《HASEENAH》PAGE 111&112
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story & written
By👇🏻
'''Aysher Abbakar ChuChu (Meerah)'''
® *Real Pure Moment of Life Writers* *P.M.L*💭💭💭
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
Follow me on Aysherabbakar
*111~112*
idi me gadi ne yayi saurin wangale gate Jin yanda ake horn Ana nanatawa, duk tunanin shi ya d'auka Mai gidan ne ya dawo kuma Yana sauri.
Ganin su Hajiya Zuwaira ya Sanya shi washe bake Yana gaida su Dan ya San yau ze samu 'yan canji.
Nan ko ta ciro dubu uku ta bashi ya rusuna Yana godiya.
Shiga ciki suka yi Nan sukayi parking a parking lot.
Fitowa duka sukayi suka nufa ciki, tsayawa sukayi suna sallama.
Mum da ke zaune kan kujera hanunta rik'e da remote tayi kaman ba ta ji ba, Dan ta gane muryan.
A Karo na biyu suka sake sallama Bata amsa ba.
Abba dake Shirin fita ne ya amsa sannan ya dubi mum yace" Wai ko bakiji ne?"
Kallon shi tayi sannan tace" tunda ka amsa Allah ba da Lada"
Shigowa su mummy sukayi ciki, Abba ya taresu da murna Nan suka nema waje suka xauna ba tare da sun kula mummy ba.
Ta cika tayi fam a tunanin ta zasu gaisheta.
Bayan sun gaisa da Abba ne mummy tace" dama mun kawo Maka Kaya ne ka gani"
Abba se faman washe baki yake yace" to an kawo ne?"
"Eh"
Fita mummy tayi sannan tayi magana wa me gadi da me wankin gidan.
Boot ta bud'e Nan suka cicciro akwatinan suka jera.
Kwasa suka fara yi suna kaiwa ciki mummy na tsaye wajan motar.
Tunda suka fara shiga da kayan gaban mummy ya fara fad'uwa, tanbayan kanta take wannan akwatinan fa?
Seda suka Gama shiga dashi duka sannan mummy Zuwaira tabi bayan su.
Advertisement
Nan aka bubbud'e wa Abba, ba abunda yake fad'i se "tubarkallah Allah Sanya albarka"
Duban mummy yayi da ita ma Satan kallon kayan take ganin yanda aka zuba manyan Kaya da lace's a ciki.
Saurin kau da ido tayi ta cigaba da kallon TV ta.
Fitowan saratu ne ya Sanya Abba kallon ta yace" saratu ga kayan er uwarki an kawo fa"
Cikin rashin fahimta tace" wa kenan Abba?"
" *Haseenah* ya Bata amsa.
Da sauri ta k'arasa taje ta zauna Tana d'aga kayan.
Se Santi take.
Mummy kuwa se aikin harara take watsa mata.
Duban Abba tayi tace" wa zata aura Abba?"
"Dan uwanki mana Haseen"
Tsam ta mik'e ta cire hanunta, had'a ido sukayi da mummy idonta ya ciko da hawaye.
'Daki ta wuce da gudu ta toshe baki saboda kukan da ke Shirin zuwa mata.
Mik'ewa mummy tayi da nufin barin wajan, mummy Zuwaira tace" ladidi ki dawo ki kalli kayan 'yarki ki Sanya albarka ai ma ke muka kawo ki gani"
Kallon banza mummy ta mata sanann tace" me zanyi da kayan tsiyarku, kuje tunda an shiga an fita an shanye mun yaro ta Allah ba taku ba, munafukai matsiyata 'ya'yan Allah bani ko ta halin Yaya...
Tsawa Abba ya daka mata sannan ya ce" ladidi banason rashin mutunci ki Kama kanki"
Harara ta watsa mishi sanann tace" tunda kaima sun shanye ka da ruwan rubutu sun jik'a sun baka ai seka Zo ka rufeni da duka"
Rufe akwati mummy ta fara yi sannan tace" ku tattara mun kayan d'iya Kar a banka musu wuta kaman yanda aka kashemun er uwa"
Aiko Nan mummy ta fara tsalle Tana zage zage ba ji ba gani.
