《HASEENAH》PAGE 75&76
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS- 08144932303
# http://
Follow me on Aysherabbakar
*75~76*
Cikin Baccin tayi mafarkin Haseen, wai bashida lafiya mutane tsaye akan shi, banda sunan ta ba abinda yake kira, ita kuma ta na can gefe tana lek'en shi cikin kuka, ba wanda yake ganin ta sai shi kaɗai, miƙa mata hanu yakeyi tazo kusa da shi, amma bata son mutane su ganta, hawaye ne sharkaf a fuskanta tana kuka.
Mum Haseen ta gani durk'ushe a kan k'afarta tana furta " son karka tafi ka barni dan Allah , karka manta kai kadai muke da shi"
Tana maganan ne ta damk'e hanunta cikin nashi, k'ank'ame hanun nata shima yayi cikin ƙarfin hali yana son nuna mata Haseenah amma ya kasa d'aga hanun.
Ana haka kawai hanun Haseen ya silale ya fad'i alamar rai yayi halinsa.
Mum Haseen ne ta kurma ihu tana faɗin" wayyo my son karka mutu ka barni"
Haseenah da gumi gaba ɗaya ya jik'a ta ganin abinda ya faru ya sata farka wa a razane haɗe da kurma wata irin ihuuu *Haaaaseeen*
A firgice ta tashi tana waige waige gashin kanta duk ya wargaje, toshe bakinta tayi da duka tafin hanunta lokaci ɗaya kuka ya su6uce mata.
Ba tare da ta sani ba ta fara sambatu" wayyo Allah Haseen karka tafi ka bar....
Cak ta tsayar da maganar ta mik'e da sauri cike da mamaki, inba hauka tayi ba kaman ji tayi tana magana ko?
Abinda ta tanbaya kanta kenan, dan tabbatar da abinda take zargi ta sake cewa" Ummah na"
Ya subhanallah, she can't believed that, is she dreaming?
Duk da haka bata yarda ba, a hankali ta shiga toilet ta bud'e pampon jacuzzi, Nan ta Fara jin ƙarar ruwan, juyawa tayi ta kalli mirror bathroom din, wanke fuskanta tayi sanan ta sake kallon madubin, still she can't believe that, Dan Haka ta fara muna kayan ban d'akin one after d other tana fad'an sunan su.
Nan ma gani take duk k'arya ne, dan haka ta fito ta dauka gwangwanin coke ta buga a ƙasan tiles d'in, jin ya bada sauti ya sata daka wata uwar tsallen murna.
Advertisement
Zubewa tayi a ƙasa haɗe da yin sujuddus shukur, nan ta fashe da wata irin kuka.
She never think or thought a day like this will come, buh what a sudden coincidence, oh Allah Alhamdulillah.
Toilet ta shige ta yi alwala, ganin lokacin 3:30 na dare ya sata shimfid'a sallaya ta fara jero nafilfili tana godiya wa Allah.
Addu'oi kam ranan ta yi su kaman bazata dena ba, tana yi tana kuka, addu'a take wa Umman ta, tana rok'ar mata rahamar Ubangiji.
Nan taji kewar gida ya kama ta.
Seda aka kira sallar asuba sannan ta mik'e ta kawo raka'a biyu.
Nan ta koma ta kwanta, kasa bacci tayi dan yau ji take kamar duka damuwarta sun tafi.
Gani take ba wanda yau zai gwada mata murna.
Amma tayaya zata sanar wa Ammi?
Wata dabara ce ta fad'o mata dan haka ta saki wata murmushi.
Nan baccin dad'i yayi awon gaba da ita.
Wajen ƙarfe 7 na safe ta farka, miƙa tayi haɗe da salati sannan ta tashi.
Jikin mirror ta nufa ta dubi kanta a madubi, murmushi ta saki haɗe da faɗa wa kanta
"hi Haseenah"
Abun sai ya bata dariya ganin tana k'ok'arin zaucewa.
Toilet ta wuce tayo wanka cike da nishad'i, ta fito nan ta zauna ta shafa mai ya feshe jikinta da turare, dogon riga ta zura sannan ta daura mayafin shi, yan kunne manne ta sanya da zobe da wrist watch.
Ba k'aramin kyau tayi ba, dan haka ta kama hanyar fita ta nufa palour dan tasan yau Monday da wuri y'an gidan zasu fita.
Bata samu kowa a palour ba dan haka juyawa tayi ta nufa d'akin Ammi, a hankali ta kutsa kai ta shiga kaman yanda ta saba.
Ammi ta hango ita ma tana k'ok'arin fito wa.
