《HASEENAH》PAGE 41&42
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
Godiya ga duk wani masoyin wannan littafi, na gode sossai da kulawarku da kuma karfin gwiwar da kuke bani koda yaushe, *Rumanah(Auta) kin kasance ɗaya daga cikin masoyana wanda ke mun magana ta pc, na gode da soyayyarki gareni da kuma addu'oinki, nima ina sonki sossai, ban manta da kuba*
Mom of 12
Raleeyerh
Hapcy
Ummu nawwar
umcee
Nanush
hauwee
Da duk sauran wanda ban ambata ba kuna raina, Allah bar zumunci da k'auna.
*41~42*
A firgice ya farka yana faɗin" gawa ta tashi, jama'a fatalwa"
Dariya da haushi ne suka cika Sameer, dubanshi yayi yace" Allah Mahmud in baka nutsu ba ranka zai 6aci"
Shiko sai zare ido yake yi a tsorace, juyawa yayi ya kalli back seat ya ga wayam, marairaice wa yayi kaman zeyi kuka yace" yaya na faɗa maka fatalwa ce baka yarda ba, gashi yanzu ta 6ace"
Nuna mishi k'ofa yayi yace" get out "
Sum sum ya fice zuciyar shi na bugawa.
Suna shiga gida sameer ya hango Mahmud zaune gefen Ammi kaman zai d'ale cinyarta, duk yayi kalan tausayi yace" Ammi wallahi da gaske nake miki"
Hararar da sameer ya zabga mishi ne ya sashi yin shuru.
Bayani ya shiga yi wa ammi, tunda ya fara magana ta nutsu tana jin shi har ya gama.
Duban shi tayi tace" son yanzu wani mataki ka ɗauka?"
"Tana asibiti na barta wajan Dr Abeed, yanzu firstly sai an Fara treating k'onan da tayi, wanda yace indai za.ayi amfani da most effective requirements bazata wuce 2weeks ba zata warke, secondly Kuma shine theatre da za.a mata a fuskanta in order to gain her normal look"
Gyad'a Kai Ammi tayi sannan tace "hakan ma yayi, da safe zan bika muje in duba ta"
Nan suka mik'e kowa da abinda yake sak'awa a ranshi.
Asibiti kuwa Haseenah oxygen aka saka mata, aka saka mata robar abinci ta hanci.
Ba tare da 6ata lokaci ba Dr Abeed ya sa nurses suka cire mata rigar jikinta aka saka mata na asibiti, bayan sun shafe mata jikin da wani magani mai ruwa.
Aaman kuwa kwana biyu yayi aka dawo dashi gida inda Mummy Zuwaira ta amshe shi.
Side d'in Ummah kuwa ana kan bincike yanda aka gano rusted gas cylinder da kuma fasashshen gidan lighter.
Kowa yayi tunanin cylinder Ummah ce, amma abin mamaki da aka duba sai aka ga Tata a kitchen, nan fa mamaki ya cika kowa.
Advertisement
Hankalin Mummy kuwa yayi dubu ya tashi, dan tasan ita kam Tata ta ƙare.
Gashi babu wata hanyar da zata bi ta fita ta siyo wani, wata dabara ce ta fad'o mata da daddare ta zaga ta shiga side d'in Abba ta bud'e store ta d'auko wani.
Tun daga ranan aka saka wa Mummy Ido, bayan masu bincike sun tabbatar da cewa kunna wutar akayi ta hanyar buɗe gas ɗin sannan aka cillo wuta, sanadiyan wutar kenan.
Hankalin Mummy ya kwanta tunda ta samu hanyar wanke kanta.
Bayan anyi sadakan uku ne washe gari mummy Zuwaira tazo ta ciccire kayan Aaman wanda yake store da d'akin shi, sannan ta sa aka kar6o spare key wajan Abban su na motar Haseenah, nan ta loda kayan a ciki ta fito tana faman sharan hawaye hanun ta riƙe da Aaman.
Mummy ce ta fito ta dube ta sannan tace" Malama ina zaki kai motar ko ya zama naki kenan?"
Cike da takaici Mummy Zuwaira tace" Lauratu karki furta abinda zaki kasa maimaita da anjima, dan zan miki illa, sannan karkiyi tunanin kinci bulus, i will surely get back to u, wallahi ki kuka da kanki"
Tana gama faɗin haka ta shige motar ita da Aaman suka bar gidan.
Mummy kuwa ranan murna ce fal zuciyar ta, dan yanzu ta tabbatar gida ya zama nata, dukiya ta zama Tata, miji ya zama nata.
Dan haka suka baje kolin su ita da Saratu, ga wasu sabin k'awayen da tayi wanda koyaushe gidan da mutane, wani lokacin kuma in suka fice shikenan bazata dawo ba sai dare.
Abba na gani amma bai isa yayi Magana ba, dan a gaban k'awayen ta zata mishi masifa.
Dan haka ya dena cewa komai ya zuba mata ido.
Tunda akayi rasuwar babu wanda ya sake takowa gidan, can gidan su Ummah suka cigaba da kar6an gaisuwan su.
