《HASEENAH》PAGE 35&36
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
*Dan Allah ina me bada hakuri na jina shiru da akayi na wasu 'yan kwanaki, hakan ya farune sakamakon rashin wuta da aka samu, na gode sosai da dakuwarku da kulawarku kaina, wa'yanda suke kirana da masu bina pc na gode sossai expecially meerah novels, I love u guyx much much Allah bar zumunci*
*35~36*
Wuta ne ya bi Haseenah sakamakon buɗe k'ofar da tayi, da sauri ta ja da baya haɗe da salati.
Haseenah na jin salatin Umman ta amma ba halin fita dalilin zafin wuta da hayak'in da ya cika d'akin, tun tana jiyo ummah har taji shuru.
Zubewa tayi wajan tana kuka tana faɗin " wayyo ummah na wayyo Aaman"
Tari ne ya turnuk'e Haseenah, kafin kace meye itama wuta ya mamaye d'akin ta.
Hakan yayi dai dai da dawowan Abba daga masallaci, Mummy na ganin shi ta daka tsalle ta hau kurma ihu tana birgima, ihun tane ya tada Saratu daga barci.
Da gudu ta fito dan ganin abinda ke faruwa, ganin wuta na tashi a side d'in Ummah ya sa Saratu ihu tana faɗin" Mummy Umman Haseenah a ciki"
Abba ko ganin wutan na dad'a tashi ya sashi fita da gudu dan neman d'auki.
Watsa ruwa ake da k'asa amma kamar fetur ake dad'a zuba wa.
Hakan yasa wani mak'wabcin su kiran fire service.
Mummy Zuwaira kuwa tunda tayi asuba ta kasa zaune ta kasa tsaye, haka haseen ma, shi mafarkin Haseenah yayi ta faɗa rijiya.
Hakan yasa shi kasa nutsuwa ya d'au makullin motar shi ya nufa gidan.
Isowar shi yayi dai dai da isowar Mummy Zuwaira.
Ganin mutane cike a gate d'in gidan ga motar fire service yasa Mummy Zuwaira firgice wa.
Haseen kuwa cike da tashin hankali ya fara ture mutane yana kutsawa ciki Mummy Zuwaira na bin shi a baya.
Ganin wuta na tashi wajan su Haseenah yasa Haseen rugawa da gudu ya nufa ciki.
Ganin ana ta shek'a ruwa ya sashi waigawa yana duba Ummah da Haseenah amma baiga kowa ba.
Mummy ya gani can gefe tayi zaman 'yan bori daga ita sai d'aurin k'irji kanta ko d'an kwali babu fuskanta sha6e sha6e da hawaye da majina tana ihu tana faɗin " wayyo Ni na shiga uku ku ceto rayuwar bayin Allan nan"
Advertisement
Nan Haseen ya fahimci abinda Mummy ke nufi.
Da gudu ya nufa wajan da nufin shiga nan aka rik'e shi, fisgewa yake yana faɗin" ku kyale Ni in shiga in fito da su tunda ku kun kasa ceton rayuwar su"
Rik'e shi sukayi suna faɗin ya nutsu amma ina baima san suna yi ba, ganin basu da niyan sake shi ya sa Haseen fashewa da kuka yayi zaman dirshan.
Mummy Zuwaira kuwa zare ido take tana faɗin" ina k'anwata take? A ina kuka barta? Ku matsa in fito da ita"
Abba ma firgici ya hana shi magana, zare ido kawai yake yana sharce zufa.
Da k'yar aka samu aka kashe wutan.
Ana kashewa kuwa aka 6alle k'ofar aka shiga.
Ummah dai babu ita babu alamar ta, cikin d'akunan aka shiga ana dubawa, d'akin Ummah ba kowa, nan suka wuce na Haseenah, can gefe suka ganta kwance ta gama k'onewa da ka ganta babu alamar rai a jikin ta.
Haseen kuwa yana ganinta ya kurma ihu ya yanki jiki ya fad'i.
D'akin Aaman kuwa ganin shi sukayi can gefe kwance, babu alamar k'una ko ciwo a jikin shi, sai dai baya numfashi.
