ita wacce ka zabeta akanmu, insha Allahu asannu zata gwada maka halinmu na mata..... "
"Fitar min agida before I loose my temper na tattataki anan wurin.... " Ya fadi hakan da karfi.
Advertisement
Ta fice daga falon tana fadin"Shegiya, mayya... Waya sani mah koh wankewa tayi ta baka kasha.... "
Biyota yayi har falon ya sake dauketa da wani gigitacciyar mari agaban Mus'ab. Sakin wani kara tayi don hakika wannan Marin yafi shigarta Akan sauran.
Yace"Ina ruwanki idan mah wankewar tayi ta bani nasha?... Kinga Labeebah kiyi sauri ki bace mini daga gani immediately idan bah haka bah wallahi jikinki zai fada miki gaskiya.... "
Mus'ab ne ya taso zuwa inda suke, don tun suna dayar falon yake tajin hayaniyarsu da kuma karar Marin da matarsa take tasha, amma kunya ya hanashi zuwa inda suke.
Da alamun wannan karon Mubeen yakai shi bango, yace"Haba Yaya ina ganin girmanka, don haka kada ka sake girman nan ya zube ah idanuwana..... ai wannan yawa ne ka daki 'ya mace kuma matar wani akan idonsa mah, babu koh kunya.... "
Azuciye Mubeen ya juyo yana kallonsa, yace"Hey! Man shut the hell up!.... kai kuma waye... Kare da gudun layya.... Who are u to interfere into a family matter?.... Diz is between me and my sister don haka ka cire bakinka aciki.......... "
"Idan kai ce, toh ni kuma E..... Don haka nasan darajar mace, so karka sake ka kuma taba min mata...... " Mus'ab ne ya fadi hakan cikin tsananin b'acin rai.
Murmushi Mubeen yayi tare da fad'in"Kasan mey? Ku tafi kawai... Amma kasan meyasa zan kyaleka?... Its because u are my inlaw kuma bazan so ace na had'a kashi da siriki na bah... ai kaga da kunya koh? So u guys should get the hell out of my house with immediate effect right away!!!! "
Mus'ab yace"Koh baka fada bah... Dama Muna da niyyar wucewa"
Juyawa sukai suka fice, Labeebah sai kuka take ayayin da Mijin ke aikin lallashinta.
Koke-koke kunnuwansa suka jiyo masa daga bayansa, juyawarsa keda wuya, idanuwansa suka kai ga Hanan wacce take rungume da Jasmine, sai aikin kuka suke.Hannun Hanan wanda aka sanya mata drip dashi sai d'igar jini yake, sabida cire drip d'in tayi ta fito jin hayaniyarsu.
Da gudu Jasmine ta ruga ta rungume Daddyn nata tana kuka"Daddy mai yasa ka mari Anty Labee kuma kayi wa Uncle Mus'ab fada.... Gashi yana da kirki sosai ya siyo min tsirei da youghourt....mey suka maka? gashi Anty Labee sai kuka take"
"Yanzu dai kaji dadi tunda 'yarka taga abin kunyar daka aikata akan idanuwanta.... Don mah bata ga na dazun kenan bah wanda yafi wannan tashin hankali.... Haba mijina akan 'ya mace kake neman b'atawa da family dinka? Ni naga mah wannan yarinyar ba wani damuwa tayi akanka bah sai idan mah kai ka nemeta.... Wannan yarinyar Sam bah alheri bace ga rayuwarka Abu Jasmine.... Pls ka gaggauta rabuwa da ita tunda yan'uwanka basa so......... "
"Hauwa'u!!!!!! " kiran sunanta yayi da karfi wanda tunda yake bai taba ambaton ainihin sunanta bah sai ayau.
Gabanta ne ya hau bugawa da sauri da sauri,ignoring d'in Jasmine yayi, ya nufi inda Hanan din take zaune.
Tsugunnawa yayi daidai saitinta, yace"Daga yau sai yau... Karki sake interfering into my relationship with 'Nagode kwarai da gaske da dukkan taimakon da kika min... Amma daga yau, karki kara sanya baki acikin maganarta tunda naga kin soma gajiyawa da taimakon nawa, tunda har zaki iya cewa na rabu da ita...... Hauwa'u Ina sonki amma ki sani bazan iya hakura da Zahra bah...... "
Mikewa yayi ya nufi daki, yana jin sanda ta rushe da wani sabuwar kuka mai ban tausayi wanda sai daya ji kukan na dukar zuciyarsa.
Dawowa falon yayi da auduga ahannunsa, ya goge mata inda jinin ke fita.Ya rungumo 'yarsa wacce har yanzu kuka take. Lallashinta ya soma yi tare da mata wasu 'yan dabaru da wasannin.. Kun san yara ai,nan da nan ta ware, ta dauko tsirenta da youghourt ta hau ci.
Komawa yayi inda Hanan take,zama yayi agefenta tare da ruko hannayenta, yace"Hauwanah!! Pls am so sorry... Forgive me... Wallahi na rasa koh wani irin soyayyace nake wa Fadima wanda hakan yake sanyani fada da family d'ina... Buh I promised u, as from today am a changed person... No more fighting da yan'uwana akanta.... "
Hanan bata san lokacin da wani murmushi ya subuce mata bah,rungumeshi tayi tana murna.
Yace"Buh hakan ba wai yana nufin na hakura da ita bane........................."
Kallonsa take cike da mamaki........
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻
Har zuwa lokacin nan Mubeen bai nemeni bah, haka zalika nima d'in ban nemeshi bah(hahaha fadima akwai jijji da kai).
