《HASEENAH》PAGE 43&44
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
*43~44*
" Ammi Dan Allah ki Dena turani wajan yarinyar nan in har ba so kike Nima a kwantar da Ni ba, wallahi bazan iya ba"
Ya 'karasa maganar haɗe da riƙe k'afar Ammi.
Cike da mamaki ta dubeshi tace" Baby meye haka? Ba kyau abinda kake yi fa, itama fa da mutum ce 'yar uwarka tsautsayi ne ya faɗa mata,kuma kaima bakafi k'arfin haka ba"
Share hawayen ya fara yi sannan yace" Ammi kiyi hak'uri zan je amma ba yanzu ba"
Duk abinda suke Sameer na kallon su saman stairs, shi mamakin Mahmud yake ganin yanda lokaci ɗaya yake fita hayyacin shi.
Dole Ammi ta yi shiru ta k'yale shi, dan tasan in ta matsa mishi zai iya daina fitowa palour ta ma.
Mummy kuwa rad'ad'in da bakin ta yake mata shi yafi d'aga mata hankali, kallon fuskanta tayi a mirror, kau da kai tayi da sauri ganin yanda kamannin ta suka koma, musamman bakin ta sai kace ja6a.
Fashewa da kuka tayi tana faɗin" Allah ya isa mun wallahi, wanda bazata gama da duniya lafiya ba"
Ana haka kuwa k'awayen ta wanda suka saba zuwa mata yawo ɗaya daga cikin su ta kira ta a waya, nan Mummy ta shaida musu itakam batanan tayi tafiya, dan bazata iya bari suga wannan abun kunyar ba.
2 weeks later
Jikin Haseenah ya gama bushewa ya d'aye tas ba komai, sai dai tabo da sauran wajan da bai warke ba, dan yanzu tana iya zama taci abinci da kanta.
Amma ba umm ba uhm, saidai tayi ta binsu da kallo, wani lokacin kuma sai kuka, gashi anyi mata tanbayar duniyar nan Bata amsawa, abunda basu sani ba ma batajin abunda suke faɗa, ita dai kawai tana ganin bakin su na motsi.
Tana son yin magana amma babu hali, ganin ta a wajan da bata sani ba duk shi yafi d'aga mata hankali, gashi duk cikin wanda suke zuwa babu wanda ta sani.
Saidai tafi ganin Sameer da Mummy sai nurses d'inda ke kula da ita sai Dr Abeed.
Advertisement
Tana son tanbayar ina Umman ta? Dasu Aaman da Haseen amma ba hali.
Iya abinda take iya tunawa tasan wajan su ya kama da wuta.
Sannan ko yaushe inta kwanta bacci salatin Umman ta ke yawo cikin kanta.
To ina Umman take? Meyasa suka barta anan? Kodai sun gujeta ne ganin jarabawar data fad'a mata?
Wata zuciyar ta bata amsa da ko da duniya zasu gujeki Umman ki bazata ta6a barin ki ba.
To ina suke?
Ba ta da wannan amsar, shiyasa takanyi kuka sossai inta tuna da haka.
Sai dai Sameer yayi ta bata hak'uri da Mummy, Amma Bata fahimtar abinda suke cewa.
Ganin ta samu sauk'i ne aka fara shirye shiryen Mata theatre, sun tsayar da rana satin da za.a shiga ran Monday kenan.
Addu'a kawai suke Allah ya basu Sa'a dan basu da wani ishesshen kayan aiki.
Dr Abeed ke ba Sameer k'arfin gwiwa, amma shi duk ya karaya.
Yau da sassafe ya shigo asibitin Mahmud na binshi a baya d'auke da basket d'in abinci.
Kana kallon Mahmud zaka ga yanda yayi kicin kicin da fuska, dan ba son ranshi ya zo ba, dan rabon da ya ganta tun ranar da suka d'auko ta, yanzu ma dan yana shakkar Sameer ne Amma wallahi da bazai zo ba.
Kai tsaye d'akin da Haseenah take suka nufa.
Suna isowa bakin k'ofar Mahmud ya ja ya tsaya, duban Sameer yayi yace" bro should I wait for u here?"
Harara kawai ya watsa mishi ya shige ciki, nan Mahmud ya bishi da sand'a.
Lokacin ko bacci ma take bata tashi ba, dan haka Sameer ya hau kujerar da ke gefen gadon ya zauna.
Mahmud kuwa jikin bangon d'akin ya mak'ale ko k'wak'k'waran motsi ya kasa.
Sameer zuba mata ido kawai yayi yana kallon yanda take sauke numfashi a hankali, wani lokacin kuma ta saki ajiyar zuciya kamar wanda taci kuka ta gaji.
Zuba mata idon da yayi zuciyar shi ke raya mishi cewa, duk yanda akayi yarinyar nan kyakkyawar gaske ce.
