《HASEENAH》PAGE 75&76
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS- 08144932303
# http://
Follow me on Aysherabbakar
*75~76*
Cikin Baccin tayi mafarkin Haseen, wai bashida lafiya mutane tsaye akan shi, banda sunan ta ba abinda yake kira, ita kuma ta na can gefe tana lek'en shi cikin kuka, ba wanda yake ganin ta sai shi kaɗai, miƙa mata hanu yakeyi tazo kusa da shi, amma bata son mutane su ganta, hawaye ne sharkaf a fuskanta tana kuka.
Mum Haseen ta gani durk'ushe a kan k'afarta tana furta " son karka tafi ka barni dan Allah , karka manta kai kadai muke da shi"
Tana maganan ne ta damk'e hanunta cikin nashi, k'ank'ame hanun nata shima yayi cikin ƙarfin hali yana son nuna mata Haseenah amma ya kasa d'aga hanun.
Ana haka kawai hanun Haseen ya silale ya fad'i alamar rai yayi halinsa.
Mum Haseen ne ta kurma ihu tana faɗin" wayyo my son karka mutu ka barni"
Haseenah da gumi gaba ɗaya ya jik'a ta ganin abinda ya faru ya sata farka wa a razane haɗe da kurma wata irin ihuuu *Haaaaseeen*
A firgice ta tashi tana waige waige gashin kanta duk ya wargaje, toshe bakinta tayi da duka tafin hanunta lokaci ɗaya kuka ya su6uce mata.
Ba tare da ta sani ba ta fara sambatu" wayyo Allah Haseen karka tafi ka bar....
Cak ta tsayar da maganar ta mik'e da sauri cike da mamaki, inba hauka tayi ba kaman ji tayi tana magana ko?
Abinda ta tanbaya kanta kenan, dan tabbatar da abinda take zargi ta sake cewa" Ummah na"
Ya subhanallah, she can't believed that, is she dreaming?
Duk da haka bata yarda ba, a hankali ta shiga toilet ta bud'e pampon jacuzzi, Nan ta Fara jin ƙarar ruwan, juyawa tayi ta kalli mirror bathroom din, wanke fuskanta tayi sanan ta sake kallon madubin, still she can't believe that, Dan Haka ta fara muna kayan ban d'akin one after d other tana fad'an sunan su.
Nan ma gani take duk k'arya ne, dan haka ta fito ta dauka gwangwanin coke ta buga a ƙasan tiles d'in, jin ya bada sauti ya sata daka wata uwar tsallen murna.
Advertisement
Zubewa tayi a ƙasa haɗe da yin sujuddus shukur, nan ta fashe da wata irin kuka.
She never think or thought a day like this will come, buh what a sudden coincidence, oh Allah Alhamdulillah.
Toilet ta shige ta yi alwala, ganin lokacin 3:30 na dare ya sata shimfid'a sallaya ta fara jero nafilfili tana godiya wa Allah.
Addu'oi kam ranan ta yi su kaman bazata dena ba, tana yi tana kuka, addu'a take wa Umman ta, tana rok'ar mata rahamar Ubangiji.
Nan taji kewar gida ya kama ta.
Seda aka kira sallar asuba sannan ta mik'e ta kawo raka'a biyu.
Nan ta koma ta kwanta, kasa bacci tayi dan yau ji take kamar duka damuwarta sun tafi.
Gani take ba wanda yau zai gwada mata murna.
Amma tayaya zata sanar wa Ammi?
Wata dabara ce ta fad'o mata dan haka ta saki wata murmushi.
Nan baccin dad'i yayi awon gaba da ita.
Wajen ƙarfe 7 na safe ta farka, miƙa tayi haɗe da salati sannan ta tashi.
Jikin mirror ta nufa ta dubi kanta a madubi, murmushi ta saki haɗe da faɗa wa kanta
"hi Haseenah"
Abun sai ya bata dariya ganin tana k'ok'arin zaucewa.
Toilet ta wuce tayo wanka cike da nishad'i, ta fito nan ta zauna ta shafa mai ya feshe jikinta da turare, dogon riga ta zura sannan ta daura mayafin shi, yan kunne manne ta sanya da zobe da wrist watch.
Ba k'aramin kyau tayi ba, dan haka ta kama hanyar fita ta nufa palour dan tasan yau Monday da wuri y'an gidan zasu fita.
Bata samu kowa a palour ba dan haka juyawa tayi ta nufa d'akin Ammi, a hankali ta kutsa kai ta shiga kaman yanda ta saba.
Ammi ta hango ita ma tana k'ok'arin fito wa.
Dan haka kawai ta sakar mata murmushi yanda suka saba gaisawa kenan.
Wannan karon Ammi yak'e kawai ta mata dan ita sam tafison ta mayar da Haseenah gida, in ba haka ba kuwa lokaci ɗaya gidanta zai wargaje.
