《HASEENAH》PAGE 101&102
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS- 08144932303
# http://
Follow me on Aysherabbakar
*101~102*
Jallabiya ya Sanya sannan ya d'au Key ya fice, agogon hanunshi ya kalla k'arfe 12:30 na dare, bai damu da lokaci ba, motar shi ya shige yayi horn me gadi Ya bud'e sannan ya fita aguje.
Zaga Garin kawai yake ba tare da yasan inda ya nufa ba, har wajan k'arfe 2 yana abu d'aya, ganin wajan shiru a dole ya juya ya dawo gida zuciyar shi cike da tunani.
Ji yayi cikin shi na murd'awa sai a lokacin ta tuna da tun breakfast har ynxu ba abinda yaci.
Kitchen ya shiga ya dafa Lipton sannan ya fito yana sha a hankali ba don yana jin dad'i ba.
Haka ya zaune har aka kira sallan asuba.
Alwala yayi ya fice zuwa Masallaci.
Seda gari ya fara wayewa sannan ya mik'e ya dawo gida yayi wanka sannan ya fita.
Ya rasa ya inda ze fara, duk wanda ya gani sai ya tare ya nuna mishi hoton haseenah amma baiyi sa'an sanin wanda ya santa ba.
Sallah ne kawai ke tsayar dashi yana yi kuwa zai ci gaba da yawo.
Da yamma mummy zuwaira ta Sanya haseenah suka tattaro kayan su suka fice a gidan, lokacin kuwa mummy ta fantama gari nema wa saratu maganin Sa'a akan haseen da kuma lalata auren haseenah.
Sai magrib ta dawo duk ta gaji, gashi gidan taji shuru babu su haseenah babu saratu ta fice yawo.
Tsuka ta ja sannan tace " an fita yawon iskanci kenan"
Sai bayan isha saratu ta dawo, mummy kuwa na zaman jiran dawowar haseenah,
Har wajan 10 ganin basu dawo ba ya sanya mum fita wajan idi me gadi.
Tanbayarshi take ko yasan inda haseenah ta tafi?
Girgiza mata kai yayi alamar a'a sannan yace" na dai ganta sun saka akwatina a mota sun fice dukan su ko tafiya sukayi oho"
Hankalin mummy ba k'aramin tashi yayi ba jin ya ambaci tafiya.
Da sauri ta juya ta shige cikin gida tun daga k'ofa ta fara k'walla ma saratu kira.
Da gudu ta fito a tunanin ta wani abun ne ya faru, ganin mum tsaye ya sanya ta cewa" haba mummy wlhy har kin razanani"
" Razana na gaba kuwa dan ubanki, Ni na fice naje can ina fad'i tashi dan ganin na mallaka miki abinda kike so kekuma kin k'ule d'aki hankalin ki kwance ko?'
Tura baki tayi sannan tace" to gani nan ai"
Duka mummy ta kai ma bakin saratu sannan tace" to dan ubanki haseenah bata gidan nan, idi yace min ya gansu da manyan akwatina sun fice basu gidan Dukansu.
Advertisement
Yamutsa fuska saratu tayi sanann tace" to Ni mummy meye damuwata da barin gidan, ai abun farin ciki ne"
Shuru mummy tayi maganganun saratu na k'ona mata zuciya sannan tace" ohhhh kin manta yau saura kwana 28 auren ta da haseen?"
Zabura saratu tayi ta dubi mum tace" yaushe aka saka ranan auren mummy?..
" Ban sani ba"
Tana fad'in haka ta juya ta bar saratu zaune a k'asa.
Kuka saratu ta saka tana birgima wai bazata yarda ba se ta kashe su duka...
Haushi da ya dad'a Kama mummy daga cikin d'aki tace" wlhy In baki tashi kin fice mun ba sena karya ki, banza shashasha kawai"
Kuka saratu take tana cewa mummy ta temake ta Amma ko kallon ta mummy Bata yiba.
