《HASEENAH》PAGE 39&40
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
*39~40*
Da gudu ya sauko d'auke da wata babbar therapy box, d'aga ta yayi ya Kaita d'akin da yake na baƙi.
Shimfid'a ta yayi kan gado sannan ya warware yadin ya bud'e iya fuskan ta.
Nan da nan ya fara bata taimakon gaggawa, sunkai kusan 30mins amma bata sake motsi ba, waya ya ciro ya kira d'aya daga cikin abokan shi, nan ya fara hura mata iska a baki, da k'yar ya samu ta fara tari daganan ta koma ta kwanta.
Juya kai kawai take da hannu, a hankali idon ta ya fara bud'e wa.
Gaba ɗaya ya kad'a yayi jajir, hawaye ke gangaro wa daga idon ta.
Tsura mishi ido tayi kaman me tunanin wani abu, shiko banda sannu babu abinda yake furta wa.
Wani dogon numfashi taja sai kuma bakin ta ya fara motsi kaman tanason tayi magana amma ta kasa.
Dubanta yayi cike da tausaya wa yace" ruwa kike son Sha in kawo Miki?"
Shuru Bata amsa mishi ba, a karo na biyu ya sake faɗin" me kikeso a kawo Miki?"
Nan ma shuru kamar bata jin shi.
Mik'ewa yayi ya shige kitchen ya d'auko Goran ruwa da cup ya fito, zama yayi a gefen ta, yana son bata ruwa amma bai san ta ina zai fara ba, dan yasan jikinta zafi zai mata.
Wata dabara ce ta fad'o mishi, komawa yayi ya d'auko spoon sannan ya 6alle murfin ruwan, zubawa yayi a murfin robar ruwan sannan ya saka spoon ya d'an bud'e Mata bakin kaɗan ya tsiyaya mata.
Nan da k'yar take iya had'iye wa.
Kaɗan ta iya sha sannan ya fara gangaro wa.
Tagumi yayi yana ta faman mata tambayoyi amma shuru.
Advertisement
Hakan yayi dai dai da zuwan Dr Muhammad, ganin Haseenah cikin wannan hali ba k'aramin kad'a shi yayi ba.
Nan sameer ya bashi labarin duk abinda ya faru.
Sossai ya tausaya mata.
Sameer ya k'ara da cewa" gashi ina ta tanbayar ta tayi shuru tak'i magana"
A sanyaye Dr Muhammad yace" aboki ka manta irin wa'yan nan basu magana, wani lokacin ma sukan rasa hankalin su gaba d'aya"
Shuru sameer yayi dan ya kasa furta komai.
Dr Muhammad ne ya dube shi yace" yanzu ya zakayi da ita gashi naga yau zaka wuce Abuja?"
Cike da rauni sameer yace" shine duk tunani na, kawai tafiya da ita zanyi a mata magani har muga abinda Allah zai yi"
Cike da gamsuwa Dr Muhammad yace" these is a good idea Dr, Nima Nan zan cigaba da bincike through internet muga ko zamu samu wata mafitar"
Gyad'a kai Dr Sameer yayi yace" Nagode abokina"
Nan sameer ya mik'e ya haye sama, d'akin k'anwar shi ya nufa ya bud'e wardrobe d'in ta ya Ciro wata doguwar riga mara nauyi.
Fitowa yayi ya dawo wajan ta,amma ya rasa ta ina zai fara canja mata kayan.
Dr Muhammad ne ya dube shi yace" Dr hakuri zakayi ka canja mata, lalura ce kuma ceton rai zakayi"
Gyad'a kai yayi yace" to plx can U excuse us?"
Mik'ewa Dr Muhammad yayi yace" why not?"
Ficewa yayi ya ja musu k'ofar.
Runtse idon shi yayi sannan ya tallafo kanta, a hankali ya fara saka mata idon shi rufe.
A haka ya zura mata, Haseenah kuwa Allah ne kaɗai yasan azabar da takeji amma ba halin magana.
Hakan ya saka ta suma.
Seda ya gama saka mata sannan ya buɗe idon shi, gani yayi idon ta buɗe amma bata motsi.