A sanyaye Haseenah ta juya Ammi tabi bayan ta, dining suka nufa dukan su.
Suna zama su Mahmud ma suka iso, dan haka duka idon su a kanta yake.
Bayan sun zauna ne Sameer ya dubi Ammi yace" mrng mum"
"Mrng"
Ta amsa mishi a tak'aice, yasan dalilin hakan dan haka bai ce komai ba , nan Mahmud ma ya gaida ta, shima ba yabo ba fallasa ta amsa.
Advertisement
Nan kowa ya fara cin abincin shi, lokaci lokaci sai su kalli Haseenah dukan su.
Tana gamawa ta koma kan sofá ta zauna tana kallon TV.
A gurguje Sameer ya koma sama ya d'auko brief case d'inshi, d'ayan hanun sak'ale da ward coat dinshi.
Ganin ya kusa latti gashi yau Monday ba ƙaramin hold up zai samu a hanya ba, duban Ammi yayi yace" Ammi na tafi sena dawo"
"Allah kiyaye hanya" exclaims Ammi.
Mahmud dake faman cika yana batsewa Ammi ta dubeshi sannan ta dubi Haseenah, ganin hankalin Haseenah baya wajan su ya sanya ta fara cewa.
" Dukan ku na kula da take taken ku, to wallahi tun wuri kusan yanda dare ya muku, dan babu wanda zaiyi gigin kawomin wata maganar banza kan yarinyar da ba kusan inda ta fito ba, kanaji ko?"
Gaban Haseenah ne ya bada daaammm.
Tsoro ya cika ta jin abinda Ammi take faɗa, bata gwada alamar taji abinda suke faɗa ba tunda dama ba wanda yasan tana ji yanzu.
Nan Ammi ta cigaba da ja wa Mahmud kunne ta ƙare da cewa" bari Sameer ya dawo shima zan ja mai kunne, in Kuma Baku ji ba to duk zan d'au mataki a kanku"
Tunda ta fara maganar bai ce komai ba, dan shi baya jin akwai wanda ya isa ya hana shi son Haseenah ko auran ta, sedai duk abinda za'ayi ayi.
Duban shi tayi sannan tace" ba dakai nake magana ba?"
Cike da jin haushi ya dube ta sannan yace
" to dan Allah Ammi what did u want me to say? atleast am matured enough to choose d ryt nd perfect partner for my self, am not a child anymore, so nidai kiyi hak'uri I can't live without her, Dan Ina sonta".
Yana gama faɗin haka ya mik'e ya nufa hanyar d'akin shi.
Cike da mamaki da tashin hankali ne ya bayyana ƙarara a fuskar Ammi, kiran sunan shi ta fara yi akan ya saurareta ya dawo amma ko juyowa baiyi ba ya shige d'aki, ƙarar bugo k'ofar taji ya danna key.
Dafe kai Ammi tayi tana furta innalillahi wa inna ilaihir raji'un, na shiga uku Ni Fatima.
Wannan wace irin masifa ne?
Haseenah da lokaci ɗaya taji tsoro ya shige ta ganin abinda ya faru, mik'ewa tayi ta bar wajan da sauri dan kar Ammi ta gano halin da take ciki.
D'aki ta shige ta kulle k'ofa ta saki kuka.
Ta rasa kukan me take, na farko ba son Mahmud take ba ballan tana tace kukan zafin rabuwa dashi take, sannan na biyu kuma ba haushin Ammi ta ji ba tunda gaskiya ta faɗa, basusan ita wacece ba haka suka rungume ta suka tallafa ma rayuwarta.
Ita lokaci ɗaya taji tsabar tsanar Mahmud, inta tuna irin wulak'anci da cin fuskar da yayi mata a baya.
Sannan batajin son Sameer ko kaɗan cikin zuciyar ta, tana mishi kallon yayanta ne, dan haka duk bata da case da su.
Haseenah bata fito cin abincin rana ba, Ammi ma bata damu ta nemo ta ba, dan itama damuwar da ke faman tunkaro ta ya ishe ta.
Mahmud ma bai sauko ya ci ba, Sameer dama sai yamma zai dawo.
Dan haka palour babu kowa sai ƙarar AC dake tashi.
Bayan anyi sallar magrib ne suka fito.
Ammi ko kallon inda Mahmud yake bata yi ba, shima baice komai ba.
Dan haka zaman kurame akayi kowa na gamawa ya tafi abin shi.
Washegari Sameer bazai fita aiki ba dan haka basu tashi da wuri ba sai 10am.
Wanka yayi ya sanya Black jeans da riga red colour an rubuta handsome a gaban.
10:30 suka fito dan cin abinci.
Mahmud ne ya gaida Ammi ta yi banza da shi.
Hakan ya ba ma Sameer mamaki, shima ya gaida ta a dak'ile ta amsa.