Dan yanayin siririn hancin ta da k'aramin bakin ta ne kawai ya sashi ganin haka, amma ji yanda wuta ya mayar da ita.
Girgiza kai kawai yayi cikin ranshi yace" poor you"
Ganin Bata motsi ya sa Mahmud lek'a ta, gani yayi tana bacci nan wata ajiyar zuciya ta k'wace mishi, dan yasan da idon ta biyu Allah kad'ai yasan dramar da za.ayi cikin asibitin nan.
Advertisement
Dan ko kashe shi Sameer zeyi wallahi bazai tsaya ba.
Tunda ya fara lek'en ta sameer ya ke kallon shi.
Dariyar mugun ta Sameer yayi sannan ya mik'e ya dubi Mahmud yace" Ni zanje duba patient d'ina, ka zauna anan ka jirani kafin in dawo,in ta tashi kuma ka bata abinci sannan ka kira Ni"
Zaro ido Mahmud yayi dan wannan maganan ta firgita shi, kallon yayan nashi yayi yace" yaya zan raka ka kaga sai nima in samu ladar ziyara"
"No need, Nan ma aikin ladan zakayi ai"
Jikin Mahmud ne ya hau rawa dan yasan ko mutuwa zaiyi bazai yarda ya bishi ba.
Ganin Mahmud ya tafi duniyar tunani yasa Sameer ficewa ya barshi nan tsaye.
Yana fita shima Mahmud ya fice ya zauna kujerar bakin k'ofar d'akin inda security ke zama.
Nan security ya fara cewa" ranka ya dad'e ka zauna ciki mana, in oga ya ganka bakin k'ofa bazaiji dad'i na bar k'anin shi a waje ba"
Cike da haushi Mahmud yace" to jani ka shiga dani mana, ina ruwanka dani ko kai ka bani ajiyar eye?"
"Tuba nake ranka ya dad'e"
Girgiza kai Mahmud yayi yace" to kayi damuwar ka, in kuma kujerar ka zan baka gashi"
Ya k'arasa maganar haɗe da mik'e wa.
Da sauri yace" yi hak'uri zauna"
K'wafa yayi ya zauna Yana mazurai.
Can Kuma sai ya mik'e ya lek'a ta ta window har lokacin bacci take.
Murna ne ya kama shi ganin har yanzu bata tashi ba.
Lek'awar da zaiyi na uku ya hango ta zaune kan gadon tana ta kalle kalle.
Gaban shine ya fara dukan uku uku, da sauri ya ciro wayar ya kira Sameer Amma abun haushi bai d'aga ba.
Tsoro ne ya dad'a kama shi gashi yace mishi ya bata abinci.
A hankali cikin sand'a ya shiga kan shi a sunkuye, da baya baya ya k'arasa ya d'au plate ya zuba mata chips nd egg with sauce, ko kallon ya baiyi ba ya mik'a mata.
Garin kar6a hanunta ya ta6a nashi, wani tsalle ya daka yayi gefe haɗe da ihu yana faɗin" wai mena miki kikeson ganin baya nane eye?"
Ya fad'a kaman zai fashe da kuka.
Ganin Sameer yayi tsaye gaban shi ya zuba mishi ido, da gudu yayi bayan Sameer yace" yaya dan Allah ka tambaye ta mena mata?"
Ko kula shi baiyi ba ya ja kujera ya zauna gefen gadon ta.
Zuba mishi ido kawai tayi tana kallon shi" to wannan d''in waye?"
Ba tada bakin tanbaya sannan bata da wanda zai bata amsa hakan ya sata yin shuru ta ci abincin kad'an sannan ta ajiye.
Nurses ne suka shigo dan gyara ta, hakan ya sa Sameer mik'e wa ya fita.
Mahmud ma yabi bayan shi yana ta faman k'ananan surutu.
*MONDAY*
misalin k'arfe bakwai na safe nurses suka shirya Haseenah cikin kayan da ake saka wa patients in za.a shiga dasu theatre, abinci suka bata sanann suka fice.
Sameer ne ya shigo ya dube ta duk hankalin ta a tashe, zama yayi ya dube ta sanann yace" ban sani ba ko kina jina ko baki ji, amma inaso kisa a ranki kuma kiyi addu'a Allah yasa ayi nasara"
Taga bakin shi na motsi amma bata jin abinda yake faɗa, amma ganin yanayin fuskan shi tasan he's saying something serious, hakan ya sata sakar mishi murmushi kawai.
Shima mayar mata yayi.
Dai dai lokacin Dr Abeed ya shigo da wasu nurses biyu, ɗaya daga cikin nurses d'inne ta Mata allurar Anesthesia sanann suka kwantar da ita.
Ganin dishi dishi ta fara yi wa mutane, can kuma taji duk jikinta yayi nauyi, within 5 mins bacci mai nauyi ya d'auke ta.