Nan aka kira ambulance, ba tare da 6ata lokaci ba aka fito da Haseenah da Aaman.
Amma Ummah kam an duba ta ko ina babu ita babu dalili.
Mummy Zuwaira ce ta shigo ta fara dube dube, tana zuwa wajan corridor da Ummah tayi sallah taga shatin toka, tsugunawa Mummy Zuwaira tayi nan taga d'an kunnen Ummah sai zoben hanunta.
Hanunta ne ya fara rawa tana maimaita innalillahi wa inna ilaihir raji'un.
Zubewa tayi a wajan numfashin ta na fita da k'yar.
Jin tana salati cikin kuka yasasu garzaya wa dan ganin abinda ya faru.
Ganin abinda Mummy Zuwaira ta tsinta ba k'aramin firgita Abba yayi ba.
Fad'uwan shi kawai akaji nan aka fitar da shi.
Da gudu Mummy ta shigo tana faɗin" ta mutu ko? Halima ta mutu?"
D'agowa Mummy Zuwaira tayi cike da tuhuma ta dubi Mummy, ganin yanda take ya sa Mummy Zuwaira mik'ewa ta shak'o Mummy, turata tayi har bango ta d'auke Mummy da Mari sau uku, duban ta tayi cikin wata irin murya sannan tace
" Lauratu wallahi na rantse da Allah in na samu da hanunki wajan mutuwar er uwata sai na d'au fansa akan ki,kap zuriyar ku sai sun k'are".
Da k'yar aka k'waci Mummy hanun Mummy Zuwaira, kafin kace meye magana ya karad'e family.
Advertisement
Gida ya cika Mak'il ba masaka tsinke, banda sautin shesshek'ar kuka ba abinda kake ji.
Haseen kuwa allurar bacci aka mishi.
Mummy Zuwaira masu investigation ta d'auko Nan tasa aka kewaye side d'in Ummah ba shiga ba fita har sai an gama bincike.
Hankalin Mummy ba k'aramin tashi yayi ba dan tasan ba makawa za aga cylinder d'in gas d'in.
Da k'yar aka samu Aaman ya farfaɗo sakamakon hayak'in da ya shak'a ya mishi illa.
Haseenah kuwa dama likita ya sanar musu ta riga da ta rasu.
Lokacin da wannan labari ya iske su anga tashin hankali, barin Umaimah da baby, Suma Kan suma, ba abinda ya d'aga musu hankali sai in sun tuna jiya ma suna tare da ita.
Hakan ya jefa kowa cikin rud'ani da tashin hankali.
Abban Ummah kam jinin shi ya dad'a hawa.
Ummah kam ruwa aka yayyafa aka tattara tokan aka saka cikin likkafani.
Haseenah ma dawowa da ita akayi aka shiga da ita side d'in Abban ta, Nan aka mata wanka aka sutura ta.
Nan akace a shigo a mata addu'a.
Lokacin Haseen ma ya farfaɗo, k'arfin hali kawai yake, yaci kuka har ya gaji.
Shigowa shi gidan kenan daga asibiti, yana ganin kowa nata faman alwala zuciyar shi ta tsinke, nan ya tabbatar da ya rasa masoyiyar shi kenan har abada.
Tafe yake kaman wanda zai fad'i, yana shiga cikin gidan cikin kuka yaji Umaimah ta faɗa jikin shi tana faɗin" ya Haseen sun kashe mun Ummah da Haseenah na, Ya Haseen ko wanene yake da hannu karka barshi"
Kasa magana yayi dan kuka yaci k'arfin shi, zubewa yayi gaban Mummy Zuwaira cikin kuka yana faɗin" Mummy Kinga abunda sukamin ko? Kinga tozarci da wulak'ancin da akamun ko? Meyasa za'amun haka? Meyasa Ni basu kasheni ba? Meyasa....
Bai iya k'arasawa ba dan kuka yaci k'arfin shi.
Kama hanun shi kawai tayi tana girgiza mishi kai.
Nan ta mik'ar dashi ta duba su Umaimah tace" suje su mata addu'a za.a tafi da ita"
A tare suka shiga su hud'u, Haseen, Mummy Zuwaira, Umaimah da baby.