To me hakan yake nufi?
Bayan sun gama cin abinci ne kowa ya koma ya zauna.
Sameer ne ya dubi Ammi kanshi a ƙasa ya fara cewa" Ammi Please i want us to talk"
Ba tare da ta kalle shi ba tace
" am all ears"
" Ammi Ni da ke kawai nake son muyi maganar kuma ga Mahmud zaune"
"Atleast shima he's part of d family so just say it"
Exclaims Ammi.
Jikin shi ya fara sanyi da irin amsar da Ammi ke bashi dan haka kaman zai fasa sai kuma ya tuna, to tunda Mahmud na wajan ai this is d ryt time da Yakamata ya faɗa, so that in ma akwai wani abu a ranshi ya cire.
Dan haka ya fara da cewa"......
First comments 08144932303
Advertisement
- In Serial19 Chapters
Interview With the Hattoris
Yuko Hiragi is an aspiring journalist. She goes about her internship with hopes of scoring a big scoop so that she can be set with a nice job after she graduates college. When she gets an opportunity to interview the corrupt and powerful Jensen Skagg, her dreams of fame become dashed when he is murdered before her eyes by a mysterious assassin. She is soon thrust into the dark world of murder and intrigue as she is hosted by the ancient and powerful Hattori family.
8 129 - In Serial238 Chapters
Stardust
Set in an alternative world where monsters and magic exist in our modern society and the entirety of its inhabitants has the ability to use said magic according to their unique ability. Stardust tells the tale of a group of friends who voluntarily calls themselves Team Stardust on a journey to win the annual school event, The Magic Duel. Our protagonist, Cyclone White is a seventeen years old boy in his final years of a magic high school but for some reason he still haven't obtained his own magic abilities like everyone else. He had it slow unlike his fellow classmates and friends but once he finally obtain an ability after an unexpected meeting, he finally allows himself to show what his introverted self is capable of. Join Cyclone White and his friends as he slowly builds his team to become one of the top young wizards in their school and achieve the elusive trophy of The Magic Duel.
8 73 - In Serial41 Chapters
Taken to Another World In My Bathrobes - Isekai
After being swallowed by a dragon Tristan Bell finds himself in Umbra, a land of swords and sorcery. He will need to figure out what's going on, gear up and learn some spells all without being killed by magical beasts, renegade magi and a dragon unleashed from a century long imprisonment. The answers he seeks and the power he needs are in Tempest academy, a school of magic and a dark secret that threatens the lives of Tristan, his friends and the whole of Umbra.
8 224 - In Serial30 Chapters
Still With You✔
Бүх зүйлийн бодит үнэн уйтгар гуниг харуусал дээр тогтоод байх шаардлагагүй шүү дээ, үгүй гэж үү?Ганц олдож байгаа амьдралаа гуниг гутралаар дүүргээд байх чинь утгагүй. Хайртай хүнтэйгээ учирч, аз жаргалаар бялхаад, ганц олдох нандин хурим дээрээ сэтгэл хөдлөлөө тэвчин зогсох, анхныхаа үрийг өлгийдөн аваад нулимсаа барилгүй зөнд нь урсгах, хүүхдээ том болж буйг өдөр өдрөөр харж өтөл болох хүртлээ аз жаргалтайгаар өнгөрүүлэх ёстой...Гол нь хэнтэй гэдэг нь л чухал.....•••Started: 2020.11.19•••Finished: 2020.12.29[Бичвэрт гарч буй бүхэн зохиомол, цэвэр төсөөлөл болохооо буруугаар ойлгохгүй байхыг анхаарна уу:) ]
8 177 - In Serial50 Chapters
FIFTEEN SHADES
***Mãture****COMPLETED#Book Three in the Fifteen SHADES SeriesOne night that they both wouldn't forget, one night that started it all, where it all began. Books in orderFIFTEEN SHADES DARKER FIFTEEN SHADES DONEFIFTEEN SHADES WITH THE DEVIL FIFTEEN SHADES OF COMPLICATED REVENGE ****"You're Lucifer" I gasp.My mouth drop open as his mouth closes over my breâšt. He nips on it lightly with his teeth and i feel fire dust in my vein pumping blood faster in my brain and my cheeks.My face is scarlet. His other hand knead my other breášt tugging on my errect nîpple until my whimper turn to loud throaty moans"That's right foxie" He breathes against my breast, sending goosebumps everywhere. His eyes will end me. "And you've been very very bad. Do you know what i do to sinners?"His voice is so dark like sex and it sends an electric bolt straight to my core.I swallow hard my breath hitching "What?" I whisper "I fuck them, hard" He growls right before he thruśt his fingers into my dripping cöre.
8 232 - In Serial23 Chapters
DarLentina One Shots (NarGina)
Them in different worlds.
8 118

