《HASEENAH》PAGE 39&40
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
*39~40*
Da gudu ya sauko d'auke da wata babbar therapy box, d'aga ta yayi ya Kaita d'akin da yake na baƙi.
Shimfid'a ta yayi kan gado sannan ya warware yadin ya bud'e iya fuskan ta.
Nan da nan ya fara bata taimakon gaggawa, sunkai kusan 30mins amma bata sake motsi ba, waya ya ciro ya kira d'aya daga cikin abokan shi, nan ya fara hura mata iska a baki, da k'yar ya samu ta fara tari daganan ta koma ta kwanta.
Juya kai kawai take da hannu, a hankali idon ta ya fara bud'e wa.
Gaba ɗaya ya kad'a yayi jajir, hawaye ke gangaro wa daga idon ta.
Tsura mishi ido tayi kaman me tunanin wani abu, shiko banda sannu babu abinda yake furta wa.
Wani dogon numfashi taja sai kuma bakin ta ya fara motsi kaman tanason tayi magana amma ta kasa.
Dubanta yayi cike da tausaya wa yace" ruwa kike son Sha in kawo Miki?"
Shuru Bata amsa mishi ba, a karo na biyu ya sake faɗin" me kikeso a kawo Miki?"
Nan ma shuru kamar bata jin shi.
Mik'ewa yayi ya shige kitchen ya d'auko Goran ruwa da cup ya fito, zama yayi a gefen ta, yana son bata ruwa amma bai san ta ina zai fara ba, dan yasan jikinta zafi zai mata.
Wata dabara ce ta fad'o mishi, komawa yayi ya d'auko spoon sannan ya 6alle murfin ruwan, zubawa yayi a murfin robar ruwan sannan ya saka spoon ya d'an bud'e Mata bakin kaɗan ya tsiyaya mata.
Nan da k'yar take iya had'iye wa.
Kaɗan ta iya sha sannan ya fara gangaro wa.
Tagumi yayi yana ta faman mata tambayoyi amma shuru.
Advertisement
Hakan yayi dai dai da zuwan Dr Muhammad, ganin Haseenah cikin wannan hali ba k'aramin kad'a shi yayi ba.
Nan sameer ya bashi labarin duk abinda ya faru.
Sossai ya tausaya mata.
Sameer ya k'ara da cewa" gashi ina ta tanbayar ta tayi shuru tak'i magana"
A sanyaye Dr Muhammad yace" aboki ka manta irin wa'yan nan basu magana, wani lokacin ma sukan rasa hankalin su gaba d'aya"
Shuru sameer yayi dan ya kasa furta komai.
Dr Muhammad ne ya dube shi yace" yanzu ya zakayi da ita gashi naga yau zaka wuce Abuja?"
Cike da rauni sameer yace" shine duk tunani na, kawai tafiya da ita zanyi a mata magani har muga abinda Allah zai yi"
Cike da gamsuwa Dr Muhammad yace" these is a good idea Dr, Nima Nan zan cigaba da bincike through internet muga ko zamu samu wata mafitar"
Gyad'a kai Dr Sameer yayi yace" Nagode abokina"
Nan sameer ya mik'e ya haye sama, d'akin k'anwar shi ya nufa ya bud'e wardrobe d'in ta ya Ciro wata doguwar riga mara nauyi.
Fitowa yayi ya dawo wajan ta,amma ya rasa ta ina zai fara canja mata kayan.
Dr Muhammad ne ya dube shi yace" Dr hakuri zakayi ka canja mata, lalura ce kuma ceton rai zakayi"
Gyad'a kai yayi yace" to plx can U excuse us?"
Mik'ewa Dr Muhammad yayi yace" why not?"
Ficewa yayi ya ja musu k'ofar.
Runtse idon shi yayi sannan ya tallafo kanta, a hankali ya fara saka mata idon shi rufe.
A haka ya zura mata, Haseenah kuwa Allah ne kaɗai yasan azabar da takeji amma ba halin magana.
Hakan ya saka ta suma.
Seda ya gama saka mata sannan ya buɗe idon shi, gani yayi idon ta buɗe amma bata motsi.
Da sauri ya d'auki ruwa ya yayyafa mata.
Seda ya gyara mata zaman rigar sannan ya fito.