Da Abba ya mata magana ma ta had'a da shi ta fara zagin shi.
Bakinta har kumfa yake d'an kwalinta Yana tintsirewa tsaban bala'i.
Advertisement
Saukan mari taji a kumatun ta Bata Ankara ba har sau biyu.
Duban Abba tayi sanann ta fara magana Tana dafe da kumatu" akan way'an Nan 'yan iskan xaka mareni?"
'Daga hanu yayi ze k'ara mata mummy ta tare shi tace" Abba kayi hak'uri, mukam ai ba bak'in kunya bane, mun Riga da mun San halinta, ta dad'e da Zama mahaukaciyar karya, se hak'uri"
Suna Gama fad'in haka suka sa Kai suka fice.
Abba ma juyawa yayi ya shige d'akin shi ya barta Nan.
Nan ta cigaba da zage zage, me gadi sun shigo zasu d'iba Kaya ma sukai mota ta bisu da wuk'a Wai duk Wanda ya shigo seta kasheshi.
Aguje suka fito daga palour, mummy Zuwaira ce ta dubesu tace "lafiya?"
Nan suka mayar mata da abunda mummy tace.
Aiko mummy suka had'a ido ita da k'annenta biyu.
A tare suka sa Kai cikin gidan mummy tace me gadi su biyota.
Mummy suka gani har yanzu wuk'an na hanunta kanta babu ko d'an kwali sekace mahaukaciya.
Se zare ido takeyi Tana huci.
Aunty Hajara ce tace ma me gadi" ku shigo ku kwashe Kaya ku Kai mun mota inga Wanda ze ta6a ku shege ka fasa"
Nan suka shigo cike da tsoro me gadi ya tsuguna ze d'au akwati, da gudu mummy Tayo kanshi Aiko malam idi ya saka ihu yayi hanyan waje.
Ganin abun bana k'are bane ya sanya su Aunty Hajara da autan su cire gyale suka aje gefe.
Mummy Zuwaira kuwa waje ta nema ta zauna a kujera tana son ganin ikon Allah.
Mummy Hajara ce ta dubi mummy sanann tace" ina kina tunanin ke mahaukaciya ce ko? To mu munfi mayaukaci hauka, in nasa a fita da Kaya ki sake wani yunk'uri kiga yanda xanyi dake"
K'walla wa me gadi Kira ta sake yi.
Lek'owa da Kai malam idi yayi a tsorace yace" Hajiya KU kaita d'aki karta kasheni"
Cikin masifa tace" Dan Allah kazo ka fita mun da Kaya in ga me zatayi"
Ba musu ya sunkuya mummy ta sake zaburowa, mummy Zuwaira dake zaune ta Sanya mata k'afa ji kake dim.
Mummy ta fad'i, d'agowa tayi bakinta har ya fashe.
Duban mummy Zuwaira tayi tace" Kika fasamun baki?"
Girgiza Kai mummy Zuwaira tayi tace" ba haka naso ba, karyaki naso nayi ki gode ma Allah ma, Dan in Kika sake wani rashin hankali wa'yannan zansa su Miki shegen duka"
Ta nuna su mummy Hajara.
Idi Kam Allah ya bashi sa'a ya fara fita da Kaya me wankin na tayashi.
Kafin kace meye fuskan mummy ya aune ya kumbura saka makon fad'uwan da tayi, bakinta har Wani karkacewa yayi.
Har aka fita da kayan Bata sake cewa komai ba.
Abba Yana jinsu a zuciyar shi ya so su mata kafirin duka su kakkaryata kaman yanda mummy Zuwaira ta so.
Saratu ma na d'aki Amma bak'in ciki ya Hana ta fitowa.
