《HASEENAH》PAGE 103&104
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS- 08144932303
# http://
Follow me on Aysherabbakar
*103~104*
Sunkuyar da kai Sameer yayi ya kasa magana se ajiyar zuciya kawai yake.
Seda daddy yace ya kwantar da hankalin shi ya fad'a mishi abinda ya faru.
Cikin mutuwar jiki da sanyin murya ya ba daddy labari tun dalilin had'uwar su da haseenah har kawo matsalar da aka samu da kuma dalilin barin ta gidan.
Shuru daddy yayi zufa na karyo mishi.
Mik'ewa yayi ya shiga ciki ya ce duka su samesu a palour.
Umaimah da ke tsaye bakin k'ofa tana bubbugawa akan haseenah ta bud'e mata k'ofa amma tak'i.
Kallon daddy Umaimah tayi kaman zatayi kuka tace" daddy kazo ka mata magana ko zata ji naka ta bud'e"
Mummy dake cikin d'aki batasan me yake faruwa ba ta fito tana tanbayan lafiya?
K'arasa wa k'ofar yayi a hankali yace" haseenah tashi ki bud'e kofar inason magana dake"
A hankali ta mik'e ta bud'e k'ofar ta sunkuyar da kai tana sharar hawaye.
Mummy ce ta dubeta ganin fuskanta yayi ja idonta sun kumbura tace" me ya sameki haseenah? Bakida Lafiya ne?"
Girgiza kai kawai tayi alamar a'a.
Dady bai sake cewa komai ba yace duk su sameshi a palour shi yanason magana da su.
Juyawa yayi ya tafi.
Hijabi haseenah ta saka sannan duka suka bi bayan shi.
Zaune ya ga sameer kanshi a k'asa.
Dukan su zama sukayi banda haseenah da ta takure waje d'aya kamar mara gaskiya.
Daddy ne ya dubi haseenah sannan ya kira sunanta.
Cikin dashashshiyar murya ta amsa, a karo na biyu daddy ya ce" ki d'ago ki kalleni"
À hankali ta d'ago tana duban shi.
Nuna mata sameer yayi yace" kinsan wanann?"
Gyad'a mishi kai tayi .
Girgiza kai daddy yayi sannan yace" sameer inaso ka basu labarin da ka bani"
Advertisement
Cikin sanyin murya ya fad'a musu komai.
Mamaki da tashin hankali ne kap ya bayyana fuskar su.
Daddy ya cigaba da cewa" Sameer ko kasan auran haseenah saura kwana 28?"
A gigice ya d'ago ya dubeta sannan ya mayar da kallon shi ga daddyn, bakin shi har rawa yake ya kasa magana sai hawaye.
Shuru palour ya d'auka banda sheshshekar kukan haseenah ba abinda kake ji a palour.
Ita kanta ga rasa kukan me take yi.
Shuru palour yayi daga bisani daddy ya yi faɗa ma haseenah kan meyasa ta b'oye musu gaskiya.
Hak'uri daddy yayi ta ba ma Sameer saboda sunyi halacci wa haseenah.
Nazari daddy yake sosai daga bisani yace" In bazaka damu ba zan baka 'yata ka aura in kanada ra'ayi"
Daddy ya k'arasa maganar tare da nuna Umaimah.
Duban Umaimah sameer yayi itama ma shi take kallo.
Sunkuyar da kai tayi k'asa saboda tun da ta d'aura idonta kanshi taji ya mata dama gata da son kyawawa.
Daddy ne ya katse musu shurun ya cigaba da cewa" bazan maka dole ba, kaje gida kayi nazari da tunani in ka yarda kuma kun sasanta kanku zan haɗa auran da na haseenah in har a shirye kake.
A hankali Sameer ya gyad'a Kai sannan yace" ba komai daddy na gode Allah ya saka da Alkhairi, In Shaa Allah zuwa Jibi zan dawo"
Allah kaimu daddy yace sannan sameer ya mik'e jiki ba k'wari ya fice.
Da k'yar ya iya ya ja motar ya isa gida saboda sarawan da kanshi keyi.
Ga wayar shi se faman ringing take, duba fuskar wayar yayi yaga Ammi ce ke kira.
Kasa d'auka yayi, a haka ya isa gida.
Yana shiga ya fad'a kan gado ya dafe kanshi.
Wayarshi ce ta cigaba da ringing, yasan Ammi ce, da k'yar ya d'au wayar ya kara a kunnen shi, a hankali ya ce" ina wuni Ammi"
Jin shi wani iri ya sata fara jero mishi tambayoyi, " son me yake faruwa ne? U sounds somehow baka da lafiya ne?"
