《SHIN SO DAYA NE? (Complete)》CHAPTER FOURTEEN
Advertisement
💘SHIN SO DAYA NE?💝
TARE DA ALKALAMIN
📝
HAFSAT AL-MUSTAPHA
_Watpadd:Hafnancy_
🌼BABI NA GOMA SHA HUDU🌼
Page 65-70
Na dawo daga rakiyarsu Ash na tarar Suhaima da Lubna na gyara wajen da muka yi breakfast.
Ko sake kallon ita Suhaimar banyi bah,nace wa Lubna"Lubna ina Umma?"
Tace"Ta tafi bangaren Abba... "
Jin hakan ya sanya na nufi d'akina ba tare da na sake cewa komai bah.Ina shiga daki, wanka na soma yi don naji dan dad'in jikina.Doguwar riga mara nauyi na sanya sannan na dauko wayata na kunna.
Wayar tana gama booting, sai text messages suka hau shigowa kamar dama can jira suke abude wayar.
Text d'in Ash na soma budewa wanda nake tsammanin tun jiya ah Kano tayi min(idan zaku tuna sanda zata dauki Mubeen hoto tayi ignoring wasu messages.... Remembered?)
The message goes lyk dix, "Fadima idan kina yiwa Allah ki taho ki kwashe shanyar da kika yi.... Kayan sun gaji da bushewa...kina can kina soyewarki da Man d'inki ayayin da mu kuma kika barmu ana cin mutuncinmu anan.... "
Murmushin takaici nayi sanda na tuna da Mummyn Mubeen wanda itace Ash ke nufin taci mutuncinsu.Har yau mamaki nake da suka ce min matan nan tayi musu rashin mutunci akaina, sabida sam koh kusa ba tayi kama da wacce zata iya yin hakan bah.Ko da yake such is life... Diz life is full of wonders... Dan'adam tattare yake da abubuwan mamaki kala-kala.
Sauran text messages d'in kuma wanda ake aiko wa mutum ne idan kayi missing voice call.I missed about 20 voice calls daga Ummana wanda hakan na nufin tayi ta trying numbata kenan koh Allah zai bata sa'a ya shiga, she never gave up.... Uwa -Uwa kenan... Believe me if I say, No one like mother.
Sauran calls d'in dana yi missing kuma, daga Leedar ne da Ash, sai kuma Mubeen.
Mubeen kenan sai ayanzu ya fad'o min arai. Nasan yana ta trying line d'ina bai sameni bah, kuma maybe yana cikin wani hali ayanzu I guessed, idan har da gaske yana sona kenan as he said, sabida ni yanzu na daina yadda da love stories na d'a Namiji..'' ya mugun koya min hankali.
Ji nayi kamar na kirashi, sai kuma na fasa because its not my class ni na fara nemansa,shi din mah ya kamata ya k'ira yaji ya muka kawo gida.Don haka zan k'yaleshi duk sanda yayi trying line d'in yaji ta shiga toh Alhamdulillah, amma idan bai k'ira bah toh Wallahi ni d'in mah bazan sake kiransa bah.
' ne ya fad'o min arai.Murmushi nayi ina tuna sanyin halinsa.Namiji ne kamilalle,maganarsa ahankali cikin sanyin voice.Abinda yafi bani dariya agame dashi bai wuce yadda idan na masa tambaya.. Instead ya maido min da amsar tambayata, No sai dai shima ya jefo min tasa tambayar.
Abin dariya ya bani wanda har nake ta k'yak'yatawa, kofar d'akina naji an bude aka shigo.
It's Umma, ganinta bai hana ni daina dariyata bah,dariya fah hadda hawaye.
Ina kallon Umma wacce sai kallona take cike da sha'awa tace"Masha Allah! 'Yar Kareematu burina bai wuce na ganku cikin farin ciki bah akoda yaushe.... Na san koh baki fito fili kin fad'a bah.. tabbas daga ganin wannan hawayen murnar, its an indication dat surukin nawan ya mugun kwanta miki arai. "
Jin kalaman da suka fito daga bakinta ya sanyani tsai da dariyata at once.