Ganinta shinfid'e cikin makara an gama shirya ta, ga tokan Ummah a gefe shima cikin likkafani.
Zubewa duka sukayi a wajan, baby kuwa tunda ta zube bata sake motsawa ba.
Addu'a kawai Haseen da Mummy Zuwaira keyi suna kuka, Umaimah kam ta kasa cewa komai sai rungume Haseenah da tayi tana wani irin kuka.
Bud'e gefen fuskan ta Haseen yayi, da sauri ya sake ganin irin k'onewan da tayi inba fad'a maka akayi ba bazaka gane Haseenah bace.
Kuka sossai yake ya dubi Mummy Zuwaira yace" dan Allah Mummy ki fad'a Mata ta tashi, wallahi zan aure ta a haka, Mummy ina sonta ki tashe ta dan Allah, inaso tamun magana ko da sau ɗaya ne"
Da ka ganshi kasan baya cikin hankalin shi.
Hakan yasa Mummy ta Kama hanunshi ta d'ago Umaimah suka kama hanyar fita.
Mummy Haseen ya hango tsaye bakin k'ofar ta, kallon da ya mata ya sata sunkuyar da kai k'asa alamar rashin gaskiya.
Saratu kuwa duk ta daburce saboda mutuwar tagirgiza ta.
Aaman kuwa na can asibiti ana mishi k'arin ruwa.
Lokacin da aka zo fita da gawar su ba k'aramin tashin hankali aka shiga ba, dan Mummy Zuwaira Suma tayi, haka baby Kam an rasa gane kanta.
Tunda suke basu taɓa shiga tashin hankali irin na yau ba.
Abba ma tafiya kawai yake kai kace mara hankali ne, janshi kawai ake duk yanda aka bi dashi nan yake bi, ji yake kaman ba shi ba, mafarki yake ko gaske sai Allah.
Seda akayi sallar su a masallacin juma'a ta anguwan sanna aka wuce dasu mak'abar ta, Haseen ma shuru kawai yayi amma idon shi bai dena zubar da hawaye ba.
A jere aka tona kabarin Ummah da Haseenah, tare da Haseen aka kama gawan da kanshi ya saka Haseenah.
Lokacin da aka gama rufe su kuwa Haseen durk'ushe wa yayi wajan yana kuka yana faɗin
" me yasa zakimun haka? meyasa Baki barni na fara mutuwa ba? me yasa kika za6i jefa rayuwata cikin garari da tashin hankali? Meyasa kinsan bazaki rayu tare da niba kika barni na shiga rayuwar ki? Meyasa baki bari munyi ban kwana ba kika tafi Haseenah? Why? Why?"
Kamashi daddy shi yayi cike da tausayin ɗan nashi ya rungume shi, cikin kuka Haseen ya k'ank'ame daddy shi yana faɗin" daddy kaga abinda rayuwa tamun ko? Kaga abunda mutuwa tamun ko? Kaga Haseenah ta tafi ta barni? Daddy fad'amun ya zanyi? Ka tashe ta dan Allah kace mata zan aure ta a haka, daddy ka fad'a mata ina sonta a haka daddy...
Toshe mishi Baki daddy yayi yana faɗin" haba Haseen kar ka zama mara tawakkali mana, ka rungumi k'addara sai Allah ya musanya maka da wata"
Da sauri ya dubi daddy yace....
Na gaji wlhy....
Plx vote nd comments
Advertisement
- In Serial13 Chapters
Celestial Void
After a year of being unable to play the newest virtual reality space game, Cam is finally able to log in. He is behind everyone else, but his friend, Will invites him along on a mission for his guild to help him get started. Soon he will push his limits of how fast he can progress to help his friends. He will have to to navigate his way through the enormous, open universe filled with all sorts of space ships, combat, politics and crafting. The universe called Celestial Void.