Haka mummy tana ji tana gani suka tafi ba ta iya ta6uka abun arziki ba.
Suna barin gidan Abba ya fito, ganin yanda fuskanta ya canja ya Sanya shi fad'in" kad'an ma Kika gani"
Kasa magana tayi Dan gaba d'aya fuskan zogi yake mata kuma ta kasa tashi.
Saratu ce ta fito a d'aki da niyar fita Dan ta Sha k'ananan Kaya,
Had'a ido sukayi da mummy Bata San lokacin da ta fashe da dariya ba har da tsugunawa.
Mummy ke Mata kallon mamaki.
Nan saratu da k'yar ta tsayar da dariyar da take ta dubi mummy tace" mummy kin ganki kuwa? Sun sauya miki Kama sekace gwoggon jeji"
Kuka mummy ta Sanya ta dubi saratu sannan tace"....
Half bread it's better than none... Kuyi hak'uri da wannan.
For comments 08144932303
Advertisement
- In Serial109 Chapters
Beyond Humanity: Lightning Falling and Hook of Rage
Humanity reaches deeper and deeper into space with its starships and Space Cities. Maybe their technology and curiosity has taken them too far? A scientist and an electrician walk down separate paths following the clues and secrets of the powers. Magical powers that let some shatter boulders with their fists and some discharge beams of ice from their palms and more. Everyone is different, and specific mental traits are key. There are many secrets left to discover. A man cloaked by mystery and power works from the shadows, he has been given the tools to ensure humanity’s place in the Universe. The future of humanity, how much is it worth? Beyond Humanity will consist of three novels and all will be published in this sequence of chapters. The chapter POVs will rotate between Beth and Milo but with some guest inclusions of other characters. A new chapter will be published every Sunday, and whenever extra words drip off my fingers.
8 108 - In Serial19 Chapters
A Brief Look
Spaceships, programming-based magic, eldritch abominations called humans, conspiracies, really what more could you want? Oh, and, escalation. Fair bit of that too. Also posting this on r/HFY.
8 126 - In Serial14 Chapters
Chaos World
Tal is just your everyday normal teenager stuck in a world of superheroes. On the day his dad takes him on another one of their apocalypse prep camping trips, the not-so-unexpected happens. An apocalypse...of sorts. The world is irrevocably changed, but Tal has the skills to survive or die trying.
8 192 - In Serial24 Chapters
Dragon Boy
Chapter One of a story I started. I'm only posting chapter one to get some feedback so I can see what works and what doesn't.It was a normal assignment: "parent" an egg for two weeks to learn about responsibility. For Kyle, however, the end of the assignment brings about a whole new beginning.
8 199 - In Serial21 Chapters
The Shinto Gods Series: The Imperial Seal(On Hiatus)
Kasumi doesn't have a childhood. At least that's what she thinks. One minute she was learning in Elementary and the next she became a renowned model. Her life always went with a blur and she hated that. She wanted to live the moment but with a mysterious fox, she might be able to. If she lives that is.A modern twist in Shinto lore, follow Kasumi Fujiwara, a Japanese demigod, to a camp hidden all these years. And she's the only one to unravel it's secret.TW (TRIGGER WARNING): Blood, violence, character death(s), slight gore
8 213 - In Serial5 Chapters
The entity
entity 303 a name or a title feared by people as he had the power of both destruction and creation... BUT that was all a legend or ... was it?. izuku yagi a child discriminated for being powerless you see the whole world is filled up with super powered people ranging from quirks to semblances, but him he was powerless and because of that he was often bullied by his sister and his so called friends that would one day become class 1A and you might think his parents are treating him good, WELL NO they neglected him for his sister, but he did have a few friends but they left with no explanation why and where they are going so izuku was alone. one day they took it too far and left him on the ground all bloody with his left arm missing he then struggled going into the forest and just laid down there waiting for death.... you are going to need to read the story to find out what happens next. none of the animes or the games in this story are mine nor are the art only the story is mine
8 124