Ta cigaba"Dama zuwa nayi muyi 'yar hira ni dake... Wanted to know ya kika gan Mubarak d'in? Shin ya kwanta miki arai or not? "... But now I hav already gotten my answers, kuma ni kaina nayi matuk'ar farin ciki... Kareematu always wants the best for her children... Allah ya sanya alheri"
Advertisement
Cikin rashin kuzari na amsa da"Ameen Ummu Fad'ima u the best.. "
Tace"Yanzu Mal. Iroro ya dawo, ya dauko motar...Wai dama wata injin ce ta sami matsala but an gyarata... Shine kuka bar min kuloli cikin motar kuka yi ta kanku right? "
Dariya na sanya don har ga Allah ni nama manta da batun wasu kuloli,ashagwabance nace"Haba ummata yanzu kulolinki sun fi 'ya'yanki kenan? "
Murmushi tayi tace"Juz kidding... Haba ai 'ya'yan Kareema always cumx first.... Bata had'a 'ya'yanta da komai... "
"Tankx best mum... " Na fad'i hakan cike da k'aunar mahaifiyata.
Tace"Abbanku wai kizo ku gaisa.... "
Atsorace nace"Umma am scared to face him..... "
Tace"Come on daugh... Wallahi he knows nothing abouh ur late journey back... Trust ur mother, na dai fad'a masa cewar around 1pm motarku ta lalace, shine kuka kirani sai na aika Mal. Abu mai gadi da tawa motar ya d'aukoku, don kin san baya cika son kuna shiga lift dat's why banyi gangancin fad'a masa cewar taimakonku akai bah... Yadai d'anyi fadar wai meyasa ba'a sanar dashi bah aka barshi acikin duhu... "
Tasowa nayi na rungumota, nace"Ummata thank you so much for everything...I love you so much mother"
Ahankali tace"Stop thanking me my baby...ai ciwon 'ya mace ta 'ya macece... "
"Exactly mommana.. " Na fad'i hakan sanda muka fice daga dakin zuwa bangaren Abba.
Azuciyata nace"Allah sarki ummata da'ace kin san Mubarak nada Mata harda 'ya nasan da kin fini bakin ciki kuma ba zaki taba bari na aureshi bah... am scared of ur reactions duk randa kika yi find out.... Ya Allah! gani gareka... Kai kadai kasan abinda zaiyi daidai ga rayuwata... Allah ka zabar min miji mafi alheri.... "
Atake naji wasu hawaye masu d'an d'umi sun gangaro saman kumatuna, da sauri na goge kada Umma ta gani. Har muka iso falon Abba hira take min.
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻
Mubeen ne kwance saman d'aya daga cikin kujerun falonsu, yayi matashi da hannun kujerar da yake kwance akai. Hanan ce ah kicin tana wanke kwanonin da suka yi breakfast dasu.
Mubeen ya d'auko wayarsa ya sake sanya k'iran Fadima akaro na barkatai tunda gari ya waye. Wannan k'aron yaci sa'a K'iran ya shiga wanda hakan ya sanyashi mik'ewa da gudu yana kwalawa Hanan k'ira.
"Wifey am lucky... Yanzu line d'in sister d'inki ya shiga... "
Jin hakan ya sanyata saurin dauraye hannayenta ta nufo falon da murnarta tana fad'in"Hubby are u serious? "
Bai samu damar bata amsa bah don tuni Fadima tayi picking call d'in har sun mah soma magana, ganin hakan ya sanya Hanan komawa kicin don kada ta saurari abinda zasu ce. Hawaye masu d'umi taji sun zubo mata saman kumatu ayayin data ji wani mugun kishin Zahra ya tokare mata kirji. Zafi sosai kirjin ke mata bana wasa bah.
Kuka ke neman kufce mata amma sai tayi kokarin dannewa kada Mubeen yaji. Ah sanyaye ta cigaba da wanke-wankenta.