8 101 - In Serial13 Chapters
Slime migration
Kip was an ordinary teenage boy going on his final, year 11, camping trip, until the world changed into that of an RPG game. He couldn't even get a simple skill like 'identification', this new world make it extremely hard for him to even kill a simple slime. With his friends dying left and right, what will happened to the humanity we knows as. Will Kip remain the same person he always was, or will he changed into something else? Hey guys, thank you for checking out my work. I've read so many novels on this site and it inspired me to write my own story. I've been studying English for about 2 years now and thought this would be a good opportunity to increase my writing skill at the same time. I am currently studying my degree at a University so I'll continue to edit and write more chapter whenever it's convenient for me to do so (which is like, all the times haha). My first work can turn out to be a bit crude, but I hope you guys will be patient and allow little small slime to grow. Thanks!!!
8 215 - In Serial25 Chapters
Transported To A Different World While In A VR Game?
Akira Kageyama, a perfectly ordinary boy with a perfectly ordinary life.Well, if you count being bullied nearly every day normal that is.From the anguish of the peer pressure he received continuously, his personality became distorted. Twisted into someone who wanted nothing to do with real life.Yes, his true life now is in a fantasy world.Meet Fantasma Online, a popular VRMMORPG set in a classic medieval era world, complete with humans warring against the Demon Lord.Now, you might be thinking, """"Well, that sounds pretty generic"""". If you do, then you can't be more wrong in your assessment.For you see, the main selling point of this game is not the visible conflict between the two races, but the stealth race between the two of them to discover the long lost civilization of Fantasma.Yes, the whole game is about that grand mystery, Players are encouraged to solve the many puzzles in the game world to gain prestige and treasure.And Akira was one of them.Indeed, after giving up on real life Akira went full on out into playing the game. He had always been obsessed with solving any puzzles he found since he was a kid, so he refused to let any puzzle in the game unsolved.And thus, he became the strongest player in the game. Not just from his character level but from the legendary Fantasma equipment he had. He owned the Pure Obsidian sword, the sword with the highest attack in the game, far surpassing any other swords. And he was the sole owner of that sword, as a reward for unearthing the Reversed Garden, one of the major Fantasma ruins of the world.However, one day, just as he thought he was about to solve what he thought was the last puzzle of another major Fantasma ruin, a blinding light suddenly enveloped him. And when he could open his eyes again, he was standing in a familiar place. It was the castle where every new player spawned.But wait, how was it that the NPC king and princess now are able to talk freely, unlike the usual fixed responses they only have? And his logout button is now gone?Could it be? Did the game just become reality?
8 252 - In Serial252 Chapters
The Faceless Minion
In a world of superheroes, the great mastermind behind it all is...that faceless minion over there?! Enter into a world of superheroes...and supervillains. A world of chaos and action, of battle and glory, of plots and danger. Watch as heroes rise, villains fall, and the normal people strive to live their lives in between. But... Behind it all... Deep within the shadows... There is one who stands above all others. A master manipulator. The one who holds the fate of nations in his hands. The one who plays with the course of history as he pleases. Neither hero nor villain can withstand him. No one can put a stop to his plans. His name is... ... Um, what was his name again? ... What do you mean we don't know the name?! Why didn't you tell me?! What do you mean I never asked?! Go find out what his name is, you stupid minion! I shouldn't assume he's a he if I don't know who he is? I don't care, you useless twap! Just get me a name! Don't you know we're live now!? ... Gah, now this intro is ruined. All because of that stupid faceless minion. An expansion of my response to https://www.reddit.com/r/WritingPrompts/comments/tokpk6/wp_you_are_the_worlds_most_successful/ [participant in the Royal Road Writathon challenge] And finisher!
8 1048 - In Serial70 Chapters
7FATES: CHAKHO
New parts every week on Fridays at 10PM ET*****It's the day of visitors.But the visitors to Sin-si are unwelcomed, vengeful beom.Unforgotten animosity fills the air and rage collides, soaking the ground with blood. Seven boys take up their weapons to end this fight, once and for all.7FATES: CHAKHO with BTS*****Content advisory: this story contains some violenceOriginal story: HYBECo-planning: HYBE / NAVER WEBTOON
8 72 - In Serial20 Chapters
A mangled love a foxy x mangle love story
Foxy gets moved to the second location. Foxy hates everyone. But when he meant a girl named mangle who is also a pirate. Everything changed. Drama drama XD
8 218

