《HASEENAH》PAGE 93&94
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar chuchu (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*93~94*
Wuni ranan Mummy tayi tana zage zage, saratu kuwa ta kasa zaune ta kasa tsaye, ta shiga ta fita duk tana jiran zuwan Haseen.
K'arfe 5 na yamma kuwa Haseen ya iso, fita Haseenah tayi ta ajiye musu plastic chair dake ajiye a harabar gidan ta gefe wanda aka ajiye domin zama.
Umaimah ce ta kawo mai ruwa da drink da snack d'in da sukayi yau ta ajiye mishi.
Kallon ta yayi yace" ku dai ba a rabaku da wanan abu sannun ku da aiki"
Dariya tayi sanann tace" wanann aikin Aunty Haseenah ce"
Murmushi kawai yayi ba tare da yace komai ba.
Zuba ma Haseenah ido yayi yana kallon ta, sunkuyar da kai tayi tana Wasa da yatsun ta, kusan wasu mintuna suka d'iba a haka sanann ya daure yace" meyasa bakiso nayi ma daddy maganan auran mu? Ko dai yanzu kin dena sona ne?"
Da sauri ta d'ago ta kalleshi jin abinda ya furta.
Gyad'a mata kai yayi alamar eh.
Ganin batada niyar magana ya sanya shi cewa" tunda baki son magana dani shikenan barina tafi"
Mik'ewa yayi da niyar tafiya da sauri batasan lokacin da ta rik'o hanunshi ba.
Tsayawa yayi cak ya kasa motsa wa, da sauri ta saki hanun a hankali ta furta" am so sorry plx ba abunda kake tunani bane, amma ba komai gani nake kaman yayi wuri, amma ka samu Mummy Zuwaira ka sanar da ita duk yanda kukayi dai dai ne"
Sai alokacin yaji wani sanyi a ranshi, bai san lokacin da ya koma ya zauna ba, duban ta yayi sanann ya ce" Are U serious?"
Advertisement
Gyad'a mishi kai kawai tayi itama tana murmushi k'asa k'asa.
Nan ya fara cin snacks sunayi suna hira, jifa jifa take amsa mishi.
Can ta nisa tace " yaya Haseen dama inaso na maka magana kan komawa ta makaranta ne"
Duban ta yayi sanann yace" nima naso miki magana to amma se nayi shuru saboda nayi tunanin karkice daga dawowarki baki huta ba shiyasa"
Girgiza kai tayi alamar a'a.
" To ai ba a ciro result d'in naki ba"
" Eh zanje in Ciro"
" No ba saikin je ba in Zan tafi ki d'aukomun slip d'inki in tafi dashi"
Cikin jin dad'i ta amsa da to Nagode.
Nan suka cigaba da tattaunawa.
Can cikin gida kuwa saratu ce ta tsala wanka ta fito ta sanya kaya, zama tayi gaban mirror ta shek'a kwalliya, turaren ta d'auko ta bulbule shi duka a jikinta, ita kanta warin turaren be mata dad'i ba amma ya zatayi.
Kwallin ta bud'e ta shafa har yana gangaro wa, abun ba kyan gani.
Mummy ce ta shigo ta fara mata masifa me take jira da bata fita ba.
Nan saratu ta kalli kanta a madubi yanda tayi sai kace balamar rago, duban Mummy tayi tace" dan Allah Mummy ki ganni fa?"
" Dalla ki fita damuwar mu a samu biyan bukata, ko kin daina sonshi ne?"
Girgiza kai tayi.
Nan ta fice ko gyale babu, Baby da Umaimah dake zaune a palour suka ga fitowar ta, kasa gimtse dariyar sukayi suka tuntsire da dariya, Baby har da hawaye..
Ko kulasu batayi ba ta fice, Haseen da Haseenah ta hango zaune gefe, nan ta canja taku har ta k'arasa basu sani ba.
Warin turaren ta ne ya bugi hancin su , da sauri Haseenah ta dubi waye me wanann warin? Ido biyu sukayi da Haseenah, sunkuyar da kai Haseenah tayi tana dariya k'asa k'asa.
Advertisement
Haseen kuwa zuba mata ido yayi yana kallon ikon Allah...
Ita duk tunanin ta tarkon tane ya kama, dan haka ta hau rausaya tana fari da ido.
Dariya ma shi abun ya so ya bashi.
Kujera d'aya taja wanda ke gefen Haseen ta zauna.
Lokacin ranshi ya fara 6aci ga warin ya fara damun shi.
Dubanta yayi yace" ke lafiyar ki kuwa?"
Cikin wata murya tace" me ka gani yaya Haseen?"
Tooo fa, yau ga ikon Allah .
Ji yayi kaman zeyi amai hakan ya sanya shi toshe hanci ya dubeta yace" ke kinada lafiya kuwa? Rabon ki da wanka sati nawa? Kinji warin da kike yi amma kika iya shiga mutane?"
Sororo tayi ta na jin kalaman Haseen kaman yana zuba mata wuta..