Bangaren Mubeen kuwa bayan Fadima ta d'aga call din,wani sassanyar ajiyar zuciya ya sake kafin yace"Haba Zahrata kin san halin da kika sanyani ciki tun jiya kuwa? Ur line wasn't getting through sai yanzu naci sa'a ya shiga.... Ina ta tunanin halin da kuke ciki......... "
"Hey! Man relax....toh ka bani damar nayi maka bayani mana... Huh? "
Ahankali yace"Alright baby Zahra ina sauraronki.... How was ur journey? "
Murmushi nayi nace"Alhamdulillah!! Allah made the journey to be safe for us through out.... " Na rasa dalilin daya sanya na kasa labarta masa gaskiyar lamarin yadda motarmu ta lalace da kuma yadda Engr. Mahmood ya taimaka mana.
Yace"Okay baby toh meya hanaki kunna wayarki diz morning after charging it? "
Advertisement
"Wallahi was so much tired... Inata bacci, tashiwata kenan mah na kunna wayar, sai ga kiranka ya shigo" Na sami kaina da yi masa wannan k'aryar.
Cike da kulawa naji yace"Babyna ai dole ki gaji... Tankx for coming and am really sorry for everything including duk wulakancin da mahaifiyata tai wa 'yan'uwanki.... Kuma insha Allah ni Mubarak ina mai yi miki alkawari da cewar.... Muna gama waya yanzu zanje na sameta na fad'a mata cewar ke nakeso kuma ina son na aureki....... "
Da sauri nace"Anya Mubarak kana ganin zatayi na'am da Zancen nan naka kuwa? "
Wani bangaren zuciyata kuma yace"Idan har mah ya samu ta amincen, ke mahaifiyarki zata amincen ki auri mai mata ne? "
Murmushi naji yayi yace"Zahrata kisa aranki kamar ta riga ta gama amincewa ne..... Ke dai kawai ki soma shirin zama amaryar Mubeen..... "
K'arar fashewar abu yaji akicin wanda jin k'arar ba karamin firgitasa yayi bah,da sauri yace"Babyna will call you back later please.... "
Ya yanke call d'in ayayin daya nufi kicin da saurinsa. Abinda ya gani ne ya matukar tsoratashi, nan da nan idanuwansa sukai jawur kamar garwashi, jijiyoyin kansa suka mimmike tamkar zasu tsinke.
Salati kawai yake yi yana dada nanatawa"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Hanan mai zan gani haka? "
Glasses ne atarwatse akasa duk sun sha jini ayayin da tafin hannun hagunta duk jini ya gama wanke mata shi har yana zuba akasa.Kukan da take rerawa ahankali, ayanzu ta samu sararin fitar dashi fili ah sa'ilin da tayi ido hudu da Mubeen.
Da sauri ya rugo hannun nata yana fadin"Sweetheart garin yaya hakan ta faru? "
Ahankali tace"Hubby tsautsayi ce kawai which I can't explain how it happens.... "
Yace"Yanzu dai muje nayi miki dressing d'insa kada jinin ya gama tsiyayewa kinga kina da juna biyu.. "
Ya fad'i hakan tare da ciccib'arta yayi dakinsu da ita, don shi sam bai yadda da wannan batun nata na wai tsautsayi bace, shi dai jinta kawai yayi amma ba wai yayi believing bane.
Bathroom ya kaita ya wanke mata hannun sannan ya dawo da ita ya ijjeta saman gado. Zuwa yayi ya d'auko first aid box don Likita kamarsa baya wasa, yakan ijje wasu kayan aikinsa agida incase of irin situation na Hanan yanzu.
Dressing din hannun yayi da bandeji bayan ya gama treating d'insa da maganin injury wato 'iodine'. Sai kuka take don zafi.
Shi kuwa sai aikin cewa yake"Sorry babyna it shall be well with you... Sannu kinji... "
Yana gamawa ya bata magunguna tasha, ciki kuwa hadda na bacci don she need to rest.Ai kuwa tana gama sha koh Mintuna goma ba'a dauka bah, wani nannauyar bacci yayi awon gaba da ita.
