《HASEENAH》PAGE 85&86
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
Assalamu alaikum, plx ina me bada hakuri na jina shuru da akayi first a while, these happen due to some circumstances, but in Allah ya yarda if time permits zan na typing da safe ko da yamma in posting, thank you all..
*85~86*
Bayan kwana biyu da gama gyara side d'in ummah Wanda Haseenah zata koma kaya suka iso, Mummy Zuwaira ce da su Umaimah suka zo suka gyara ko ina suka jera, Sa'a d'aya dan tun safe da Mummy ta fita bata dawo ba, haka ma saratu ita bata ma kwana a gidan ba.
Soyayya kuwa tsakanin Haseenah da Haseen sai abinda ya karu, dan ji suke kaman in Suka rabu ba zasu sake had'uwa ba, hakan ya sanya Haseen ya fara yi ma Mummy Zuwaira maganan auren su, da k'yar Mummy ta lallab'a shi tace ya hak'ura komai ya dawo dai dai sannan a fara maganar.
Da k'yar ya hak'ura ba dan ranshi ya so ba.
Haka ya hana Haseenah fita ko ina duk abinda take so sedai ya kawo mata, ita ma bata damu da fitar ba zama take a gida.
Shak'uwa me tsanani ne ya shiga tsakanin Haseenah da k'aninta Aaman.
Duk da ba saninta yayi ba amma yafi sakewa da ita, duk yanda tayi yana biye da ita.
Hakan ba k'aramin dad'i ya mata ba.
Can Abuja kuwa tunda Haseenah ta fita a gidan gaba d'aya gidan ya zama wani iri, barin Sameer da ko abinci baya saukowa yaci in ya dawo office ya hau sama baya sake saukowa sai washegari, in yunwa ya dame shi sai ya ci biscuit da maltina ko coke.
Advertisement
Mahmoud ko sedai in abun ya dameshi ya tasa Mummy a gaba yayita mata kuka yana fad'in taje ta dawo mishi da Haseenah.
Ta rasa yanda zatayi da su itama tausayin su ke sanya ta zub da hawaye.
Bata ta6a sanin Haseenah ta zamo musu sani 6angare a rayuwar su ba seda ta bar gidan.
Ita kanta ba jin dad'in gidan take ba amma haka take daurewa.
Sameer Kam ma ba kulasu yake ba duk yayi duhu ya koma miskilin dole.
Can kuwa ana saura kwana d'aya Haseenah zata koma gida suka fita da yamma Dukansu suka je siyayyan kayan sawa.
Duk Haseen ne ya biya kud'in dan ya hanata biya, haka Umaimah da Baby da Aaman ma yace su d'auka abinda suke buk'ata.
Sossai sukayi siyayya da yake yanzu Haseenah batada wani kayan sawa.
Yawanci dogayen riguna ne sai atampopi da laces wanda suka mik'a wajan tailor sannan suka dawo gida.
Washe gari da daddare Abba ya taho da motar shi yazo d'aukan Haseenah.
Motar Haseenah wanda tun bayan abinda ya faru da Mummy ta sanya aka lullube ta Bama driver ya Kai car wash tun safe.
Dan haka Abba yana isowa aka loda mata kayayyakin ta a Boot sanann suka shiga Dukansu a mota uku suka d'au hanya.
Motar Abba ne sai abokin shi a ciki, d'aya motar Haseenah kuma Mummy ce ke driving sai Haseenah da Baby da Aaman, d'aya motar kuma ta Haseen ce, shi ne a ciki sai sister Mummy wato Aunty sadiya da Aunty zainab a ciki.
A hankali suke tafiya yayin da Haseenah ke faman sak'e sak'e a ranta, tunani take irin zaman da zasuyi da Mummy, Dan wannan karon da shirin ta take, dan bazata d'au wannan rainin hankalin ba.
Jin an tsaya ne ya sanya ta d'agowa da sauri, gani tayi an kutsa cikin gidan, lokaci d'aya taji rayuwar su ta baya ta dawo mata, ummanta kawai take gani a idon ta, bata san lokacin da hawaye ya fara zubo mata ba, haka ma Mummy Zuwaira duk jikinta yayi sanyi, Baby da Umaimah kuwa ganin kukan da Haseenah take suma sai kuka.
Advertisement
Kasa fitowa daga cikin motar sukayi, duk jikinsu nauyi ya musu, tsaye Abba yake da su Haseen suna jiran fitowar su, ganin zasu 6ata lokaci ya sanya Aunty zainab k'arasowa jiki a sanyaye ta knocking window, a hankali Mummy ta sauke glass d'un sanann tace " gamunan fitowa"
Duban su tayi tace" let's go"
Aaman ko yana manne jikin Haseenah ya tsira mata ido ganin tana ta kuka, shiko sai faman share mata hawayen yake yana ce mata "choli aunty na"
Murmushi kawai tayi sannan ta fito daga motar tana rik'e da Aaman.
Suma fitowa sukayi nan suka k'araso wajan su Abba.
Tunda Mummy taji horn na motoci ta ra6e jikin window ita da saratu amma Abba kawai suka gane da yake dare ne basu gane komai.
A tare suka shiga ciki Abba ya sanya key ya bud'e side d'in.
Shiga duka sukayi a tare har cikin palour.
Ba k'aramin kyau yayi ba ganin tsarin da akayi ma wajan.