Dr Muhammad ya samu tsaye a wajan, nan suka tsaya tattauna wa kan yanda zasu ɓullo wa lamarin.
Advertisement
Daga nan sukayi sallama ya tafi.
Mahmud kuwa tunda ya haye sama ya kullo k'ofar bai sake fitowa ba.
Sameer wayar shi ya ɗauka ya danna numbar Ammin shi, nan ya mata bayani, shuru tayi tsawon wasu mintina ba tare da tace komai ba.
A karo na biyu Sameer yace" Ammi Are u there?"
"Yes son, Amma kana ganin babu wata matsala?"
Gyad'a kai yayi kaman yana gaban ta yace" Ammi wallahi inkin ganta saikin zubar da hawaye,very tortured"
"Shikenan Allah kawoku lafiya"
"Amin" yace sannan ya katse wayar.
Kiran wayar Mahmud yayi yana d'aga wa yace" Are u ready to go or I should go alone?"
Da sauri yace " on ma way stepping downstairs"
Bud'e k'ofar yayi a hankali, kanshi ya fara sakowa sannan ya lek'o, ganin ba kowa ya sashi saukowa a hankali a fito.
Seda ya rufe gidan sannan ya nufa motar.
Sameer ya hango zaune ya riga yayi key wa motar ma, back seat ya lek'a ya hango Haseenah kwance idon a rufe.
Shiga gaba yayi kafin ya kulle sameer ya bawa motar wuta.
Kai tsaye hanyar Abuja suka d'auka.
Time to time Sameer Kan juyo dan ganin halin da Haseenah ke ciki.
Mahmud kuwa baccin dole yayi dan inyace ido biyu zasu isa to ba makawa yasan wani abu zai biyo baya.
*KANO*
Mummy Tabi duk wata hanyar da zata bi dan ganin ta d'auko wannan cylinder Amma Abu yaci tura, Mummy Zuwaira da Mummy Saudatu sun kasa sun tsare, ko k'wak'k'waran motsi Mummy tayi akan idon su.
Hakan yasa wuni ɗaya ta fice a hayyacin ta, ina baka san halin ta ba zakayi tunanin mutuwar ce ta girgiza ta.
Haseen kuwa addu'a aka fara tofa mishi cikin ruwa da nasihohi sannan ya samu ya fara magana, amma baya wuce yace eh ko a'a, sai in an mishi ta'aziya yace "ameen" shikenan.
Mum Haseen ce tasa Mummy gaba tana faɗin" haba yaya meyasa baki yi tunanin abinda zaije ya dawo ba kika yanke wannan mummunar hukuncin? Yanzu kina ganin alhaki zai barki ki zauna lafiya? Kina ganin shikenan burin ki ya cika ko? Bayan kinsan Zuwaira da Saudat na raye, wallahi kinyi babban kuskure, kuma abinda hakuri bai baki ba rashin sa bazai ta6a baki ba"
Shuru Mummy tayi badon tayi nadamar abinda tayi ba, kawai shuru tayi saboda kudirin haɗa auran Saratu da Haseen,amma ba don haka ba mum Haseen Bata Isa ta sata gaba tana faɗa mata son ranta ba tunda ba uwarta bace.
Ganin haka yasa mun Haseen cigaba da cewa" ki san yanda zakiyi ki fidda kanki, dan wallahi babu hanuna cikin wannan abu, wannan meye inba son zuciya da zalunci ba? Ke yanzu ko da garwashi ne ya k'ona ki ya zakiji? Ballantana rai kacokan ki salwantar da bayin Allah wanda basu jiba basu gani ba kawai saboda son zuciya da kishin banza duk akan miji, to yanzu in mijin ya sake ki ya zakiyi?"
Da sauri Mummy ta mik'e ta bud'e k'ofar ta nuna wa mum Haseen sannan tace" tashi ki fita tun kafin nayi abinda baki tunani"
Cike da 6acin rai mum Haseen ta mik'e ta nufa hanyar fita, har ta kai bakin k'ofar ta juyo tace" zan tafi amma ki sani duk abinda yaje ya dawo karki nemeni"
Tana kaiwa nan ta fice ta nufa wajan su Mummy Zuwaira ta zauna.
Sai bayan la'asar Sameer suka shiga Abuja, tun kafin ya k'araso ya Kira Dr Abeed dake aiki a asibitin FMC ya sanar mishi da abinda ya faru.