Dan haka Mummy ta dad'a sakin jiki ba abinda ya dame ta.
Mum Haseen ma tunda haka ta faru bata sake kiran Mummy ba balle ta tako k'afan ta.
Haseen kuwa ko yaushe zaka ganshi d'auke da wayar shi yana kallon hotunan da yayi wa Haseenah last had'uwan da sukayi kafin ta rasu.
Wajan aiki ma ya dena zuwa kullum yana d'aki, da yake a Company daddy shi dama yake sai bai matsa mishi ba, dan ko bai dena zuwa ba shi zai dakatar da shi, dan yana buk'atan nutsuwa.
Haka zai zauna ya zuba ma hoton ido, wani lokacin yayi ta sambatu, in hakan bai mishi ba kuma sai kuka.
Randa abun ya motsa kuma haka zai wuni ba magana, ko abinci baya ci, sai dai Mum d'inshi tayi ta lallashi sannan zai ci yayi wanka.
Advertisement
Da taga abun na son zama matsala sai ta kira best friend d'inshi Habeeb tace dan Allah yazo yana zama da Haseen suna d'an fita yana zagawa ko damuwar shi zata ragu.
Hakan kuwa akayi.
Da safe kuwa Ammi ta shirya dan zuwa duba Haseenah, fitowa tayi palour ta hango Mahmud sanye cikin farar riga da three-quarter, yayi kyau sossai hasken shi ya dad'a fitowa.
Duban shi tayi tace" Auta muje ka rakani asibitin mana"
Bai san sanda ya fad'o daga kan kujerar ba yayi zaman dirshan, zare ido yayi yace" Ammi Allah ba zani ba, ki tafi kawai Allah kiyaye hanya"
6ata rai tayi tace" kaga banason shashanci kaji ko?"
Marairaice fuska yayi sannan yace" nikan ma Ammi cikina ciwo yake yanzu ma da kika ganni nan ke nake jira dama ki bani magani"
Ta sani sarai k'arya yake dan haka tace" kaje wajan yayan ka mana ko yau nice likitar?"
Da sauri ya mik'e yace" barshi ma na tuna inada shi a d'aki na, sai kun dawo"
Bai jira me zata ce ba ya haye sama da gudu har yana tuntu6e.
Dariya Ammi tayi a ranta tace " Allah yaye maka"
Lokacin da Ammi ta ga halin da Haseenah ke ciki saida ta zubda hawaye, dan duk yanda Sameer ya so ya describing Mata situation d'in da take ciki abun ya wuce nan, in ba faɗa maka akayi ba bazaka yi tunanin mutum ne ba.
Dan saboda maganin da aka shafa mata cikin net aka saka ta ga oxygen mak'ale a hancin ta.
Ganin bazata iya juran ganin ta ba ya sata ficewa daga asibitin.
Kano kuwa bayan an gama sadakan bakwai ne Mummy Zuwaira ta rok'a Abba ya bar Mata Aaman, ba tare da wani tunani ba ya amince mata.
Aiko komawar shi gida knan ya samu Mummy zaune palour, tana ganin shi ta mik'e dama shi take jira, duban shi tayi a wulak'an ce tace" ya na ganka hannu na bin cinya ina yaron yake?"
A sanyaye yace" na bar musu shi a wajan su ai"
Wata zagi Mummy ta auno tace ya koma ya d'auko shi ita ya kamata ya rik'e shi.
Wucewa yayi ya barta nan tsaye tana surfa masifa da ashar.
Dan yanzu target d'inta kan Aaman ne, dan tasan tunda shi namiji ne to in Abba ya rasu shi zai janye duk kason.
Dan haka idon ta ya rufe bata jira komai ba ta d'au gyalen ta ta shige mota ta fice a gidan.
Bata tsaya ko ina ba sai k'ofar Mummy Zuwaira.
Tun daga waje ta fara fad'in a fito mata da yaron miji.
Babu wanda ya kula ta har ta iso palour.
Su Umaimah da baby da mummy Zuwaira ne zaune suna hira, sai Aaman dake kan cinyar Mummy tana bashi tea.
Nan Mummy ta hau girgiza tana cewa a bata shi.
Ba wanda ya kalli inda take balle Su san akwai wata halitta a wajan.
Hakan ya dad'a 6ata mata rai.
Da zafin jiki ta nufa Mummy Zuwaira ta sa hannu da nufin janyo Aaman.
Carap Mummy Zuwaira ta rik'e hanunta sannan ta ajiye Aaman gefe ta mik'e.
Duban Umaimah tayi da ita ma jikinta ya hau rawa dan ji take kaman ta kashe Mummy.
Mummy Zuwaira tace" Umaimah kulle mun k'ofar palour"
Kaman jira take nan ta rufe k'ofar, Mummy Bata San nufin hakan ba shiyasa bata damu ba.
Sai ma ta shak'o wuyar Mummy Zuwaira.
Aiko Bata yi aune ba taji saukar marin da ya gigita mata lissafi.