Dan haka kawai ta sakar mata murmushi yanda suka saba gaisawa kenan.
Wannan karon Ammi yak'e kawai ta mata dan ita sam tafison ta mayar da Haseenah gida, in ba haka ba kuwa lokaci ɗaya gidanta zai wargaje.
A sanyaye Haseenah ta juya Ammi tabi bayan ta, dining suka nufa dukan su.
Suna zama su Mahmud ma suka iso, dan haka duka idon su a kanta yake.
Bayan sun zauna ne Sameer ya dubi Ammi yace" mrng mum"
"Mrng"
Ta amsa mishi a tak'aice, yasan dalilin hakan dan haka bai ce komai ba , nan Mahmud ma ya gaida ta, shima ba yabo ba fallasa ta amsa.
Advertisement
Nan kowa ya fara cin abincin shi, lokaci lokaci sai su kalli Haseenah dukan su.
Tana gamawa ta koma kan sofá ta zauna tana kallon TV.
A gurguje Sameer ya koma sama ya d'auko brief case d'inshi, d'ayan hanun sak'ale da ward coat dinshi.
Ganin ya kusa latti gashi yau Monday ba ƙaramin hold up zai samu a hanya ba, duban Ammi yayi yace" Ammi na tafi sena dawo"
"Allah kiyaye hanya" exclaims Ammi.
Mahmud dake faman cika yana batsewa Ammi ta dubeshi sannan ta dubi Haseenah, ganin hankalin Haseenah baya wajan su ya sanya ta fara cewa.
" Dukan ku na kula da take taken ku, to wallahi tun wuri kusan yanda dare ya muku, dan babu wanda zaiyi gigin kawomin wata maganar banza kan yarinyar da ba kusan inda ta fito ba, kanaji ko?"
Gaban Haseenah ne ya bada daaammm.
Tsoro ya cika ta jin abinda Ammi take faɗa, bata gwada alamar taji abinda suke faɗa ba tunda dama ba wanda yasan tana ji yanzu.
Nan Ammi ta cigaba da ja wa Mahmud kunne ta ƙare da cewa" bari Sameer ya dawo shima zan ja mai kunne, in Kuma Baku ji ba to duk zan d'au mataki a kanku"
Tunda ta fara maganar bai ce komai ba, dan shi baya jin akwai wanda ya isa ya hana shi son Haseenah ko auran ta, sedai duk abinda za'ayi ayi.
Duban shi tayi sannan tace" ba dakai nake magana ba?"
Cike da jin haushi ya dube ta sannan yace
" to dan Allah Ammi what did u want me to say? atleast am matured enough to choose d ryt nd perfect partner for my self, am not a child anymore, so nidai kiyi hak'uri I can't live without her, Dan Ina sonta".
Yana gama faɗin haka ya mik'e ya nufa hanyar d'akin shi.
Cike da mamaki da tashin hankali ne ya bayyana ƙarara a fuskar Ammi, kiran sunan shi ta fara yi akan ya saurareta ya dawo amma ko juyowa baiyi ba ya shige d'aki, ƙarar bugo k'ofar taji ya danna key.
Dafe kai Ammi tayi tana furta innalillahi wa inna ilaihir raji'un, na shiga uku Ni Fatima.
Wannan wace irin masifa ne?
Haseenah da lokaci ɗaya taji tsoro ya shige ta ganin abinda ya faru, mik'ewa tayi ta bar wajan da sauri dan kar Ammi ta gano halin da take ciki.
D'aki ta shige ta kulle k'ofa ta saki kuka.
Ta rasa kukan me take, na farko ba son Mahmud take ba ballan tana tace kukan zafin rabuwa dashi take, sannan na biyu kuma ba haushin Ammi ta ji ba tunda gaskiya ta faɗa, basusan ita wacece ba haka suka rungume ta suka tallafa ma rayuwarta.
Ita lokaci ɗaya taji tsabar tsanar Mahmud, inta tuna irin wulak'anci da cin fuskar da yayi mata a baya.
Sannan batajin son Sameer ko kaɗan cikin zuciyar ta, tana mishi kallon yayanta ne, dan haka duk bata da case da su.
Haseenah bata fito cin abincin rana ba, Ammi ma bata damu ta nemo ta ba, dan itama damuwar da ke faman tunkaro ta ya ishe ta.
Mahmud ma bai sauko ya ci ba, Sameer dama sai yamma zai dawo.
Dan haka palour babu kowa sai ƙarar AC dake tashi.
Bayan anyi sallar magrib ne suka fito.
Ammi ko kallon inda Mahmud yake bata yi ba, shima baice komai ba.
