《HASEENAH》PAGE 89&90
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*89~90*
Cikin kid'imewa da damuwa saratu ta k'araso wajan mum sannan tace" Mummy me ya faru?"
Cikin gigita Mummy ta Bata amsa " wallahi Haseenah ce, bata mutu ba itace"
Shuru dukan su sukayi na d'an wani lokaci sannan saratu ta sake cewa" to amma ya akayi haka bayan kuma har kabari aka saka su?"
"Nima abunda ya d'aure mun kai kenan da har yanzu na kasa fahimta da kuma gano amsar"
Mik'ewa Mummy tayi ta shige cikin d'akin, fitowa tayi hanunta rik'e da key na motor da gyalen a kafad'arta dan ko yafa shi ma ta kasa yi.
Dubanta saratu tayi sannan tace" Mummy Ina zaki a wanann yammar?"
Ta bata amsa a tak'aice" ai zama bai ganni ba, dole inje in bincika inji ainihin labarin"
Bata sake cewa komai ba ta fice daga gidan, a guje ta figi motar ta saura kad'an ta bige me gadi yayi tsalle ya koma gefe.
Bata tsaya ko ina ba sai gidan mum Haseen.
Ko parking me kyau bata yi ba ta kutsa cikin gidan, tun daga k'ofar palour ta fara k'walla mata kira.
Da sauri mum Haseen ta fito jin irin kirar da ake mata, karo suka ci tana k'ok'arin shiga d'akin.
Tsayawa tayi suna duban juna, Mummy sai faman wangale hanci takeyi, murmushi mum Haseen tayi dan abun ya so bata dariya, gintsewa tai sannan ta ce " mun wuni lafiya?"
D'aga mata hannu tayi sanann tace" ba abinda ya kawoni ba kenan"
" To ki zauna mana yaya" mum Haseen ta fad'i haka.
Ba musu ta zauna sannan ta dubi mum Haseen tace" ki fad'amun ya akayi Haseenah ta dawo kuma kinsan tana raye amma baki sanar dani ba"
Advertisement
Cikin d'aure fuska tace" yanda abun ya taho miki a bazata nima haka naji, dan Haseen ne ya kirani lokacin da ta dawo naje gidan hajiya Zuwaira na tarar da ita"
Gyara zama mum tayi dan anzo wajen, dama labarin take so taji.
Jin mum Haseen tayi shiru ya sanya Mummy cewa" uhm ina jinki se kuma me ya faru?"
Bata tsaya 6oye mata komai ba nan ta sanar da ita yanda abun ya faru.
Tun kafin ta gama bata labari riga da d'an kwalin Mummy suka jik'e da gumi, ga sanyin AC amma ji take kaman wuni tayi tana yawo a rana.
Gyalenta ta janyo ta fara fifita ba shiri tana girgiza kai.
D'aura hannu a ka tayi tana furta" na shiga uku, wanann shine anyi ba ayi ba ai"
Cikin rashin fahimta mum Haseen tace" ban gane me kike nufi ba"
" To ai an kashe maciji ne ba a sare kan ba, wanann ai shirme da aikin banza nayi"
Kan mum Haseen ya kulle dan bata gane yanda maganar ta dosa ba.
Amma ganin rikicewar da Mummy tayi ya sanya ta yin shiru.
Mik'ewa Mummy tayi ta nufa hanyar fita.
Mum Haseen na mata magana amma ko sauraron ta batayi ba.
Mota ta sake shiga ta nufa gidan k'awarta me bata shawara a fad'anta wai.
Nan ta kwashe labarin komai ta fad'a mata.
Shuru tayi tana jinjina Al Amarin, can ta dubi Mummy tace " to ke wani mataki kika d'auka?"
Wani ajiyar zuciya tayi ta furzar da iska mai zafi sanann tace" ai tunda kika ga nazo wajanki to mafitar nake nema"
Can tace " kinga dai yarinyar nan tuntuni tsoron ki take ji, to meze hana ki azabtar da ita ga yanda sai ta nutsu ta bada kai dan dole?"
Shuru Mummy tayi sannan tace" ke yanda fa naga yarinyar nan ta dawo wlhy na Razana, ga wani kyau da ta k'ara kamar ba ita ba"
Advertisement
Tsuka Hajiya Xulaihah tayi sanann tace" to meye na karaya da wuri, ki gwada abinda na fad'a miki mana in Abu ya gagara kema kinsan akwai mutumin mu ai, ze gyara mata zama"
Sai a lokacin hankalin mum ya kwanta ta saki murmushi sanann tace" shiyasa nake k'ara sonki tawan"
Nan suka ci gaba da maganar su sai magrib sanann Mummy tayi shirin komawa gida.
A tare suka danno da hancin motar su gate d'in, Haseen ne ya fara shigewa sanann Mummy tabi bayan su.
Fitowa sukayi a motar dukan su, Umaimah da Baby Suka kwashi ledodi da kayan suka shige.
Haseen da Haseenah da kuma Aaman na tsaye.
Kasa fitowa a motar Mummy tayi ta zuba musu ido, Aaamn da ta gani duk shi yafi tsaya mata a rai dalilin shi d'in na miji ne.
K'wafa tayi ta girgiza kai cike da takaici.
Sallama sukayi sanann Haseenah ta kama hanun Aaman suka shige gida.
Juyowa Haseen yayi ze koma mota suka had'a ido da Mummy.
Kau da kai yayi kaman bai ganta ba, hakan ya dad'a 6ata mata rai.
Da sauri ta fito ta tarar dashi na k'ok'arin rufe murfin motar.