Gaskiyar lamari kuwa shine,alokacin da Mubeen ke waya da Zahra, sanda yacewa Zahra 'ta soma shirin zama amaryar Mubeen' da karfi yayi wannan maganar, wanda kuma Karaf! akunnen Hanan d'in.
Alokacin tana wanke wani glass cup ne taji wannan maganar, wanda hakan ya sanya bata san sanda ta yamutsa glass cup din da hannun hagunta bah don zafin kishi,shi kuma cup d'in azabar daya ji ne ya sanyashi tarwatsewa har ya jijji mata ciwo, daga bisani ta watsar da tarwatsassun glasses d'in akasa alokacin data jiyo takun Mubeen ya nufo kicin d'in.
Mubeen kuma ganin bacci ya d'auketa ya sanyashi sakin wata wahalalliyar ajiyar zuciya.Ya tafi kicin d'in, yayi clearing wajen da glasses d'in suka tarwatse tare da mopping d'in wajen.Yayi spraying wani liquid perfume mai kamshi awurin. Nan da nan wajen ya d'au kyalli da wani fitinannan kamshi.
Ahankali yake magana da kansa"Haba Hanan d'ita meyasa kika cika sona da yawa ne har ya janyo kika yiwa kanki illa haka? Hanan nima zanfi so ace na zauna dake ke d'aya amma kuma ina ganin hakan ba zai yiwu bah sabida yadda Allah ya jarabceni da son '
Ji yayi kamar ana bugun gate d'in gidansu. Don haka da sauri ya fice don dubo koh wanene.
Bugu ake bana wasa bah. Azuciye yace "Don Allah ana Zuwa mana... "
Yana gama bud'ewa yayi arba da Mummy, Engr. Mahmood da kuma Usman kaninsu.
Gabansa ne ya shiga faduwa sanda yaga Mummy ta jefesa da wani mugun Kallo.
Cewa tayi"Tunda jiya wucewarku kukai babu koh sallama don kasan laifin daka aikata dat's why kaki shigowa toh gashi nan ni na biyoka da kaina muyi magana.... Don haka ni bani hanya na shige.... "
Da sauri ya basu hanya suka shigo cikin gidan,lek'awa yayi yaga motar Engr. Awaje.
Ahankali ya maida dubansa ga Mahmood wanda duk jikinsa asanyaye yake, yace"Brother ba zaka shigo da motar bane? "
Engr. Ya juyo yace"No, tace ba dadewa zamuyi bah don nima ina da wurin Zuwa ta sanya na kawosu... "
Jin hakan ya sanya ya maida kofar ya rufe, sannan ya juya ya nufesu wanda tuni sun riga sun shige cikin falon har mah sun zazzauna.
Cike da rashin kuzari ya nufi inda Mummy ke Zaune sai faman aika masa da sakonnin harara take.
Russunawa yayi yana gaidata"Mummy an kwana lafiya... ? "
Saurin taran numfashinsa tayi"Da ban kwana bah Zaka ganni da safiyar nan agidanka? "
Shiru yayi mata,ganin shirun nasa yai yawa ya sanya ta cigaba"Ina ita Hanan d'in take mai shegen son miji da har zata iya tunanin had'a kai da kai ta hanyar boye min abu kamar haka... Toh albishirinku duk naji komai da kuka yi discussing awaya jiya.... "
Da karfi tace"Nace ina take? "
Da sauri yace"Tana kwance bata ji dan dadi bane, ta samu bacci ya d'auketa. "
Cikin halin koh ajikina ta cigaba"Wannan kuma ita ta sani...kadan mah ta gani kenan na rashin jindad'i idan har ta cigaba da baka goyon baya ka karo aure.. Idan banda abin shashashar mah wacce macece take kaunar ayi mata kishiya? "
"Toh wallahi Mubarak ka bud'e kunnuwanka ka saurareni da k'yau... Kama cire batun yarinyar nan acikin zuciyarka don muddin ina raye kuma ina numfashi adoron kasar nan toh wallahi bazan taba bari ka auri wata mace bah... Matarka d'aya anan aduniyar, kuma itace 'Sai dai idan so kake ka nuna min cewar bani 'ce na haifeka bah...... "
Da sauri ya d'ago jajayen idanuwansa yana kallonta,yace"Mummy kin isa dani kuma ni kallon uwar data haifeni nake miki.... Amma mummy ina son Zahra kuma ina son na aureta ba wai kuma don na daina son Hanan bane.......... "