Dan haka zaman kurame akayi kowa na gamawa ya tafi abin shi.
Washegari Sameer bazai fita aiki ba dan haka basu tashi da wuri ba sai 10am.
Wanka yayi ya sanya Black jeans da riga red colour an rubuta handsome a gaban.
10:30 suka fito dan cin abinci.
Mahmud ne ya gaida Ammi ta yi banza da shi.
Hakan ya ba ma Sameer mamaki, shima ya gaida ta a dak'ile ta amsa.
To me hakan yake nufi?
Bayan sun gama cin abinci ne kowa ya koma ya zauna.
Sameer ne ya dubi Ammi kanshi a ƙasa ya fara cewa" Ammi Please i want us to talk"
Ba tare da ta kalle shi ba tace
" am all ears"
" Ammi Ni da ke kawai nake son muyi maganar kuma ga Mahmud zaune"
"Atleast shima he's part of d family so just say it"
Exclaims Ammi.
Jikin shi ya fara sanyi da irin amsar da Ammi ke bashi dan haka kaman zai fasa sai kuma ya tuna, to tunda Mahmud na wajan ai this is d ryt time da Yakamata ya faɗa, so that in ma akwai wani abu a ranshi ya cire.
Dan haka ya fara da cewa"......
First comments 08144932303
Advertisement
- In Serial482 Chapters
Echoes of Rundan
His salvation comes in the form of a digital invitation... Mild-mannered accountant Dylan McIver needs something more than takeout, spreadsheets, and the occasional PUG. Everyone around him is getting married and popping out kids, and neither of those sound like the adventure Dylan wants out of life. His best friend, Nakala, has the answer. A beta invite to Monsoon Entertainment's latest MMO. But it isn't just an offer; it's a plea. Dylan will need to sacrifice five years of his real life to help her. The grind in the game is real, but Dylan is up for the challenge. There's monsters to kill, towns to build, mysteries to uncover, crafting to master, and fishing to enjoy. He'll sleep eventually. Echoes of Rundan is a Royal Road and Patreon exclusive fantasy LitRPG that starts with Landfall. Chapters are uploaded every other day!
8 464 - In Serial9 Chapters
Oddity
☾Don't tell me the sky is the limit when there are footprints on the moon.☽The Autobots and deceptions had been at war for what felt like an eternity, and the deceptions were tired of losing. A stroke of genius compels Megatron to send his most loyal to search the planet for worthy humans to aid them in crushing the Autobot forces once and for all.Enter a small group of online friends who could never have anticipated that their compelling personalities and strong bonds would set them up as prime targets for an alien warlord. Published on:WattpadQuotevRoyalRoad Transformers Prime and all like characters belong to Hasbro
8 96 - In Serial19 Chapters
Adaptive Learner
When the world is destroyed by nuclear explosions on January 17th, 2022, everybody died. With the earth gone many were given the choice of choosing a server or queueing for a new one. This is the story of one boy's life in a newly queued server. You can also find this story here: https://www.webnovel.com/book/adaptive-learner_20876139905728405 https://www.scribblehub.com/series/351973/adaptive-learner/
8 259 - In Serial56 Chapters
The Shade of the Sun
Ren always knew that Penny had a thing for mystical creatures and artifacts. In fact, she loved them, but all the dribs and drabs that Mrs Russell sells never works. Ren thought the onyx ring would turn out to be the same as all the rest, but it soon takes them to another world with the power of the Sun's Blessing. Now, trapped in another, apocalyptic-looking world with absolutely no sun in sight, how can the duo ever hope to get home? [participant in the Royal Road Writathon challenge]
8 148 - In Serial16 Chapters
The Fox Girl From The White Plains
Apparently, I transmigrated into the body of one of the fox kin. Found and rescued by a mysterious man, I can only hope for the best.
8 110 - In Serial11 Chapters
Souls
To be summoned to another world of swords and magic is the dream of anyone who wants more from life. With the chance of becoming a master of the sword, to grow more powerful than anyone could ever imagine. All this could be Leon one day. If he was the Hero. Instead, he along with his entire school was summoned into this world to fight the demon race whose king was recently died for unknown reasons, all to protect the people who Leon could really not care if they die. He mainly just wants to use magic and fly. But why has the Demon King died? How were these people able to summon people from across dimensions? And how could such a plain-looking boy like Leon ever hope to survive in a world where everyone, including the demons, don't really like him. They don't hate him, but they would rather not have anything to do with him. Disclaimer: My grammar is crap, and you have the right to tell me just how much I suck at writing. Also if your feeling like this series is very much like Arifureta, then I'm sorry. Because the beginning of this story will sound very much like that series.
8 219