Tunanin Suhaima ne ya fado min arai.Atlast, ayau ta gane cewar da gaske son Leedar take wanda ada take musa min.Hmmmm! Dat means game d'ina da Leedar will soon be over wanda bah hakan naso bah... Becuz game d'in ya soma min dadi. Lallai Suhaima da sauranki, becuz I will make sure dat diz game will insha Allah be very tough and hard for you baby................
Wanka nayi na tafi school don yau Monday. Ash na kira don zuwa makarantar nan da zanyi ayau,it is mostly because of Ash and Leedar, don bamu cika yin much lectures ran Monday bah.Ayau nake son na bayyanawa Ash komai dake tsakanina da Leedar........................... 📝
HAFNAN'S POV
Tofa jama'a akwai bidiri kenan.
Shin wani game kuma Fadima da Leedar suke playing?
Wannan kuma wani irin mahaukacin so ne Mubeen kewa Fadima da har ya sanya yake fada da yan'uwansa akanta?.... Ku dai ku biyo Hafnan.
Sorry pls, I know dat diz episode is too scanty buh u guys juz have to bear with me... Wutarmu ta lalace kuma da kyar nake samun chargy yanzu!!!
SAHIBARKU CE
©QUEEN HAFNAN©
Advertisement
- In Serial56 Chapters
Magnum Opus
Before Kyle Greenar was the great Magus Jade Eye, he was just a normal villager from the province of Rock grove. Spending his formative years working on his family's farm, where High Magus Theta Jade happened to be passing by. She saw his talent for magic and decided to take him as a disciple, taking him back to her guild Jade palace. Where he dove into the study of mysticism and the craft of magic head first. Spending hundreds of years to reach the heights of a Great Magus. But on the precipice to becoming a High Magus he was betrayed by his fellow disciple. Follow Kyle Greenar as he takes his new lease on life and follows a different path of magic.
8 194 - In Serial12 Chapters
DISSOULVER
It was supposed to be a chill holiday with friends and family. Another world, no problem. It was supposed to be fair and safe. No powers, no problem. It was supposed to be... I'll kill them all, no problem. This story follows Jay, who - due to higher powers - is summoned to another world. He might not be loving it, but he wasn't supposed to be betrayed, left for dead, tortured, and sentenced to death. There's a gray area between love and hate, but Jay's world is red. --- *The story will occasionally switch perspectives throughout* Chapters will be released weekly, maybe two if I have a chance to write a bit more. Check out my other work - The Tale of Aza, the Villanous Hero Bodyguard.
8 86 - In Serial19 Chapters
Veiled
Sixteen-year-old Desirae Cradle knows how to survive in the human world, but knowing and doing are two different things. Until her mother disappeared under questionable circumstances, Desirae lived as part of a magical community kept secret from humans for more than 4,000 years. But not all of Desirae's people live on Earth. Some live in the Otherworld, exiled there after an ancient war. They are known as the Faye and still seek a way back to Earth. With feelings of abandonment, and no other family among her kind, Desirae makes her way in the human world using the only skill she has-knowing how to cross between Earth and Otherworld. But when a crossing goes bad, Desirae has to do something she swore she never would - go back home. Determined to not only fix her mistake but to mend old friendships, Desirae returns to the community she abandoned. But the Faye are after more than she thought. With lingering questions about what really happened to her mother and the discovery that her friends have changed even more than she has, Desirae finds that stopping the Faye and regaining her friend's trust might not be as easy as she hoped. This is a completed work, approx 75,000 words. I’m just editing chapter by chapter and posting as I finish them.
8 177 - In Serial16 Chapters
Dragon Spirit
In a time of War and Strife, a dragon is born into the World. Kind, Fearless, and completely inexperienced, he battles his way up the evolutionary ladder. Always growing stronger, he sets out to explore his wide world, keeping his friends close, and decimating any who dare to be his enemies. Read on as he meets many creatures, talks back to doting Gods, and slays countless other beasts on his way to reach his destiny! Written by a brand new author, this is a mainly light-hearted adventure story. It’s really not following one distinct genre, instead incorporating fantasy, game worlds, reincarnation, Xia-Xia, and potentially some romance ( ; - D) into a story. Release schedule of about 2-3 chapters a week. Comments and questions are always welcome!
8 192 - In Serial102 Chapters
Reborn in The Marvel World
The story centers around a boy who has been reincarnated and as a result, can't remember who he is. The last thing he remembers before dying is fighting with his friend about which superhero franchise is better. The next thing he knows, he has been reborn as Zen Shade, a half- black, half- Japanese kid. Let’s just say as soon as he gets shot out of the womb, shit hits the fan. His new mom is not ordinary. She takes out ninjas with a magic sword right after giving birth. Zen thinks she is a badass and does not want to get on her bad side. After being born, he moves to New York and sees the Avengers’ Tower. He later realized he has been reincarnated in the Marvel world. The first fourteen years of his life were pretty chill. He learns a whole lot of shit from his mom from sword fighting to Qui control to martial arts even medicine and poisoning and he even gets a special sword that can cut through anything. One Day, he is at the bank that a super villain tries to rob. He lets it go; none of his business; he is not a hero. But, they piss him off. So, using his skills and his sword, Kurohime he beats the super villains. This gets the attention of the Principal of Avengers Academy, Old Man Tony Stark who recruits Zen to the academy. There, he meets the kids of super heroes such as Spiderman, the Hulk, and even Thor. He makes friends and enemies. Being a super hero is easy; surviving high school with a ton of super-powered, emotionally unstable teenagers, now that is the hard part.
8 281 - In Serial65 Chapters
Control [Carlisle Cullen]
•They send me away to find them a fortune•[Carlisle Cullen][Twilight-Breaking Dawn Part 2][cover by: @kingsmaria][Started April 2018][Ended March 2019]
8 85

