《HASEENAH》PAGE 41&42
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
Godiya ga duk wani masoyin wannan littafi, na gode sossai da kulawarku da kuma karfin gwiwar da kuke bani koda yaushe, *Rumanah(Auta) kin kasance ɗaya daga cikin masoyana wanda ke mun magana ta pc, na gode da soyayyarki gareni da kuma addu'oinki, nima ina sonki sossai, ban manta da kuba*
Mom of 12
Raleeyerh
Hapcy
Ummu nawwar
umcee
Nanush
hauwee
Da duk sauran wanda ban ambata ba kuna raina, Allah bar zumunci da k'auna.
*41~42*
A firgice ya farka yana faɗin" gawa ta tashi, jama'a fatalwa"
Dariya da haushi ne suka cika Sameer, dubanshi yayi yace" Allah Mahmud in baka nutsu ba ranka zai 6aci"
Shiko sai zare ido yake yi a tsorace, juyawa yayi ya kalli back seat ya ga wayam, marairaice wa yayi kaman zeyi kuka yace" yaya na faɗa maka fatalwa ce baka yarda ba, gashi yanzu ta 6ace"
Nuna mishi k'ofa yayi yace" get out "
Sum sum ya fice zuciyar shi na bugawa.
Suna shiga gida sameer ya hango Mahmud zaune gefen Ammi kaman zai d'ale cinyarta, duk yayi kalan tausayi yace" Ammi wallahi da gaske nake miki"
Hararar da sameer ya zabga mishi ne ya sashi yin shuru.
Bayani ya shiga yi wa ammi, tunda ya fara magana ta nutsu tana jin shi har ya gama.
Duban shi tayi tace" son yanzu wani mataki ka ɗauka?"
"Tana asibiti na barta wajan Dr Abeed, yanzu firstly sai an Fara treating k'onan da tayi, wanda yace indai za.ayi amfani da most effective requirements bazata wuce 2weeks ba zata warke, secondly Kuma shine theatre da za.a mata a fuskanta in order to gain her normal look"
Gyad'a Kai Ammi tayi sannan tace "hakan ma yayi, da safe zan bika muje in duba ta"
Nan suka mik'e kowa da abinda yake sak'awa a ranshi.
Asibiti kuwa Haseenah oxygen aka saka mata, aka saka mata robar abinci ta hanci.
Ba tare da 6ata lokaci ba Dr Abeed ya sa nurses suka cire mata rigar jikinta aka saka mata na asibiti, bayan sun shafe mata jikin da wani magani mai ruwa.
Aaman kuwa kwana biyu yayi aka dawo dashi gida inda Mummy Zuwaira ta amshe shi.
Side d'in Ummah kuwa ana kan bincike yanda aka gano rusted gas cylinder da kuma fasashshen gidan lighter.
Kowa yayi tunanin cylinder Ummah ce, amma abin mamaki da aka duba sai aka ga Tata a kitchen, nan fa mamaki ya cika kowa.
Advertisement
Hankalin Mummy kuwa yayi dubu ya tashi, dan tasan ita kam Tata ta ƙare.
Gashi babu wata hanyar da zata bi ta fita ta siyo wani, wata dabara ce ta fad'o mata da daddare ta zaga ta shiga side d'in Abba ta bud'e store ta d'auko wani.
Tun daga ranan aka saka wa Mummy Ido, bayan masu bincike sun tabbatar da cewa kunna wutar akayi ta hanyar buɗe gas ɗin sannan aka cillo wuta, sanadiyan wutar kenan.
Hankalin Mummy ya kwanta tunda ta samu hanyar wanke kanta.
Bayan anyi sadakan uku ne washe gari mummy Zuwaira tazo ta ciccire kayan Aaman wanda yake store da d'akin shi, sannan ta sa aka kar6o spare key wajan Abban su na motar Haseenah, nan ta loda kayan a ciki ta fito tana faman sharan hawaye hanun ta riƙe da Aaman.
Mummy ce ta fito ta dube ta sannan tace" Malama ina zaki kai motar ko ya zama naki kenan?"