Tashi saratu tayi ta shige d'aki, jakarta ta bud'e ta ciro kwalin sigarin ta da lighter ta shige toilet.
Zama tayi kan toilet ta kunna ta fara busawa, yana k'arewa zata sake kunna wani.
Seda ta sha kwali d'aya sannan ta hak'ura, gaba d'aya wajan ya d'au hayak'i ba abinda kake gani.
Ji tayi kanta na juyawa da k'yar take iya bud'e idon ta, tashi tayi ta wuce bedroom d'inta ta zube kan gado had'e da dafe kai.
Bata san lokacin da bacci ya d'auke ta ba ba sallah ba salati.
Washe gari da yamma su haseenah suka shirya suka fice a motar ta ita da su baby, Umaimah da Aaman.
Dukan su dogayen riguna suka sanya amma kowa da colour nashi, haseenah dake sanye da bak'i ta rolling gyale ta Sanya glasses a fuskanta.
Shiga motar sukayi suka harba titi, kai tsaye wajan shak'wata suka nufa, nan ta ajiye motar ta suka fito.
Neman waje sukayi suka zauna aka kawo musu menu.
Kowa ordering abunda yake so yayi suka fara shan ice cream suna hira.
Umaimah na faman d'aukar su a hoto, nan suka 6ata lokaci ana k'ok'arin kiran magrib sannan suka mik'e sukayi ordering snacks suka fice.
Hold up ne ya rik'esu wajan traffic, tsuka haseenah tayi sannan tace" wannan zasu b'ata mana lokaci gashi mum tace kar muyi dare"
Farar motor ya hango dake d'an gaba da shi, kallon window motar yayi wajan zaman driver Amma bai ci sa'ar hango wanda ke driving d'in ba.
K'irjin shine ya fara dukan uku uku, gani yayi me motar ta sako hanunta ta window ta dafe kai.
Zoben da yagani hanunta ya sanya yaji ta burge shi, haka kawai yaji yana son ganin yarinyar..
Matsawa da motar shi yayi ya iso dai dai wajan da take, gaban shi ne ya bada sautin dammmm, ganin wanda ke cikin motar Ba k'aramin rikicewa yayi ba, k'ok'arin bud'e motar shi yayi dai dai lokacin traffic light ya Basu hannu.
Advertisement
Ganin zata 6ace mishi ya sanya ba ma motar wuta ya rufa mata baya.
Duk da ta mishi nisa amma yana iya hango motar su, wata kwana yaga ta shige nan shima ya bi, amma sedai me? Ba ita babu labarin ta, kalle kalle ya fara yi dan ganin hanya ya rabu biyu, ya rasa wanne tabi, dukan sitiyarin motar yayi yayi wata k'ara ya buga kanshi kan sitiyarin ya fitar da wani iska me zafi.
Dafe kanshi yayi da yaji na faman sara mishi, da k'arfi ya furta " Haseenah why?"
Yakai kusan minti talatin anan ya kasa motsawa, duk wanda ya gani se ya tsare ya tanbaya ko ya ga wata farar mota amma babu.
Komawa gefe yayi ya parking motar shi ya buga tagumi,Allah ya bashi ikon ganinta amma ta 6ace mishi, dafe kai yayi yana kiran sunayen Allah kan ya temake shi ya bayyana masa haseenah a karo na biyu.
Ganin har lokacin ba motor makamanciyar Tata ya Sanya shi ta da motar jiki a sanyaye ya bar wajan.
Saratu kuwa da mummy tayi a gaba tana kuka.
A dole ta saurare ta Nan ta nata alƙawarin zata aura haseen ko me ze faru.
Haka sameer ya rink'a yawon shi ya koma gida.
Bayan kwana biyu ya sake dawowa anguwan.
Tsayawa yayi daga nesa yana ta faman waige waige, wani yaro ya gani ya taho, da sauri ya fito a motar ya tsare shi, nan ya nuna mishi hoton haseenah.