Da sauri tace"Mubarak ayau ni kake fad'awa ra'ayinka?.... Ina baka umarni amma kai kana neman ni nabi ra'ayinka......? "
Kokarin magana yake, ba zato bah tsammani yaji Engr. ya sako baki"Kai ana nemar zab'a maka abu mai k'yau ga rayuwarka amma nema kake ka kawo taurin kai.... har nawa kake da har mummy take zartar da hukunci akanka kake nemar ta bi naka ra'ayin?..... wai ni mai mah ka nema ka rasa ne agun wannan yarinyar kirkin Hanan da har kake neman jajibo wa kanka fitinar k'aro aure? Koh baka san wani sa'in keeping more than one wife fitina ce ba?.... Bar ganin Mummy da Umma(mahaifiyar Mubeen) sunyi zamar lafiya kayi zaton koh kaima hakan za'a samu anaka gidan.... Sam, it might turn out to be a negative view in ur own case..... "
"Brother pls stay out of diz... Bah damuwarka bace idan mah na tara mata d'ari acikin gidana tunda dai ba'a cikin naka gidan zan ijje su bah, its non of ur business..... Wannan maganace tsakanina da mahaifiyata don haka ka cire bakinka aciki.... Ka kuma kama girmanka...... " Mubeen ya fad'awa Engr. Wannan maganganun cikin zafin rai.
Mummy ce ta wanke masa fuska da Mari tana huci"Iyyeh Mubarak rashin kunya zaka yiwa dan'uwanka na gaba da kai akan 'ya mace? "
Kafin ta gama rufe baki taga Engr. Ya mike shima yana huci, ya tunkaro inda Mubeen yake yana fad'in"Mubarak ni kake fad'awa na kama girmana kuma na cire bakina acikin maganarsa? "
Mubeen shima mik'ewa yayi ba tare da ya damu da Marin da Mummy tayi masa bah, yace"Mahmood an fada maka hakan.... Do ur worst.... "
Da gaske fah so suke suyi dambe, don sanda Mahmood ya tunkaro inda Mubeen yake, mubeen d'in hadda cire T-shirt d'in jikinsa yayi.
Mummy ce tace"Wallahi kar ku kuskura kuyi min dambe anan.... " Ta fad'i hakan cikin tashin hankali don ta san dukkansu akwai shegen zuciya.
Hanan ce ta fito falon don hayaniyarsu ce ta tasheta. Ah daddafe ta fito falon don jirin da take ji.
Ganin Mijinta da Mahmood na shirin dambe ya sanyata fashewa da kuka, da sauri ta nufesu tana fad'in "Abu jasmine pls kar kayi fad'a da dan'uwanka akan mace..... Yaya Mahmood pls ku bari" Arude take fadin hakan...
Tuni Mubeen yakai wa Engr. Naushi ahancinsa................... 📝
HAFNAN'S POV
Hahaaha!!! Anayi muna shan Lipton agefe..... Anfa zo gun dearie's
Don Allah muna barar addu'a agareku... Matar wana is seriously sick... Ur prayers are all needed pls... Thank you all!!!
Pls ignore any errors seen ayayin typing d'ina... Kun san nobody is perfect!!!
SAHIBARKU CE
©QUEEN HAFNAN©
Advertisement
- In Serial11 Chapters
Erased
Alone in a vast expanse of knowledge and void of any previous memory what else was I to do but learn? The world above awaited me, but down here it was all I could do to read about it, prepare for it. How long would it take for me to see my first of the Learned Races, or encounter my first monster? To simply see a [City Guard] or a [Warrior] maybe even a [Mage], even then I'd be sated no matter how basic the Class. I wanted to witness what I read about, the fantastical [Secret Stache] of a [Treasure Hunter] or a [Pickpocket] using [Deft Hands]. These were natural occurrences above, but alas, I was below. And this deep down, I'd see my first horror before seeing any mere monster. My escape were the books but soon I'd turn that knowledge into a real escape, I'd emerge from this dear library and claw my way above. But I'd need to prepare myself, I just didn't know how yet. So back to my books.
