《HASEENAH》PAGE 49&50
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
Da Allah ina me bada hak'urin rashin jina da akayi na wasu kwanaki, hakan ya faru ne sakamakon wasu uzurori da nakeyi da kuma rashin wuta,wanda ke kirana da kuma wa'yanda suke mun magana privately Dan jin dalilin rashin ganin post Dina na gode sossai da kulawarku da kuma soyayyarku gareni da kuma littafi na, i hope my excuses will b considered.
*Team Haseenah*
Haseenah na Nan tana gaisuwa ga masoyan ta, kuma ta gode da tausayawar ku gareta, tace ku kwantar da hankalin ku Dr Sameer is by her side.
Iya comments d'inku iya d'adin page d'in gaba.
Thnx all.
*49~50*
Haseen bayan sun gaisa da iro me gadi ya dubeshi yace" Baba nazo maka da wata magana ne me girma, da fatan zaka bani had'in Kai?"
Shuru Baba yayi na wasu seconds kaman me tunani sannan yace" ina jinka yaro"
Gyara zama Haseen yayi sanann ya fara cewa" ba wani abu bane ya kawoni baba, Kan mutuwar Umma ce da kuma Haseenah, wanda kowa yake zargin mutuwar akan kunna wutar akayi, ko Kanada wata 'yar masaniya kan faruwar hakan?"
Malam iro shuru yayi, yayin da k'irjin shi yake dukan uku uku, saboda tsananin tsoron dake zuciyar shi, dukda ba wani abu ya sani ba amma yasan halin matar gidan kamar yunwar cikin shi, abinda ya dad'a firgitashi kenan dan yasan ko wucewa ta zo yi tagan su tare da Haseen to Allah ne kawai ze k'wace shi daga cin mutunci.
Ganin ya tafi duniyar tunani yasa Haseen ta6a shi yace" Baba lafiya kuwa?"
A firgice ya d'ago yace" ba komai Haseen, maganar gaskiya bansan komai akai ba nima lokacin ina nan waje naga Alhaji ya fito yana kwalalar wuta"
Haseen ya kula a birkice Baba yake dan haka mik'ewa kawai yayi ya sa hannu a aljihu ya ciro dubu biyar ya bawa Baba, hannu na rawa ya k'ar6a ya hau washe baki yana an gode.
Hakan ya tabbatar wa da Haseen cewa wannan baban mayen kud'i ne, ta haka kawai ze sa ya ja hankalin shi har ya samu abinda yake so.
Bai sake cewa komai ba ya nufa wajan motar shi ya shiga da niyar barin wajan.
Advertisement
Reverse ya fara yi da nufin juyawa nan ya hango wata mota CRV tazo tayi parking, wani bak'in saurayi ne a ciki bakin shi ma bak'ikk'irin, Bai gama k'arewa na cikin motar kallo ba yaga Saratu ta fito cikin gida.
Wajan motar ya ga ta nufa, sanye take cikin wasu dogayen riga armless, ta d'aura kimono a Kai, kanta yaci uwar attachment, fuskan ta Babu masaka tsinke saboda kwalliya, ga uban glass tafkeke data maka wanda ya kusan rufe mata hanci, k'afar ta kuwa high heel ne kalan kayan sai hanunta d'aya rik'e da jaka d'ayar kuma wayar ta ce tana wasa dashi.
Gayen kuwa yana ganin ta ya hau washe baki itama tana mayar mishi, gidan gaba ya bud'e mata ta shiga sannan ya rufe.
Duban shi tayi suka fuskanci juna sannan suka sake sakewa wa juna murmushi ta manna mishi kiss a kumatu.
Zaro Ido Haseen yayi ya k'ame a wajan saboda tsananin kad'uwa, yaushe Saratu ta zama haka?
Kafin ya samu amsar tambayar shi buzzing d'in motar ne ya dawo dashi daga tunanin da ya tafi, k'urar motar kawai ya gani dan bai ma san ta inda suka yi ba.
Jiki a sanyaye ya bar wajan shima ya nufa hanyar gida.
*Abuja*
Bayan kwana biyu da yin aiki wa Haseenah Ammi ta ce wa Sameer a sallame su kawai su koma gida su fara shirin tafiya turkey, tunda ance nan da sati d'aya zasu tafi.
Ba musu Sameer ya k'ar6a musu sallama suka tattara kaya suka koma gida.
Da daddare ne kowa na zaune a palour, yayin da Mahmud ke zaune chan gefe yana buga game.
Haseenah kuwa duk a takure take ganin irin hararar da Mahmud ke zabga mata.
Hakan yasa jikinta yin sanyi ta sunkuyar da kanta k'asa tana hawaye.
Tausayin kanta kawai take dan bata san inda take ba balle tayi tunanin inda zata ga wanda ta sani.