Cike da takaici Mummy Zuwaira tace" Lauratu karki furta abinda zaki kasa maimaita da anjima, dan zan miki illa, sannan karkiyi tunanin kinci bulus, i will surely get back to u, wallahi ki kuka da kanki"
Tana gama faɗin haka ta shige motar ita da Aaman suka bar gidan.
Mummy kuwa ranan murna ce fal zuciyar ta, dan yanzu ta tabbatar gida ya zama nata, dukiya ta zama Tata, miji ya zama nata.
Dan haka suka baje kolin su ita da Saratu, ga wasu sabin k'awayen da tayi wanda koyaushe gidan da mutane, wani lokacin kuma in suka fice shikenan bazata dawo ba sai dare.
Abba na gani amma bai isa yayi Magana ba, dan a gaban k'awayen ta zata mishi masifa.
Dan haka ya dena cewa komai ya zuba mata ido.
Tunda akayi rasuwar babu wanda ya sake takowa gidan, can gidan su Ummah suka cigaba da kar6an gaisuwan su.
Dan haka Mummy ta dad'a sakin jiki ba abinda ya dame ta.
Mum Haseen ma tunda haka ta faru bata sake kiran Mummy ba balle ta tako k'afan ta.
Haseen kuwa ko yaushe zaka ganshi d'auke da wayar shi yana kallon hotunan da yayi wa Haseenah last had'uwan da sukayi kafin ta rasu.
Wajan aiki ma ya dena zuwa kullum yana d'aki, da yake a Company daddy shi dama yake sai bai matsa mishi ba, dan ko bai dena zuwa ba shi zai dakatar da shi, dan yana buk'atan nutsuwa.
Haka zai zauna ya zuba ma hoton ido, wani lokacin yayi ta sambatu, in hakan bai mishi ba kuma sai kuka.
Randa abun ya motsa kuma haka zai wuni ba magana, ko abinci baya ci, sai dai Mum d'inshi tayi ta lallashi sannan zai ci yayi wanka.
Advertisement
Da taga abun na son zama matsala sai ta kira best friend d'inshi Habeeb tace dan Allah yazo yana zama da Haseen suna d'an fita yana zagawa ko damuwar shi zata ragu.
Hakan kuwa akayi.
Da safe kuwa Ammi ta shirya dan zuwa duba Haseenah, fitowa tayi palour ta hango Mahmud sanye cikin farar riga da three-quarter, yayi kyau sossai hasken shi ya dad'a fitowa.
Duban shi tayi tace" Auta muje ka rakani asibitin mana"
Bai san sanda ya fad'o daga kan kujerar ba yayi zaman dirshan, zare ido yayi yace" Ammi Allah ba zani ba, ki tafi kawai Allah kiyaye hanya"
6ata rai tayi tace" kaga banason shashanci kaji ko?"
Marairaice fuska yayi sannan yace" nikan ma Ammi cikina ciwo yake yanzu ma da kika ganni nan ke nake jira dama ki bani magani"
Ta sani sarai k'arya yake dan haka tace" kaje wajan yayan ka mana ko yau nice likitar?"
Da sauri ya mik'e yace" barshi ma na tuna inada shi a d'aki na, sai kun dawo"
Bai jira me zata ce ba ya haye sama da gudu har yana tuntu6e.
Dariya Ammi tayi a ranta tace " Allah yaye maka"
Lokacin da Ammi ta ga halin da Haseenah ke ciki saida ta zubda hawaye, dan duk yanda Sameer ya so ya describing Mata situation d'in da take ciki abun ya wuce nan, in ba faɗa maka akayi ba bazaka yi tunanin mutum ne ba.
Dan saboda maganin da aka shafa mata cikin net aka saka ta ga oxygen mak'ale a hancin ta.
Ganin bazata iya juran ganin ta ba ya sata ficewa daga asibitin.
Kano kuwa bayan an gama sadakan bakwai ne Mummy Zuwaira ta rok'a Abba ya bar Mata Aaman, ba tare da wani tunani ba ya amince mata.
Aiko komawar shi gida knan ya samu Mummy zaune palour, tana ganin shi ta mik'e dama shi take jira, duban shi tayi a wulak'an ce tace" ya na ganka hannu na bin cinya ina yaron yake?"