Gyad'a mishi kai yaron yayi alamar ya gane ta.
Da sauri sameer ya dube shi yace "da gaske kake ka santa?"
" Eh na santa sunan ta Haseenah"
Wani sanyi ne haɗe da farin ciki ya kama shi.
Nan yace ma yaron "zaka iya kaini gidan su?"
Nan ya shiga motar suka kama hanya.
Tsayawa sukayi bakin gate d'in yana neman d'an aika.
Gani yayi an buɗe gate d'in, wata budurwar yarinya ce ta fito, sallama ya mata ta amsa sannan yace" dan Allah haseenah nake nema"
Shuru tayi sannan tace " to barina mata magana"
Tana shiga ta samu haseenah ta fito wanka tana shafa mai.
Kallon ta tayi sanann tace" Aunty kinyi bak'o"
Da sauri ta dubi baby tace" Ni Kuma?"
" Eh"
" Bana nan"
Nan baby ta fara magiya tana bata hak'uri amma ko kulata batayi ba.
Daga waje taji muryan mummy na cewa" jeki bud'e mishi guest palour tana zuwa"
Tura baki haseenah tayi a shagwab'e tace" mummy Dan Allah wlhy...
" Ki tashi ki shirya kije ki sallame shi"
Harara ta daka ma baby tayi k'wafa.
Umaimah dake kitchen Bata San abinda ake ba.
Nan baby ta fita ta k'arasa dashi palour sanann ta fice..
Kusan 30mns haseenah bata fito ba, seda mummy ta koro ta sanann ta fice sanye da atampa dogon riga.
Gaban ta ne taji na fad'uwa saboda jin warin turaren da tayi, kuma ta rasa a ina tasan me irin turaren.
A hankali tayi sallama ta shiga.
Ba tare da ta d'ago kai ba ta shiga ciki ta zauna nesa dashi.
Tunda ta shigo ya zuba mata ido har ta zauna amma bata d'ago ba.
Jin Muryar shi tayi ya doki kunnenta jin an ambaci sunanta.
A razane ta d'ago da sauri tana son gasgata me Muryar.
Zaro ido tayi bakin ta na rawa ta mik'e tsaye tanuna nuna shi.
Kasa furta komai tayi sai hawaye.
Mik'ewa shima yayi ya k'araso ya zube kan gwiwar sa ya fara magana cikin wata irin murya ya fara cewa" haseenah mesa Zaki gujemu? Me muka miki? Kinsan halin da kika samu ciki? Kinsan me kika bari me ya faru bayan tafiyar ki? Kinsan halin da Ammi ta shiga da Ni kaina dalilin ki?"
Shuru yayi jin ta tsananta kuka, Muryar ta ba k'aramin k'ona mishi zuciya yayi ba, banda sautin kukan ta ba abinda ke tashi.
Nan ya cigaba da cewa" gidan mu ya zama kaman gidan mutuwa, ga Mahmud can ba lafiya dalilinki"
Toshe kunnenta tayi da duka hanunta biyu tana kuka.
Shima hawayen yake yi yana mata magiya yana fad'in" ki temakeni ki temaki rayuwar 'yan uwana ki dawo cikin rayuwar mu"
Shuru duka sukayi.
Nan ya cigaba da cewa" haseenah ki temakeni ki aure Ni na miki alk'awari zan miki duk abinda kike so, plxxxx haseenah"
Ya k'arashe maganar had'e da zubewa gabanta shima kukan yakeyi..
Ji tayi jiri na neman zubar da ita ga kanta dake faman juyawa.
Da gudu ta fice daga palour ta nufa hanyar shiga gida lokacin Abban su baby na parking.
Ganin halin da take ciki ya sanya shi kallon inda ta fito.
Fitowa yayi a motar sannan ya nufa yanda Sameer yake.
Ganin shi yayi durk'ushe ya rik'e kai yana kuka kaman k'aramin yaro.
Hakan ya tabbatar ma Abba akwai wani babban al amari...