Saboda haka suna isa asibitin ya wuce, an rigada an gama komai yana isowa aka d'auko gadon marasa lafiya aka d'aura Haseenah suka wuce da ita ciki.
Saida ya gama duk abinda zeyi sannan ya dawo ya ja motar ya nufa gida, har lokacin Mahmud bacci yake yi dan yana farkawa zai koma ya kwanta.
Suna isa Sameer ya d'aga hannu ya kwad'a wa Mahmud mari saida hular kanshi ta tuntsire, a firgice ya farka yana faɗin....
Plx vote nd drop ur comme
Advertisement
- In Serial171 Chapters
Heart of Dorkness
When an accident causes the early death of two young women, one is chosen to become a hero, a saviour, and a servant of the God of Heroes! This is not her story. This is the story of Valeria, whose soul clung to her friend’s, and who was dragged into a new world where her wandering spirit was claimed by the Goddess of Darkness. And so, one who doesn’t belong grows to become the servant of the Dark Goddess, a servant—definitely not a daughter—who will usher in a new age of despair and disgust. The only problem is, she’s really bad at the whole “evil” thing, not that she’s unwilling to do her best to please her adoptive mom, the Dark Goddess Luciana.
8 115 - In Serial15 Chapters
Life in Diamond no Ace with a system
A 19-years old boy who was watching the Animation "Diamond no Ace" just as he finishes he feels un-satisfaction as he imagine himself in the story about how he would he done it if he was in the anime *cough* with normal fantasy that everyone desire a system. Just as he was watching anime the threat of dead made him to do what he was supposed but with his mistake he was shocked unconscious --------------------------------------------------The characters in the story is all owned by its there own original creator and i only own the character that i have created in these book. This story is all based on my imagination and this might not follow the same plot as the original one.-------------------------------------------------- ###ENJOY READING MY FAN-FICTION ###
8 165 - In Serial72 Chapters
Ninth World Lia's Struggle
Life is never as it seems and one can find themselves in different situations. What if you were to find yourself in a rather odd one. Magic, swords, war, amongst other things. That is what our lead found when she was reincarnated. Amelia bellevie, a simple girl with a simple life, that is until she got done in by truck-kun. Now she is having to find her way around the ninth world. A battle world created by the eight gods of the main races for entertainment, as well as for competition. Will she make friends and have a good life? or go into a darker path of hatred and murder? the cover is a character named Casselia illustrated by Selenada, commisioned by ShiningSiria. However, this is how I imagine Amelia looks like.
8 400 - In Serial32 Chapters
M-chan Wars: Rise and Fall of the Cat Tyrant
Welcome to M-chan, the place where individuals called denizens fight over any little thing with incredulous powers or sheer tenacity. This time, the Cat Tyrant has unleashed a deadly virus, taking over M-chan for itself. Read about how the other denizens fight back to reclaim M-chan, along with all the crazy antics and atrocities that occurs in the process! Warning: Disturbing content ahead. Some LN, manga, anime knowledge required.
8 104 - In Serial19 Chapters
The Temptations for the Wallflower |Book 1 Complete; Book 2 In Progress|
Seahill, Northern Ireland; 1997Tabitha was the new girl in town, just around to help her sick grandmother with her bookshop. She was quiet, trying to keep out of the way of others, particularly the attention of men. She never meant to get his attention, not with his power. Stephen was the young head priest of the Church, revered by all in town. He never expected to find himself tempted by anyone, especially not her. He finds himself searching for her, and he does, running from him. What happens when he finds himself questioning his morals and she questions her place in her faith? Trigger warnings inside book(Editing is complete)[Both books will be published here]Cover by thewritingamateur#1 in wallflower#1 in catholic #2 in church#2 in Ireland#3 in thriller
8 154 - In Serial53 Chapters
Counting To Fifteen [Grey's Anatomy]
"What is she doing?" Mark asked Calypso. Daisy had flipped out, and Mark hadn't understood why. Her breakdown had come out of nowhere, and she had been mumbling to herself as she shut her eyes tightly."Counting to fifteen." Calypso had explained as if it were the most elementary concept ever. She had offered Mark a small smile. "It calms her down."~~~~~~~In which Daisy and her little sister are taken in by Mark Sloan[Following Season 8]
8 145