8 225 - In Serial105 Chapters
Magic Monsters Money
Key Godfre Tanner is just your everyday normal guy, or supposed to be when one morning, he woke up with a news from his mother that he isn't a normal human, but a magician that came from another world and an arictocrat. By his mother's wish, he has to attend an academy for magicians in the other world called 'Marzenthura'.By fate's unexpected twist, he suddenly becomes the enemy of the Gods and branded as a heretic. Now, he must travel in order to find a way to retaliate against those gods.Will he be able to survive with that world's Gods against him? !Warning!*Genre changes along the way**Confusion in the story is inevitable**First few chapters are boring and stupid AF**Author is Playful with readers**Best to ignore common logic in this.**You'll hate 1-6**This warning is Stupid*
8 158 - In Serial35 Chapters
Lazarus: Death's Companion
After years of studying the occult, 85 year old Morris has found a way to be reborn into an immortal body in a another world. However, it comes at the cost of his humanity. Morris is reborn into this new world with High Magick as Lazarus the Lesser Lich. Thrown into the Saint Theocracy where he knows no one and nothing, Lazarus must make a new (un)life for himself. This is a living story, meaning events are sometimes chosen from dice rolls. Even the writers will not always know what will happen next! Suggestions on direction, skills and new characters welcome. This is a first draft. Updates Tuesdays, probably!
8 140 - In Serial9 Chapters
Forgotten
Lee doesn’t know who he is. He doesn’t even know where he is. All Lee knows is that he’s woken up in a world filled with monsters intent on killing him. But that’s not all. The monsters here don’t really die. Some perpetual curse keeps bringing them back to life. And it’s affecting him as well. With each death he loses more memories—memories he must fight to regain by defeating more and more powerful foes. His only hope lies in a tattoo on his hand that seems to gain him power from his fallen enemies. But between his lack of memories, the odd messages that appear before his eyes and the nightmarish creatures of the world, Lee might just go mad first. When he meets a mysterious woman who tasks him with finding an end to the curse, Lee realizes it will take more than just his wits and instincts to survive. Lee will need to gather weapons, find allies and build a stronghold to destroy the evil permeating the world. But as he recovers his lost memories, Lee realizes that this may not be the first time he’s tried to save this world. He’s failed at least once before, and unless he can figure out where he went wrong, he could be doomed to repeating history. Forever... For fans of dark fantasy and the soulsborne series.
8 205 - In Serial82 Chapters
Fire & Ice - A Draco Malfoy fanfiction
Eleanor Selwyn and Draco Malfoy had three things in common: a high, pure-blood status, academic talents and Slytherin house.Other than that, they were complete opposites and hated each other. That was rather unfortunate, as the Selwyns and the Malfoys had been part of the same social circle for decades. They went to the same parties, visited the same shops and restaurants and visited each other far more than Eleanor would have liked.If it were up to their mothers, they'd already have been betrothed, but ever since birth, the two were like fire and ice. But what happens when ice gets too close to fire?
8 503 - In Serial41 Chapters
The Steele Brothers (Completed)
Adopted Brothers Jett, Raven, Ash and Grey Steele, were campus kings.Their parents were huge benefactors at the university, there was even a building with their name on it. Even without that, everyone knew who they were, knew their exploits, after all everything they did was watched by all... they ruled simply because everyone either wanted to be them or be with them.Viridian Waters incoming student... shy, curvy and ready to focus on her studies, her plan to get all her uni years over as soon as possible. She had no plans to socialise, she was here to learn. She had her own secrets.The ultimate challenge, a girl who ignored them, it had been a long time since that happened, who did she think she was. Who will win her, they are all up for the challenge.But as the chase begins...Others are threatening what they want, what will they do to keep her safe? Will she let them?Or would they be the ones learning a lesson...
8 202