Da sauri ya d'auki ruwa ya yayyafa mata.
Seda ya gyara mata zaman rigar sannan ya fito.
Dr Muhammad ya samu tsaye a wajan, nan suka tsaya tattauna wa kan yanda zasu ɓullo wa lamarin.
Advertisement
Daga nan sukayi sallama ya tafi.
Mahmud kuwa tunda ya haye sama ya kullo k'ofar bai sake fitowa ba.
Sameer wayar shi ya ɗauka ya danna numbar Ammin shi, nan ya mata bayani, shuru tayi tsawon wasu mintina ba tare da tace komai ba.
A karo na biyu Sameer yace" Ammi Are u there?"
"Yes son, Amma kana ganin babu wata matsala?"
Gyad'a kai yayi kaman yana gaban ta yace" Ammi wallahi inkin ganta saikin zubar da hawaye,very tortured"
"Shikenan Allah kawoku lafiya"
"Amin" yace sannan ya katse wayar.
Kiran wayar Mahmud yayi yana d'aga wa yace" Are u ready to go or I should go alone?"
Da sauri yace " on ma way stepping downstairs"
Bud'e k'ofar yayi a hankali, kanshi ya fara sakowa sannan ya lek'o, ganin ba kowa ya sashi saukowa a hankali a fito.
Seda ya rufe gidan sannan ya nufa motar.
Sameer ya hango zaune ya riga yayi key wa motar ma, back seat ya lek'a ya hango Haseenah kwance idon a rufe.
Shiga gaba yayi kafin ya kulle sameer ya bawa motar wuta.
Kai tsaye hanyar Abuja suka d'auka.
Time to time Sameer Kan juyo dan ganin halin da Haseenah ke ciki.
Mahmud kuwa baccin dole yayi dan inyace ido biyu zasu isa to ba makawa yasan wani abu zai biyo baya.
*KANO*
Mummy Tabi duk wata hanyar da zata bi dan ganin ta d'auko wannan cylinder Amma Abu yaci tura, Mummy Zuwaira da Mummy Saudatu sun kasa sun tsare, ko k'wak'k'waran motsi Mummy tayi akan idon su.
Hakan yasa wuni ɗaya ta fice a hayyacin ta, ina baka san halin ta ba zakayi tunanin mutuwar ce ta girgiza ta.
Haseen kuwa addu'a aka fara tofa mishi cikin ruwa da nasihohi sannan ya samu ya fara magana, amma baya wuce yace eh ko a'a, sai in an mishi ta'aziya yace "ameen" shikenan.
Mum Haseen ce tasa Mummy gaba tana faɗin" haba yaya meyasa baki yi tunanin abinda zaije ya dawo ba kika yanke wannan mummunar hukuncin? Yanzu kina ganin alhaki zai barki ki zauna lafiya? Kina ganin shikenan burin ki ya cika ko? Bayan kinsan Zuwaira da Saudat na raye, wallahi kinyi babban kuskure, kuma abinda hakuri bai baki ba rashin sa bazai ta6a baki ba"
Shuru Mummy tayi badon tayi nadamar abinda tayi ba, kawai shuru tayi saboda kudirin haɗa auran Saratu da Haseen,amma ba don haka ba mum Haseen Bata Isa ta sata gaba tana faɗa mata son ranta ba tunda ba uwarta bace.
Ganin haka yasa mun Haseen cigaba da cewa" ki san yanda zakiyi ki fidda kanki, dan wallahi babu hanuna cikin wannan abu, wannan meye inba son zuciya da zalunci ba? Ke yanzu ko da garwashi ne ya k'ona ki ya zakiji? Ballantana rai kacokan ki salwantar da bayin Allah wanda basu jiba basu gani ba kawai saboda son zuciya da kishin banza duk akan miji, to yanzu in mijin ya sake ki ya zakiyi?"
Da sauri Mummy ta mik'e ta bud'e k'ofar ta nuna wa mum Haseen sannan tace" tashi ki fita tun kafin nayi abinda baki tunani"
Cike da 6acin rai mum Haseen ta mik'e ta nufa hanyar fita, har ta kai bakin k'ofar ta juyo tace" zan tafi amma ki sani duk abinda yaje ya dawo karki nemeni"
Tana kaiwa nan ta fice ta nufa wajan su Mummy Zuwaira ta zauna.