Kama murfin tayi sanann tace" mara kunya ɗan iska, kaje ka 6oye yarinya kun gama iskancin ku hakan bai maka ba seka biyota gida?"
Maganganun Mummy sun masa zafi amma ya dake ya gyara zama ya dubeta sanann yace" to ai Ni nawa iskancin me license nakeyi wata kuwa uwarta na kallo ake zuwa har gida a d'auke ta sai kuma Randa Allah yayi ta waiwoyo gida"
Shuru ya ratsa tsakani sannan ya dubi Mummy ya cigaba da cewa" kinsan ya ake kiran masu irin wanann iskancin? Karuwar gaban iya"
Yana gama fad'in haka ya ja murfin motar shi ya tayar ya sa kai.
Nan Mummy ta tsaya kaman an dasa ta a wajen, kaman bishiya haka ta tsaya ta kasa motsa wa.
Kusan minti biyar tayi wajan da k'yar ta ja k'afar ta ta shige ciki.
Maganganun haseen ba k'aramin dakatar mata da tunani yayi ba, gaba d'aya ya birkita mata lissafi, wanann shine ake kiran in kasan na fad'a baka San na mayarwa ba.
Wato yau Haseen ne ya kira saratu da karuwar gaban iya?
Girgiza kai tayi ta shige d'aki.
A ranta kuwa neman yanda zata bi ta k'untata musu take.
For comments 08144932303
Advertisement
- In Serial401 Chapters
Class: Mash
In a world full of magic and power, where strength is defined by classes and levels. Follow Mash, a young boy who gets to experience the wonders of the world, from receiving his first class to realizing his dreams, and all the little progress in-between. Although things don’t go as he predicted. His first class defined him as something he was not, yet it offered him a new opportunity. Only through gaining experience and levels can he even begin to reach his dreams, whatever they may be. After having his first real fight, Mash catches a glimpse into the profound wrongness in his world. In this moment of revelation, Mash’s life takes a new path, one he will have to carve for himself. A path that was not for knights, heroes, or kings, instead one for gods, of power beyond even his own understanding. Participant in the Royal Road Writathon challenge. I upload everyday at 12:00pm cst. P.S I am working on rewriting the first couple of chapters, expect those to release slowly over the next week or so. I will keep the above schedule for the normal chapters. Thanks for reading. I will mark them with edited, when done. The story itself won't change much, i will just be adding clarification and editing it so it matches the form of the later chapters.
8 797 - In Serial9 Chapters
Mundinem
A father-son story with a weird twist, follow our two protagonist through there daily lives and experience the world that they see as normal, a land, both scared and forgotten, were day bleeds and the night does not sleep, were ancient monuments stand unfallen, but still rotting. though this adorable duo wont be let down so easily! and hopefully neither will you.
8 190 - In Serial49 Chapters
The Godfather {Being Edited}
"Ooo girl look, look, look." She tapped her shoulder repeatedly.Euphoria looked to the entrance instinctively only to see the man she had seen in the alley the first night she worked here. Her breath hitched as she watched them walk in. She never dared to tell a soul about what she'd seen that night. She wasn't looking for any trouble. Especially when he let her go."Who is he?""That bambina, is no other than Demetrius D'Agostino. The Godfather. He's basically the Capo of all the Capo's. You see Jamal is a Capo, Yes? But he is the top Capo making him the boss of Jamal and all others like him. Everybody answers to him. Nothing travels unnoticed by him. He's the King of the underworld. He owns the politicians, the President and the law. He has everyone in the palm of his hand. His family has been the most ruthless and merciless mafia family to live. Rumor has it that he's the worst society has seen but the best the underworld has ever that's led the D'Agostino family. He is all badbambina, you should stay as far away from him as much you can.""After what you just told me. I'll do exactly that. No need to tell me twice."🚫18 CONTAINS MATURE CONTENT/ ADULT THEMESDISCLAIMER: I DON'T OWN ANY OF THE IMAGES USED IN THE BOOK OR ON THE COVER‼️⚠️Read at own risk⚠️
8 312 - In Serial34 Chapters
Chains
Eric Bane is one tough thug, but even he's not immortal. After a deadly ambush, he falls unconscious only to awaken in a castle preparing to meet a king. He was apparently summoned to a parallel world of fantasy to act as a hero who wields one of six Divine Weapons. However, being unfamiliar with video games, he doesn't see the new world the same way the other five do. After being framed for rape, Eric ends up hobbling out of the city with no money, no party, and draining motivation. However, if there's one thing that Samson is good at, it's spite. If the world is going to kick him to the curb, then he's going to beat the shit out of the next person he sees to get back on track. As Eric grows stronger through a natural progression, he slowly discovers the hidden history of the world and the dark secrets of the Church of the Trinity. And while some might wait for the right moment to strike, Samson isn't one for patience. >>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>> This is a story that I've already gotten pretty far with, but I want to release it slowly over a few days to see what the critics say. I haven't finished it, but I've got a general idea where I want to go with it. Maturity for violence, sexual themes, and slavery. No outright sex or nudity, and there is no cruelty exhibited towards slaves. Tell me how you like it.
8 423 - In Serial20 Chapters
Legend of Xeor
Part of The Chronicles of Allastar. Early after the creation of the world Beasts were the Rulers of the world with physical might and low intellect acting mostly on instinct and desire. Xeor is a "Young" lionman who travels around the world of Allastar following his destiny. Might contain grammar mistakes and bad jokes.
8 84 - In Serial35 Chapters
The destiny
What will happen when two young men, are send to other world, to save it from a alone man . What will be there choice?. Will they protect it ? Or simply ran away from it. (also btw, the title before was the great rulers)
8 187