Advertisement
Girgiza kai yayi sannan yace" Ammi na rasa haseenah, Ammi haseenah Auré zatayi, Ammi ya zanyi da rayuwa ta? Ya zanyi da son haseenah cikin zuciya ta?"
Kuka ya fara yi kaman k'aramin yaro, hankalin Ammi a tashe ta ke bashi baki nan ta shaida mishi gobe zasu taho Kano.
Washegari Ammi da Mahmud suka biyo jirgin k'arfe 9 na safe, ba 6ata lokaci suka iso gidan.
Kwance yake kan kujera sanye da jallabiya fara, fuskan shi na kallon ceiling, maganganun daddy kawai ke mishi yawo, ga kuma fuskar Umaimah da ke gani duk da yana cikin tashin hankali amma ya ga tana da kyau sossai.
Shafa kanshi yayi had'e da furzar da iska me zafi.
Shigowan Ammi da Mahmud ya sanya shi tashi ya zauna, zama Ammi tayi gefen shi ta dafa shi sannan tace" son kayi hak'uri komai me wucewa ne, duk abinda kaga baka samu ba dama can ba rabon ka bane"
Nan ta cigaba da mishi nasiha, ko ba komai hankalin shi ya kwanta, kuma zuciyar shi ta amince mishi da Umaimah.
Nan ya sanar da Ammi yanda sukayi da daddy, sossai taji dad'i sanann tace" to son kai ya kace musu"
"Ammi nace gobe zan dawo duk yanda ake ciki zan sanar mishi"
Dariya tayi sannan tace" ai ko tare zamuje nima inason ganin haseenah"
Haseenah ko na can duk damuwa ta ishe ta , bata cika magana sossai ba se In ya zama dole, mummy ce tayi ta bata baki sannan ta d'an sake.
Washegari da safe k'arfe 10am Ammi suka iso, me gadi ne ya shiga yace ana sallama da daddy.
Fitowa daddy yayi, ganin Sameer ya Sanya shi murmushi, fitowa a motar Sameer yayi ya gaida daddy sanann ya sanar dashi tare da momyn shi suke.
Nan yace su shigo ciki.
A palour Ammi Dukan su suka zauna, nan ya shiga ya sanar da mummy zuwan su.
Nan aka kawo musu drinks da snacks aka ajiye musu.
Mahmud ko se baza ido yake yana jiran ganin ta inda haseenah zata fito.
Daddy ne ya Sanya aka kira mishi haseenah da bby da Umaimah.
Ba 6ata lokaci suka iso, k'ura mata ido Mahmud yayi.
Gaban Ammi ta k'arasa ta zube tana gaida ta
Girgiza kai Ammi tayi sannan tace" bazan amsa ba haseenah, dan baki kyauta ba"
Hawayen da bata so ya fito ne ya k'arasa gangaro wa.
Cikin rawar murya tace" dan Allah Ammi ki yafeni bazan saké ba"
Janyota Ammi tayi ta rungume ta tana buga bayan ta.
Seda tayi shuru sannan Ammi ta d'ago ta ta zaunar da ita gefen ta.
Gyaran murya daddy yayi sannan yayi bayani wa Ammi yanda sukayi da Sameer.
Murmushi Ammi tayi sannan tace" ya fad'amun kuma mun amince da wannan halacci Allah bar zumunci"
Duka suka amsa da Ameen.
Ammi ce tace " to wacece surukar tawa a ciki?
Nuna Umaimah dady yayi da ta sunkuyar da kai...
" Masha Allah taho kusa dani 'yata"
À kunyace Umaimah ta k'arasa ta zauna gaban Ammi.
Shafa kanta Ammi tayi sannan tace" Allah muku albarka"
Nan daddy Yake tanbayar su ko sun shirya a had'a auran su da na haseenah?
Gyad'a kai Ammi tayi tace ba wani damuwa, gobe zan koma Abuja in Allah ya yarda zamu kawo komai nan da sati d'aya".
Mahmud da ke satan kallon baby ya dubi daddy kaman zeyi kuka yace" Daddy Nima a bani wancan"
Ya nuna Baby.
Dariya duka suka sa sannan daddy tace" in dai kun daidaita kanku shikenan"
Duban Baby Mahmud yayi sannan yace" dan Allah ki soni kinji?"
Dariya duka suka sake yi, duban Baby daddy yayi yace" uwata kina son shi?"
Sunkuyar da kai tayi cike da kunya.