Sai bayan la'asar Sameer suka shiga Abuja, tun kafin ya k'araso ya Kira Dr Abeed dake aiki a asibitin FMC ya sanar mishi da abinda ya faru.
Saboda haka suna isa asibitin ya wuce, an rigada an gama komai yana isowa aka d'auko gadon marasa lafiya aka d'aura Haseenah suka wuce da ita ciki.
Saida ya gama duk abinda zeyi sannan ya dawo ya ja motar ya nufa gida, har lokacin Mahmud bacci yake yi dan yana farkawa zai koma ya kwanta.
Suna isa Sameer ya d'aga hannu ya kwad'a wa Mahmud mari saida hular kanshi ta tuntsire, a firgice ya farka yana faɗin....
Plx vote nd drop ur comme
Advertisement
- In Serial25 Chapters
At Wit's End
Escaping his fate, a young man finds himself powerless in a world of wonder, where magic spills from every hand and demons make both men and monster. Follow Wit as he weaves his own epic. From making unlikely friends and unimaginable foes to being crushed by tragedy and finding the will to move forward, watch as he embarks on an adventure of mythical proportions. Sunday / Thursday @ 8pm Central Time The cover art is the work of a great digital artist named Amir Zand over on ArtStation.
8 294 - In Serial9 Chapters
Demonic Descent
Abandoned by the one you love and tortured by your love rival for months on end, can you maintain your faith in humanity and cling on to your hope for life or you will admit your faith and die to escape your suffering? Or will you choose revenge and begin your descent into demon hood, abandoning everything that made you human?Follow Kael Strider in his Demonic Descent into a world that governs the world we know. [trying for Moonquil]
8 142 - In Serial8 Chapters
A New Dynasty (One Piece)
Justice consists not in being neutral between right and wrong, but in finding out the right and upholding it, wherever found, against the wrong. Disclaimer: I do not own anything Madara
8 148 - In Serial75 Chapters
Water and Ice | Shoto Todoroki
⌜ Y/n is finally on her way to the school she's wanted to attend since she was a child. Surrounded by powerful classmates at UA, she's immediately thrown into the whirlwind of making friends, enemies, and training to become a hero. However, it's a little hard to focus when a red and white haired boy is constantly occupying your thoughts. 」__________➳ credit for bnha world components to kohei horikoshi➳ credit to original artists for pics at the top of chapters➳ loosely based on bnha timeline➳ some events and almost all interactions are stuff i come up with➳ slow burn even tho it looks rly fast at first lol__________➳ all rights reserved➳ not mature➳ rly cringe➳ completed➳ unedited
8 60 - In Serial12 Chapters
Successfully Demon Lord
Do you ever wonder, what is the next step for a demon lord after he conquers the world?Conquer another one, of course, the bigger one.Zaiden, a man from earth, died and reincarnated to a fantasy world and became the demon king, when he finally came back to earth he got transported to another fantasy world by God.This is the story of a demon lord that successfully conquer the world and ready for the next one.(This is my first fiction, so if you find anything wrong, please tell me so I can correct my self. Oh and I'm not a native English speaker so if I make a mistake, I'm truly sorry)
8 200 - In Serial30 Chapters
Alpha King's Human (completed)
I looked out of the window. The huge window had bars on it. It was designed in a way only I could see outside world. That's what I could only do. I could never live there. Why? There were two huge arms wrapped around me like chains as I stared at the window blankly. "Mate, I can still feel your dislike towards me. Tell me, what should I do to gain your affection. I'll do everything you say or buy anything for you. I love you, mate. Name it"I stared at his wolf eyes filled with love which made my heart churn. I pressed my urge to puke and stared blankly at him."Free me" "I told you. I'll never leave you. How dare you think about going away mate. I'll fuck you so hard that you won't be able to step out of the bed. Then you'll carry my pups. Let's see how you'll deny my love" He growled angrily. In a minute. I was lying under him naked... Again.---
8 178