Sameer ne ya sauko daga kan steps, duban shi Ammi tayi sannan tace" son dama Kai nake jira tuntuni akwai maganar da nakeso muyi dakai"
Zama yayi gefen ta sannan ya dube ta yace" Ammi am here"
Nan ta Fara cewa" magana kan rashin jin yarinyar nan nake so muyi, nace why not mu sami malam Kabir yana mata rubutu ko Allah zesa a dace, tunda in Allah ya wuce gaba sukan dawo da jinsu"
Kafin yayi magana Mahmud yayi karap yace" Ammi karku wahalar da kanku da kud'in ku, kuka sani ko dama tuntuni kurma ce?"
Advertisement
Tsawa Sameer ya daka mishi cikin 6acin rai yace" tashi ka fice a nan"
Mik'ewa yayi yana k'ananan surutu ya haye sama ranshi a 6ace.
Tsuka ya ja sannan yace" Ammi nima dama inaso in Miki maganar sai kika rigani, yanzu da asuba in mun had'u a masallaci zan tsayar dashi in mishi bayani sai muji yanda abun ze kasance"
Nan suka cigaba da maganar yanda tafiyar zata kasan ce.
Tare suka ci abinci sannan kowa ya kama gaban shi.
Dama Haseenah wani d'aki dake jere dana Ammi aka gyara mata.
Seda ta gama cin kukan ta sannan tayi nafila raka'a biyu sannan ta kwanta.
Bayan anyi asuba ne Sameer ya tsayar da malam Kabir ya mishi bayani, ya gamsu da bayanin shi sannan yace yau ze Fara mata rubutu zuwa k'arfe goma zai shigo mata dashi gida.
Nan sukayi sallama ya koma ciki.
Ammi bayan ta idar da sallah ta fito da niyar tashin Haseenah, nan ta hangota zaune kan sallaya , murmushi tayi ta juya ta koma.
Nan Haseenah na idar wa ta koma bacci.
K'arfe bakwai da rabi ta tashi a firgice, sakamakon mafarkin Umman ta da tayi, kuka ta saka tana 6ari, ta rasa da wani bakin zata yi bayani, waye ze Gane halin da take ciki? Wa ze mayar da ita cikin dangin ta? Ina zata ga Haseen d'in ta? Ina zata ga Mummy Zuwaira da su Umaimah da Baby, ga Aaman d'inta ma?"
Wanann abubuwan suke sata kuka.
Mik'ewa kawai tayi ta shige toilet, wanka tayi ta fito sanann ta zura dogon riga cikin kayan da Sameer ya siya mata ta fito, dan ko mai bata shafa ba balle taje garin kallon madubi dan ta dena kalla.
Fitowa tayi ta lek'a d'akin Ammi amma bata nan, palour ta fito nan ma ba kowa, kitchen ta lek'a Nan ta hango Ammi tana k'ok'arin had'a kayan breakfast.
Shiga tayi sannan ta tsaya bayan Ammi.
Knocking k'ofar tayi, da sauri Ammi ta juyo, nan suka sake wa juna murmushi kawai.
Nuna mata kujera Ammi tayi, girgiza kai tayi sannan ta nufa wajan ta d'au wuk'a ta fara fere dankalin da Ammi ta d'ebo.
Tare suka gama komai, nan taje da kanta ta jera su kan dinning ta dawo tayi wanke wanke ta goge wajan.
Shirin da tayi kan table ya burge Ammi, dan haka ta tsaya kawai tana kallon ta.
Yanda Ammi taga Haseenah ta iya sarrafa ko wani na'urar girki da tsarin shirya table hakan ya tabbatar wa Ammi ba daga gidan talaka ta fito ba, to ina iyayen ta suke?
Sallamar Malam Kabir ne ya katse wa Ammi da tunanin ta.
Nan ta bashi umarnin shigowa, hanun shi d'auke da robar swan k'arama, rubutu ne aciki.
Bayan sun gaisa ne yayi wa Ammi bayanin yanda za tayi amfani dashi.
Nan Ammi tace kaga dama ba abinda ta ci sai a fara amfani dashi yanzu.
Nan sukayi sallama ya fice.
Haseenah dake zaune gefe suka haɗa ido da Ammi, da hannu Ammi ta kira ta nan ta taso ta zo.
Cup Ammi ta d'auka ta zuba mata rubutun sannan ta sake tofa addu'a ta mik'a mata, Bismillah tayi itama dukda batasan na meye ba ta shanye.
Kar6an cup d'in Ammi tayi ta ajiye sannan ta jawo Haseenah ta sunkuyar da ita had'e da kwantar da kanta kan cinyar Ammi, kad'an ta zuba a murfin goran sannan ta d'an zuba kad'an cikin kunnen Haseenah, seda ta tabbatar ya shiga sannan ta juya ta zuba mata a d'ayan.