A sanyaye yace" na bar musu shi a wajan su ai"
Wata zagi Mummy ta auno tace ya koma ya d'auko shi ita ya kamata ya rik'e shi.
Wucewa yayi ya barta nan tsaye tana surfa masifa da ashar.
Dan yanzu target d'inta kan Aaman ne, dan tasan tunda shi namiji ne to in Abba ya rasu shi zai janye duk kason.
Dan haka idon ta ya rufe bata jira komai ba ta d'au gyalen ta ta shige mota ta fice a gidan.
Bata tsaya ko ina ba sai k'ofar Mummy Zuwaira.
Tun daga waje ta fara fad'in a fito mata da yaron miji.
Babu wanda ya kula ta har ta iso palour.
Su Umaimah da baby da mummy Zuwaira ne zaune suna hira, sai Aaman dake kan cinyar Mummy tana bashi tea.
Nan Mummy ta hau girgiza tana cewa a bata shi.
Ba wanda ya kalli inda take balle Su san akwai wata halitta a wajan.
Hakan ya dad'a 6ata mata rai.
Da zafin jiki ta nufa Mummy Zuwaira ta sa hannu da nufin janyo Aaman.
Carap Mummy Zuwaira ta rik'e hanunta sannan ta ajiye Aaman gefe ta mik'e.
Duban Umaimah tayi da ita ma jikinta ya hau rawa dan ji take kaman ta kashe Mummy.
Mummy Zuwaira tace" Umaimah kulle mun k'ofar palour"
Kaman jira take nan ta rufe k'ofar, Mummy Bata San nufin hakan ba shiyasa bata damu ba.
Sai ma ta shak'o wuyar Mummy Zuwaira.
Aiko Bata yi aune ba taji saukar marin da ya gigita mata lissafi.
Juyawa tayi taga waye da wanann aikin, Umaimah ta gani tsaye jikin ta har tsuma yake.
Ga baby rik'e da sandar moper, d'irka Mata Baby tayi a baya nan Mummy ta saki ihu.
Sake ta Mummy Zuwaira tayi ta koma gefe ta zauna.
Yayinda Baby da Umaimah suka kayar da Mummy k'asa, Nan suka haye kanta suka hau dukan ta ta ko ina.
Seda suka tabbatar taji jiki sannan suka sauka.
Lokacin Mummy kuka take tana numfashi sama sama.
Duban ta Mummy Zuwaira tayi sannan tace" Ni banida lokacin fad'a dake saboda inada dai dai ke, sannan ko kasheki sukayi ba wanda ya isa ya kamani tunda ke kika shigo har gida"
Ta kalli su Umaimah, nan suka ja Mummy suka fice da ita waje.
Kuka sossai take ganin lokaci kaɗan sun sauya Mata halittar jiki da fuska.
Yanda bakin Mummy yayi suntun dama gata da dogon baki, inka ganta ko bakada niyar dariya ba zaka san lokacin da zai k'wace maka ba.
Da k'yar ta ja jiki ta shige motar ta ta fice.
Tana shiga gida ta tarar Saratu zaune a palour,tana ganin Mummy ta tuntsire da dariya tace" Mummy hatsari kikayi ne?"
Bata kula ta ba ta wuce d'aki.
*Abuja*
Yau kwanan Haseenah bakwai a asibiti, jiki da sauk'i sossai dan an cire mata oxygen din, sai dai har yanzu ta hanci ake bata abinci dan ba halin ta6a ta.
Magani kawai ake shafa mata a mayar a kwantar da ita.
K'unan kuwa har ya fara 6arewa da kanshi, har na fuskan ta ma.
Koyaushe sameer kan shiga duba ta fiye da sau biyar.
Ammi ma takan je, Mahmud kuwa da Ammi ta matsa mishi yaje sai ya fashe da kuka ya fara cewa"....