D'aurata sukayi kan gadon suka tura ta zuwa theatre suka fita da ita.
Likitoci biyar ke kanta, Sameer kuwa sai kai kawo yake a k'ofar theatre d'in, tun 7:30 aka fara mata har 10am basu fito ba.
11am sharp aka fito da ida fuskanta gaba d'aya an nad'e da bandage, ko motsi batayi kamar gawa haka aka turota.
Cikin A&E aka wuce da ita sai dai an ware mata wata d'aki ita kadai ke ciki.
Robar abinci aka zura mata a hanci aka nad'e da bandage.
Babu abunda kake hangowa a fuskanta dan gaba ɗaya aka nad'e ta.
Kana kallon fuskan Sameer kasan Yana cike da damuwa.
Wayarshi ne ta fara ruri yana dubawa yaga Ammi ke kira, picking yayi ya kara a kunne shi, ji nayi yace....
Please share, vote nd drop ur comments
Advertisement
- In Serial355 Chapters
Falling with Folded Wings
Morgan was a technician upon the Arkship, Pilgrim-9, bound for the Tau Ceti solar system. He wasn't ready for what would happen when the ship arrived. He wasn't prepared for a seemingly omniscient "System" to take control of his life and thrust him into some sort of proving ground. He just wanted to survive, figure things out, and get back to the rest of the colonists, wherever they may be. What happens when a few thousand humans are thrust into a world with magical Energy and hostile entities with unimaginable abilities? How will Morgan and his friends cope with the trials and tribulations? Will they grow in power, solving the mysteries of their new world and beyond, or will they succumb to the many forces aiming to impose their will upon the newcomers? This LitRPG serial will follow the lives of Morgan, Bronwyn, Olivia, and others as they work to survive, explore and grow in a fantastical world. 5 chapters per week release schedule: Mon - Fri Cover art by: Carlos Monteiro
8 767 - In Serial55 Chapters
Echoes of Infinity
The gods tore the world apart. Now magic is carefully controlled. As a recently graduated Mage from the Citadel, Marek upsets many when he decides to go on the frowned-upon World Tour. Intent on creating a mercenary company, Marek discovers an incredibly powerful object that will change the world. Once the Captain of the Citadel's Guard, Wyatt is now a mercenary and Marek's second in command, a position he knows will eventually force him to make a difficult and life-changing decision. After escaping her family’s efforts to marry her off, Ako is swept up in an adventure of a lifetime. Forced to evolve, Ako discovers that becoming a warrior is not without cost. Malevolent is the first book in Echoes of Infinity, an epic fantasy saga full of magic, battles, and twists and turns that will stay with you long after its shocking conclusion. Malevolent is now complete and will be available soon on Amazon as both an e-book and physical book. Book 2, Virulent, is currently being edited. I'm not sure where or when it'll release, but whenever I figure something out I will let everyone know. Thanks for reading. - Tristan Kerry.
8 169 - In Serial7 Chapters
Amethyst Phoenix
A sweet nectar drips before me. All other sources of sustenance have dried up. I’m afraid to drink it because I’ve seen the consequences of even a drop too much. It can be a poison, but we are nothing without it. I have been nothing without it. A husk. But once I drink this sap from the forbidden fruit, it cannot be undone, regardless of whether I take too much. I choose to take this leap through the void. And so I raise this ancient cup. I will not die a husk. A man without ambition is reborn in the body of Aegis Hyades Rastine to a world of fairy tales, only to find that it's as screwed up as any other. War, rape, pillaging, torture, starvation, slavery, genocide... You know, the good old stuff plaguing (Did I mention there were plagues too?) earth. How will he survive? Can he even? Note: This is the first story I've ever written, so I'd appreciate some cut throat critiques on my writing.
8 205 - In Serial26 Chapters
Whispers of Time 3
"Я не думал, что это может разрушить тебя" - Луи.Третья часть замечательного фанфика "Whispers of Time". Наслаждайтесь)
8 83 - In Serial16 Chapters
Broken (Peeta Mellark Fanfiction)
Peeta Mellark has survived the Hunger Games, he escaped the Quarter Quell, then he was rescued from the torturous hands of the Capitol. His memory has been tampered with, so everything he sees could be either real or fake. Instead of a smooth recovery, he is thrown right into war. What would become of him in the end? Broken. (Taking place a little over halfway through the Mockingjay book and after the movie Mockingjay Part 1) This is a somewhat sequel to the other story I wrote called Hijacked, but I think you could read this without reading the other one. This story and these characters are owned by Suzanne Collins, not me (obvi)
8 108 - In Serial14 Chapters
Cuffed For Good
Niah is just a regular girl who wants to show the world what's hers. She wants to stay with the one she loves the most. Will that last?
8 158