Komai na palour pink nd purple ne,.
Zama dukan su sukayi ba tare da ance komai ba, dan ji suke kaman yau akayi mutuwar.
Da k'yar Abba ya iya share hawayen dake gangara mishi sannan ya fara musu nasiha.
Sunkai kusan hour suna tattaunawa daga bisani Abba ya fice.
Mummy ya gani tsaye jikin k'ofar d'akin shi sai girgiza take, kau da kai yayi da nufin shigewa, tsare shi tayi cikin masifa tace" ban gane abinda kake nufi ba a kwanakin nan, su waye naga an kawo su wajan nan eye?"
Ko kallon ta baiyi ba illa ma yana neman hanyar shigewa ne, tare hanya ta sake yi sanann tace" kana nufin aure ka k'ara?"
Ba tare da ya kalleta ba yace " eh, ko babu kyau ne?"
Kasa magana tayi nan tayi zaman dirshan.
Hakan ya bashi daman wucewa ya banko k'ofar ya rufe.
Kuka Mummy ta sanya tana shura k'afa.
Da sauri saratu ta taso ta tsuguna tana tanbayan dalili, kasa magana Mummy tayi, ganin tana neman tara musu jama'a ne ya sanya saratu dagewa ta kamo hanunta suka wuce side d'insu.
Hauka da surutu kam Mummy take da zage zage.
Babu wanda ma yasan tanayi ballantana ya kula ta.
Snacks d'in da sukayi a gidan Mummy Zuwaira Suka baje sunaci abunsu suna hira.
Ganin wajan 10 na dare yayi ya sanya Mummy mik'ewa ita da sauran zasu tafi.
Mik'a wa Haseenah key d'in motar Mummy tayi sannan ta dubi su Umaimah tace" kukuma sai yaushe zaku dawo?"
" Mummy kawai kije kinga yanzu hutun school ake, sai kin ganmu kawai"
Duban haseen Baby tayi sannan tace" uncle gobe in zaka taho plx Kabi gida ka taho mana da kayan mu harda na Aaman ma"
Amsa mata yayi sannan ya fice.
Suma bin bayan shi sukayi sannan sukayi sallama da Abba suka kama hanyar komawa gida.
Ayi hakuri da wanann plx....
For comments 08144932303
Advertisement
- In Serial90 Chapters
A Gentleman's Curse
Living a normal, content blue-collar life in the States, MC hadn't expected his situation to change for a long time. When his soul is stripped of his body, however, his plans were thrown out the window. Thrown into a new world with regrets and the memories of a life that is no longer his, he can either embrace this new environment of magic and monsters, striving to make a new life here using his old knowledge, or suffocate under his past. Hey! Author here. Chapters post every other week and are anywhere from 3.5-6.5k words apiece. This'll be the first story I've ever written but I have a plot in mind and a plan in place. Just let me know if there's anything you'd like to see or if something about the grammar is bugging you. Thank you for reading! Please keep in mind there will be some minor adjustments made to the earlier chapters as the book progresses. I'm building a story chapter by chapter, so I may/will need to go back and touch up some things. If you like the story, please consider supporting me on Patreon!
8 259 - In Serial141 Chapters
The Mad One
One day Humanity ruled the World. The next day they were gone. The system is put into play to help Humanity cope with their new, cruel reality. Some will walk their paths, continuously progressing. Others will end their paths, a dead-end. And a few, very few people will fall off their paths, finding nothing but cold water to drown themselves in. Updated on Modays, Wednesdays, Fridays and Sundays.
8 435 - In Serial98 Chapters
Silence the Hunger
Forcefully taken into a new world Alphonse is met with a new opportunity to become strong. A strange alien mothership, soldiers forcing them to learn how to kill. Forced to go on quests to different planets where survival is anything but guaranteed. This is Alphonse's quest to survive, eat, and evolve. A fast paced story telling the tales of Alphonse on his Glutenous journey as a soldier slave of the Great Migrators. Watch him devour monsters for their forms, reaping them of their delicious stat points. All while a terrifying plot simmers beneath his feet. Silence the Hunger is dark in nature, much like Alphonse's fighting style. Sensitive topics are brought up with a hint of tragedy, you've been warned. I am a new author, and this is my very first go at writing a story. Please be lenient with me! Release schedule - three chapters a week Monday-Wednesday-Friday https://discord.gg/xrbGGn6vtj
8 155 - In Serial6 Chapters
The Superb Lyre
With her fathers will reading happening in a few weeks, Valerie has to return home only to juggle finding a long since missing sister and keeping her locked up brother in check so that they can all get their part of the inheritence. All the while, having the mind-numbing nature of working in a call centre grating at her soul.
8 71 - In Serial57 Chapters
Killer Frost • Stiles Stilinski / Boyxboy
"People say that monsters don't have nightmares. Oh but sweetheart,How do you think Monsters are born?" Stiles X Killer Frost (Chris Snow)
8 141 - In Serial8 Chapters
betrayed op gojo deku
izuku midoriya who had just witness his mother die only to be knocked out and beaten by his friends to near death as he unlocks a new power powers of gojo satoru and another power while those who didnt betray him felt so much rage that they their quirks evolved but izuku decides to go to i-island to be with the person he loves melissa shield but she will share izuku with afew more girls too.And this story is a short story not a one shot but not over 10 chapters long but i hope you will enjoy :)
8 82