Juyawa tayi taga waye da wanann aikin, Umaimah ta gani tsaye jikin ta har tsuma yake.
Ga baby rik'e da sandar moper, d'irka Mata Baby tayi a baya nan Mummy ta saki ihu.
Sake ta Mummy Zuwaira tayi ta koma gefe ta zauna.
Yayinda Baby da Umaimah suka kayar da Mummy k'asa, Nan suka haye kanta suka hau dukan ta ta ko ina.
Seda suka tabbatar taji jiki sannan suka sauka.
Lokacin Mummy kuka take tana numfashi sama sama.
Duban ta Mummy Zuwaira tayi sannan tace" Ni banida lokacin fad'a dake saboda inada dai dai ke, sannan ko kasheki sukayi ba wanda ya isa ya kamani tunda ke kika shigo har gida"
Ta kalli su Umaimah, nan suka ja Mummy suka fice da ita waje.
Kuka sossai take ganin lokaci kaɗan sun sauya Mata halittar jiki da fuska.
Yanda bakin Mummy yayi suntun dama gata da dogon baki, inka ganta ko bakada niyar dariya ba zaka san lokacin da zai k'wace maka ba.
Da k'yar ta ja jiki ta shige motar ta ta fice.
Tana shiga gida ta tarar Saratu zaune a palour,tana ganin Mummy ta tuntsire da dariya tace" Mummy hatsari kikayi ne?"
Bata kula ta ba ta wuce d'aki.
*Abuja*
Yau kwanan Haseenah bakwai a asibiti, jiki da sauk'i sossai dan an cire mata oxygen din, sai dai har yanzu ta hanci ake bata abinci dan ba halin ta6a ta.
Magani kawai ake shafa mata a mayar a kwantar da ita.
K'unan kuwa har ya fara 6arewa da kanshi, har na fuskan ta ma.
Koyaushe sameer kan shiga duba ta fiye da sau biyar.
Ammi ma takan je, Mahmud kuwa da Ammi ta matsa mishi yaje sai ya fashe da kuka ya fara cewa"....
Please vote nd drop ur comments
Advertisement
- In Serial106 Chapters
The Legendary Ghost Hunter
Thousands of years ago, the First Expungement came. The world changed, and humanity was nearly wiped out. Thankfully, with the paracausal power of Angelicas, humans was able to push back the Ghost tide and rebuild their civilization.Now, however, it was time for the Second.Finn Thresher was just a normal university student at first. He, like the rest of the public world, had no idea what was coming for them — but sometimes, just because you don’t know, doesn’t mean you can’t be harmed.His family… his sight… his purpose. All lost to the paranormal.It was time to abandon his beliefs. To throw away his morals.After all… if these creatures weren’t human anyway, there was no point in showing them humanity.In the first battle of this war, the Ghosts won, nearly driving the human race to extinction. In the second, the humans fought back with the power of Angelicas and managed to secure a victory.Now, the third and final round was approaching — and this time, it’s personal.
8 813 - In Serial13 Chapters
Karma - The Game
Martin Cline is somehow an average man with an average life. Truth be told: He is bored to death until he finds a new purpose.Nothing excites him much but a new game called Karma. It is the first of its kind and has almost nothing to do with the """"old"""" games played on plain displays.Karma is a true virtual world Martin wants to explore and fulfill himself a tiny dream he had no chance to chase in his life so far.It is easier said than done. Karma might just be more than a fantasy world with mmorpg elements set up in a virtual reality.
8 193 - In Serial13 Chapters
HARU
Dark forces rule Japan in 1867. Things that should never have happened, changed history forever. Follow Arata Haru on his quest for revenge against the Daimyo who decimated his clan after their bones. Travel through a dangerous land where thieves plunder the mountains, soldiers become corrupt, monks pray to ancient gods, sorcerers create potions with cruel effects, legendary samurai resurface, and the dead dance again to the drums of war.
8 128 - In Serial11 Chapters
Soulblade
Magic is a dangerous tool, wielded by Soulblades. They are necessary for the survival of humanity, but when an uncontrolled Soulblade can potentially destroy entire cities by accident, it only makes sense that heavy regulations are put in place to prevent such accidents. Cassian is a revolutionary who has stumbled onto the truth of magic and is willing to use it for the freedom of his fellow Soulblades. Darian is a king who only wants his people to thrive under his rule. Kara is a Soulblade Guardian, burdened with the responsibility of exterminating any Soulblades who fall out of line.
8 84 - In Serial9 Chapters
The Grand eGress
Original Sci-fi Fantasy LN by Itsutsu KamiA young man becomes a beta tester for a new type of VR to help pay for his dorm fees but gets more than he bargains for.
8 144 - In Serial14 Chapters
Quest for Madness
This world is one of many that has been enriched by magic. Unlike the other worlds, this one's magic can force the user into the long windy road of madness. The main character must make hard choices to leave the only place she has ever known, one that negates and protects from dangers of the rest of the world, all to bring her older brother back. She must decide how much to rely on the magic to safely complete her objective. Balancing on a knife's edge or become a grotesque form of herself that ravages all those around her.
8 189