To Alhamdulillah Allah sa mu dace.
Nan suka cigaba da tattaunawa, daddy ne ya dubi Ammi da mummy sannan yace" to ku tashi mu shiga ciki mu barsu su zanta.
Ba musu suka mik'e palourn ya rage daga haseenah, Sameer, baby, Mahmud da kuma Umaimah.
Tsumul Mahmud ya mik'e ya zauna gefen baby ya dubeta sannan yace".....
For Comments 08144932303
Advertisement
- In Serial254 Chapters
Possessive Love By Powerful Billionaire CEO
My motto : Never owe anyone anything .
8 1783 - In Serial406 Chapters
The Bloodline System
In a future timeline, the earth was visited by a species known as the Slarkovs.
8 140 - In Serial77 Chapters
Their Shattered Angel
Living in a hell hole with her abusive foster parents and older brother is all she knows. Magnolia Cambell's body is covered in scars of her past and her present, as she tries to fight her way through life. She thinks she is unfixable, knowing only pain, hatred and anger. On top of that, she has experienced death from both her parents and the one boy who took her heart one night in a black Bugatti.She tries to forget, but little does she know that there is one thing her mind decided to already forget ; everything that happened before the deadly accident of her parents when she was only 6 years old. Trauma made her forget everything. Her true and only family, her brothers.What happens when one dark day a boy who has the same features as her, enters the coffee shop she works in, only for her to find out that he is one of her long forgotten brothers...One of her five brothers who happens to be extremely rich and handsome. Their intriguing life style will turn her life upside down and her life won't ever be the same as before. But you know what will remain ? Her passion for illegal racing, which will only grow and drag her into darker places...Read the rest to see what will happen to the story of Magnolia Rose Knight...Cover made by this amazing person : @_navyblueee_{ careful the story moves on pretty fast in the beginning} No°1 in teendramaNo°1 in foster homeNo°1 in protective brothersNo°1 in broken familyNo*1 in racing No*2 in TeenNo*14 in Story
8 1019 - In Serial30 Chapters
The Innocent Salvatore (Niklaus, Elijah and Kol)
A baby's cry pierces the air as the midwife passes the baby to the awaiting hands of the father. Damon happily takes the baby from her hands holding her close to his chest not worried about the blood most likely staining his clothes. As quickly as the moment began it was lost, Damon was pushed out of the small room the baby still in his hands. "Stop! Wait! What's going on?" Damon yells trying to get back into the room. That's when he gets a look into the room noticing the many midwives rushing around attaching things to his wife lying on the bed, covered in blood and sweat from just giving birth."Ruby! Ruby!" Damon yells over the loud cries of the baby in his arms. Damon stops yelling the shock to great. He hears the midwife's declare her dead, the blood loss to severe. In that one lonely moment Damon realizes that he will do everything he can to keep the little girl in his arms safe, no matter the cost.---------Angels Mother died when she was only a few minutes old leaving her in the hands of her father, the great Damon Salvatore. Who knew that that one special little girl would later have three of the most powerful men in the world wrapped around her finger?------This is kind of an AU but I will follow the plot the best I can.(Kol Mikaelson X OC X Niklaus Mikaelson X Elijah Mikaelson)(The beautiful covers are by @heartsails)
8 148 - In Serial15 Chapters
A strange version of ipkknd
This is really a strange version of ipkknd. You'll get to see that side of your favourite character which you never thought existed. So... ready to see my version of Arshi?
8 137 - In Serial24 Chapters
Mr and Mrs Malfoy | Hermione x Draco
- "𝐀𝐟𝐭𝐞𝐫 𝟐 𝐦𝐨𝐧𝐭𝐡𝐬 𝐌𝐫. 𝐃𝐫𝐚𝐜𝐨 𝐌𝐚𝐥𝐟𝐨𝐲 𝐰𝐢𝐥𝐥 𝐜𝐡𝐨𝐨𝐬𝐞 𝐰𝐡𝐨 𝐡𝐞 𝐰𝐚𝐧𝐭𝐬 𝐭𝐨 𝐬𝐩𝐞𝐧𝐝 𝐭𝐡𝐞 𝐫𝐞𝐬𝐭 𝐨𝐟 𝐡𝐢𝐬 𝐥𝐢𝐟𝐞 𝐰𝐢𝐭𝐡." -#1 in hermionexdraco#4 in Dramione #397 in Random#133 in story DISCLAIMER: I DON'T OWN THE CHARACTERS!! WISH I DID BUT I DON'T!!
8 144