Kama hanun shi kawai Abba yayi ya mik'ar dashi tsaye.
Hanyar palour shi suka nufa ya zaunar dashi.
Ruwa ya d'auko a fridge da cup ya zuba ya mik'a mishi.
Ba musu ya amsa hanun shi na rawa , da k'yar ya iya kur6a sau d'aya sannan ya ajiye.
D'aki Abba ya wuce ya canja kaya sannan ya dawo ya zauna ya fuskanci Sameer sannan ya fara cewa....
Cikin gida kuwa haseenah d'aki ta shige ta kulle k'ofa ta fad'a kan gado ta saki kuka me k'arfi.
Abba ne yace" ka nutsu ka fad'amun me yake faruwa?"
Da k'yar Sameer ya fara da .....
For comments 08144932303
Advertisement
- In Serial36 Chapters
The Guardian of the Stars
It was Iya's birthright to become the next Commander of the infamous Sagen Army. Their purpose was to restore and bring peace and equilibrium to all habitats in the universe. It was considered an honor to the Sagens to work under the Star Lord and his Council of Twelve Queens. Raised to be the best, she was on a path to becoming a legend. Until her whole world gets turned upside down. Deep underground secrets start resurfacing, jeopardizing their way of life. Iya finds herself in difficult situations trying to piece together the buried secrets of her people. Everything she had known to believe and trust slowly became something she could never imagine. While the enemy works to unravel everything the Sagens have achieved, the young commander falls in with the one man she's not allowed to be with. She found herself taking a path she never thought she would take... She will have to make a choice.
8 174 - In Serial9 Chapters
Here There Be Pirates: The Dragon and the Bear
After being separated in the unforgiving world of pirates and magic, once best friends, Kaida and Click, now find themselves reunited. Though, after seven years, much has changed. Now secrets, gods, and fate itself threaten to keep them apart. The children they once were are a distant memory, and who they've become are worlds apart.
8 182 - In Serial10 Chapters
Youjo Senki CYOA (SI) Fanfiction Elmer Mandel
Welcome to my Youjo Senki Choose Your Own Adventure Fanfiction, logically your comments or the lack thereof will determine the future of the good Major Elmer Mandel. (SI) (Self Insert) That being said, should your comment not drive the story in the direction you want it to go, please remember that I myself as well as other readers have our own ideas for where the story should be going. Should you want to see the story on YouTube here you have the link to my YouTube channel, might take a while. https://www.youtube.com/channel/UCElL-U5W9hW-1PeuqKPxhdw
8 137 - In Serial7 Chapters
The Demon's Soul Pearl
Anzan is the guardian spirit beast of the sealed and abandoned Great Monad Temple. He’s kept a lonely watch over his home for years, but when the seal destabilizes and the temple is opened to the world, he realizes that he cannot protect it. Torn between duty and longing, Anzan makes a deal with a demon and ventures forth with new companions, hoping to find his masters and a way to protect his home. *A character-driven cultivation story.* Comments and criticism are always appreciated.
8 166 - In Serial12 Chapters
Adventures of Alex Blackwell
Alex Blackwell was just your average everday wizard that pretended to be a psychic detective. He was fond of his work and his life. Life was easy and trouble free however case just began to pile up that led Alex into a mystert that he would soon learn to hate. Case after case will bring Alex closer to the thruth of the events surrounding him. The only question in the end is will Alex have what it takes to survive this plot and to save his city.
8 97 - In Serial26 Chapters
Tumse Na Jaane Kyuin✓
Past.. Is a tricky word. It's past, The past which has already occurred. Yet, The same past has the power to affect the beautiful present and future of oneself. Arnav doesn't come for the remarriage. Reason? Is it really needed? Khushi is heartbroken She has done nothing but cry all these days One incident of the past had overpowered her love. He had blamed her, Though not directly, But he had.. Even when she had no control over the happenings of that day. But... There's more to the story than meets the eyeCover by MeghaMiglani
8 292