Ganin yanda ta zuba mishi ido hakan ya sanya shi daka mata tsawa yace" ki dena kallona da wannan idanun naki marasa kyan gani"
Kasa daurewa tayi ta fashe da kuka ta mik'e ta shige ciki tana matsanancin kuka.
Baby da Umaimah suka sake kallon ta ganin duk hawaye ya jik'a kwallin da ta lapta ya gangaro sai kace wata boka.
Dariya suka sake yi sanann Umaimah tace" ga dukkan alamu maganin baiyi aiki ba kenan"
Dariya suka sake yi suka tafa.
Nan saratu ta sake cika tayi fam.
Mummy na jin kukan ta ta fito da sauri ta iske ta kan gado tana kuka.
Zama tayi tace" meye ne kuma?"
Cikin kuka saratu ta fara kora mata bayani...
Ran Mummy ya sake 6aci ta d'auka waya ta kira Aminiyar ta, ko gaisuwan arziki basuyi ba Mummy ta fara surfa masifa" amma wanann bokan d'an iska ne, abinda ya bamu ba wani aiki sai cin mutunci"
Da k'yar da shawo kan Mummy sanann tace" to ko dai batayi amfani dashi yanda ya dace bane?"
" To ina zan sani yanzu kam Ni talatu"
Duban saratu tayi tace " kinyi amfani dashi yanda nace?"
"Eh"
Kashe wayar Mummy tayi tace" karki damu k'ila an samu kuskure ne gobe zamu sake jarabawa, in Allah ya yarda kin aure shi an gama"
Dad'i ya cika saratu nan ta manta cin mutuncin da Haseen ya mata.
Sai wajan magrib Haseen ya kar6a slip d'in Haseenah sanann ya fito musu da kayan k'walamar da ya kawo mata ya tafi..
Kai tsaye gidan Mummy Zuwaira ya wuce, bayan sun gaisa ne ya sanar mata da abinda ke tafe da shi. .
Sossai taji dad'i nan tace ya sanar da daddyn shi duk yanda suka tsara shkann zata sanar ma Abba.
Cike da murna ya koma gida.
Bai 6ata lokaci ba nan ya sanar da daddyn shi, daddy ya ce ba damuwa ya faɗa ma Haseenar jibi zasuzo neman auranta.
Tsalle Haseen yayi ya rungume daddyn nashi yana godiya.
Mamaki abun ya ba daddy da Mummy duka, dan rabon da su ga farin cikin Haseen haka its been a while, tun kafin Haseenah ta 6ata.
Murna yayi tayi ranan da k'yar ya iya bacci, tunanin Haseenah ne ya sa shi gaba, sai yanzu yake dana sanin meyasa bai siya mata waya ba?
Nan ya ba kanshi amsa nan da kwana uku zai siya mata in Allah ya yarda.
Haka ya kwana cikin shauk'i da farin ciki, hango irin rayuwar da zaiyi da abar k'aunar shi kawai yake.
Nikuma nace Allah ya nuna mana Ameen....
For comments 08144932303
Advertisement
- In Serial8 Chapters
Psycho in Naruto
Psycho reborn in the Naruto world attempts to make himself the most notorious ninja of them all. Game elements to help the character along the way.
8 71 - In Serial7 Chapters
The Blunderbuss Chronicles: Jon The Traveler
Book 2 in The Blunderbuss Chronicles Jon has just finished his first major battle. Now, as a savior of his village and newly christened temporary mercenary, Jon hopes to escort Mercy back into the hands of her father in the faraway land that she and the rest of the King's Gaurd mercenary troupe hail from. After making amends with the Farm, he sets off on his first journey. Will he survive the experience? Well, he did last time...
8 180 - In Serial20 Chapters
In the Shadow of the Builders
Long ago, the world declined and eventually collapsed. But this wasn't the end of everything. Giant mechanical beings known only as Builders roam the lands, picking up the leftover pieces and repairing the cities and infrastructure of the old world. New societies popped up in their wake and for many life goes on. Lavinia lives in the sleepy town of Seventy-Seven where she spends her days tinkering, repairing, and enjoying the slow pace of life with an old-world mecha named Arlo. But even though it's a peaceful existence, it's rarely boring. When you're living after the "end of the world," you can always find something to get up to. Cover made with Wombo Dream.
8 115 - In Serial73 Chapters
Three Keys
The World Tree holds as many worlds as it has leaves. Three keys are all it takes to replace the stablilty of the nine regions with an apocalyptic war, and the possibility of total destruction. The Asgar and the Jotun hold one key apiece, and the third key changes hands from possessor to possessor. But when one of the soldiers of the Asgar deserts, that key is lost. With two keys on the loose, whomever can assemble all three can control existence.
8 130 - In Serial54 Chapters
Something Unimaginable (Niall Horan Fanfic) Book 3
Break-ups, make-ups, marriage and kids. The lives of One Direction and their families have gotten crazy but they're still trying to keep it all together. Especially Kiersten and Niall. Please read books 1 and 2 before
8 88 - In Serial9 Chapters
Fly You To The Moon (Diaval Fanfic)
"I will FLY YOU TO THE MOON..."
8 91