Please vote nd drop ur comments
Advertisement
- In Serial19 Chapters
Bloodlust
Born with an uncommon sickness, Asmund was raised in solitude inside a cage of glass. Living all his life hating this damned world, even as his death was quickly approaching never did he let go of his wrath. But... As he was right about to reach the river Styx, something unexpected happened.A new change came to the world, and a chance for Asmund to gain all that he always desired, his merciless heart set on conquering the world!WARNING: This story contain pretty much anything that could hurt the poor sensibility of the weak hearted... Blood, Gore, Sex, Weird Puns and Vulgarities! Also the author is french so it doesn't help! Fuckign french, who like french?! Also the story have a EVIL protagonist, so please bear it in mind when you read this story!Another word from me, the damn french! I already started writing this story a while ago and was only sharring it among the guys of the Den of Madness, and decided to share it on a whim. Suggestion? Won't listen to them. Praise? Sure go ahead, always cool to hear it not that it would change anything trololol! Insult? Used to them, won't change anything either. Critisism? Don't care.There you go! NOW ENJOY THE DAMN STORY UNTIL I'M BANNED FOR WRITING SOMETHING YET AGAIN DISTURBING!
8 219 - In Serial33 Chapters
Monstrous Heroic Decimation
Can a single person rise above everything the world throws at him? A world where a single person's life is only worth the amount they're able to carve out of the other's body... a world where the veil of society is held together with a thin veneer, in tiny pockets of a world they once inhabited... Sam is about to hit the coming of age ceremony, and his life up til this point has been good with two caring parents attending school everyday, yet will he throw all that away because of what's about to come? A cultivation-esque, monster taming/evolution story.
8 161 - In Serial19 Chapters
A new horizon
Trevor committed suicide to end his sufferings and pain. Only to realize that he got transmigrated to another world and the first thing he saw after opening his eyes was a woman lying dead beside him. "Dear God, do you want me to go through another suicide again? Do you hate me so much?" Trevor said as he thought he would be accused of murder. But soon he realized that the world he was in had different rules. Take a walk with Trevor, as he rises above everyone else and takes control of his own destiny. -------This is a [Game of Thrones] X [Star Wars] fan-fic. It will be a little slow burn but I will try to go through all the lore and stories of both the books. Hope you will enjoy it. Sorry - I am still trying to make the conversation parts more acceptable and funny so bear me with this.
8.18 183 - In Serial72 Chapters
The Akashic Record Entry 1: Ascension
The Akashic Record, the record of all things, begins with the story of a man, A man on a long and arduous journey, a journey to surpass himself,To become more than what he was, to attain what he could be,A journey full of pain, suffering, adversity, and sacrifice.Marked with loss and regret, Slava strives forward,To reach where no one has ever reached before.Despite not always having a destination,Despite facing failure after failure,He persists and struggles,To find his purpose. I am Akash,The Keeper and Recorder.As Observer, it is my duty to document,To write this story and the world which sprouted from it.Let me show you what I have witnessed,Slava’s heart-wrenching story,The world it broughtThrough The Akashic Record
8 118 - In Serial66 Chapters
The Rícewelig Crown
King Firgen wants to retire but has no heir. Magic and monsters are rising within his Kingdom and Firgen is reluctant to deal with the ever increasing turmoil. Using his mighty powers of inappropriate delegation, Firgen issues a proclamation: The first person to discover and remove the source of Rícewelig's woes will be named heir. Questing knights, impatient nobles, and reluctant men-at-arms disperse across the country, all chasing their own agenda, leaving Firgen's desire trampled in the dust. Note: Many names are in Old English. Pronounce them however you wish.
8 140 - In Serial41 Chapters
Regretting And Rejecting
When Hannah is mated to her old bully, everyone implores her to move on and forgive him for the good of the pack. She will need to decide if the pack is worth risking her happiness or if she should do what she's wanted to do for years.Leave them all behind.**This is an enemies to lovers story. If you don't like that trope, don't read this story**________________________________________"I think I could give you a chance." I say quietly and he let's out a breath of relief. He takes my hand off of his face and places a kiss to my palm before resting it on his chest, covering it with both of his larger hands."Really?" He asks hopefully. I give him another wide smile.Before I narrow my eyes and scowl at him, ripping my hand away from him. His brows furrow in confusion as I take a step back."No."Cover made by @ViaAlyssaNicole
8 316