Murna ne fal zuciyar Haseenah dan ta gane ko na menene.
Dama kullum setayi addu'a Allah dawo mata da kunnen ta.
Lokacin ƙarfe goma harta gota.
Da yake weekend ne suna ta bacci.
A tare Sameer da Mahmud suka sauko k'asa.
Gaida Ammi sukayi sannan Sameer ya dubi Haseenah ya sake mata murmushi, sunkuyar da kanta kawai tayi.
Idon Mahmud ne ya kai kan table, zaro ido yayi haɗe da furta" wow, Nice deco"
Dariya Ammi tayi sannan tace" k'anwar ka ce tayi"
6ata rai yayi ganin ance wannan mummunar ce k'anwar shi, har zeyi magana yaga kallon da Sameer ke mishi hakan ya sashi yin shuru.
Nan suka hau table d'in suka fara cin abinci.
Bayan sun gama ne Ammi take sanar dashi ankawo rubutun harta fara sha.
Dad'i sossai yaji sannan yace Allah ya sa a dace.
Mik'ewa Ammi tayi ta koma d'aki yayin da Mahmud ya nufa wajan computer ya fara game.
Haseenah kuwa zama tayi a takure waje d'aya.
Hakan ya sashi bud'e side drawer ya d'auko paper da biro ya nufa inda take ya zauna gefen ta sannan ya d'au biron yayi rubutu ya mik'a mata.
For comments only 08144932303
Advertisement
- In Serial22 Chapters
Rose of Thorns and Blood
I do not own Naruto, the original author is Masashi Kishimoto. An SI/OC reincarnated as a female naruto in the naruto_verse "My name was Sarah, I was a human experiment during the second world war I was barely 5 years old, back then a group of russian scientist discovered a withered fruit that fell on earth together with a meteorite, they didnt know where it came from, butit didnt matter much in the end, what it mattered was that the fruit had incredible amount of energy, they made me eat it, with eating it came untolds amount of power, power that made me immortal, I developed a second persona, while I have warm and kind, personality, the second is cold, ruthless, efficient and I can even switch between them in a blink." a woman in what looked like she was barely twenty in age, with white hair royal purple eyes, and with a well-endowed body said. "well you are dead now so I guess your immortality was flawed, even if you had a body that far surpassed the common human and did not catch any disease you will be hard pressed to survive a nuclear warhead huh, hmm I think you will fit in the world of naruto pretty well, you already consumed the Phoenix aspect chakra fruit even though it was stripped of most of its power during the dimensional travel hahaha" an androgynous voice said. the man before my eyes was pretty effeminate with shoulder length blonde hair and green eyes he is like that bishounen you see in anime and manga, ehehe what can i say I never liked those shows and movies from the west and I had to get a hobby, what it's not like I am embarrassed by being an immortal otaku, well I am dead now, damn those North Koreans. "wait did you say Naruto? is this reincarnation?" Mary Sue maybe There will be lemons, but not so much, I am just a horny bastard.
8 369 - In Serial13 Chapters
Questing
A LITRPG novel that has the protagonist Anon making his way through a new virtual game world, There are no gold farmers, no alts and no overpriced economy at least not yet. Anon is not in a hurry to level but is content to enjoy the game and explore the new world at his own pace. But like all new games there are bugs and problems.
8 141 - In Serial29 Chapters
True Assassin of Round Table
[ Google Translete Warning !!! Don't read if you don't like Horrible Grammar ] In 21st century, world entered a new stage of VR games…and “YGGDRASIL” is considered top of all MMORPG…but, After announcing that all its servers will be off, the internet game ‘Yggdrasil’ shut down…or so was supposed to happen, but for some reason, the player character did not log out some time after the server was closed. NPCs start to become sentient. A normal youth who loves gaming in the real world seemed to have been transported into an alternate world along with his queen, becoming his game character, Nash George Faust. The True Assassin has come to the New World. [ Daily Update ]
8 93 - In Serial7 Chapters
This World Really Knows How To Hit A Nerve
A 26 year old entrepreneur had sold game he developed, a VR MMORPG game to world's largest console company, thus making him a millionaire. He is using that money to live his life in luxury as well as develop yet another game. What happens when he is thrown into an unknown fantasy world with his console?
8 169 - In Serial34 Chapters
Dungeon Accident
On his way home after buying a pack of cigarettes, Dude suddenly finds himself in the lowest floor of a labyrinth! After conquering the legendary labyrinth in accident, he wanders around as he asks himself what to do next. Can he find his way back home? Or will he choose to live in this game-like fantasy world filled of adventurer?
8 100 - In Serial25 Chapters
A Mindful Relationship [Jensoo]
A world where you can talk to your soulmate through your thoughts alone. A mystery of who your soulmate would be begins now in the life of Kim Jennie. Who would it be? ...Inspired by Soulmate Accident converted by @blinkbell
8 140

