《HASEENAH》PAGE 33&34
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
*33~34*
Ganin Yana k'ok'arin Mata mummunan fahimta yasa Haseenah cewa" shikenan kayi abunda ya Dace"
Dad'i ne ya Kama Haseen lokaci d'aya ya mayar da jikin shi ya kwantar Kan kujerar ya lumshe Ido, hango su kawai yake yanda suke tafiyar da rayuwar auran su.
D'agowa yayi ya dube ta sannan yace" yanzu wajan Abba Zan aika ko wajan yayan Abba?"
Sunkuyar da Kai tayi sannan tace" ka samu Mummy Zuwaira ita zata sanar dakai"
Farin ciki ne ya dad'a rufe shi, Dan ji yake kaman ya rufe Ido ya bud'e ya ganshi gaban Mummy Zuwaira.
Bayan sun gama komai Haseen ya biya bill d'in sannan ya sake musu take away suka mik'e, motar shi ya shiga yace su Umaimah da baby su shiga ya mayar dasu gida Dan Kar su wahalar mishi da Mata.
Dariya suka sa Banda Haseenah da ta tura Baki Dan ba hakan ta so ba, Amma ba yanda zatayi Haka ta shige ita da Aaman suka d'au hanyar gida.
Yana Isa gidan ya shige ciki, Mummy Zuwaira ya hango zaune a palour ita kad'ai tana Shan fruits.
Zama yayi gaban ta shima ya d'au toothpick ya fara Sha, bayan sun gama ne Nan ya sanar da Mummy abunda ke tafe dashi.
Sossai taji dad'in Haka Nan ta Kira Mummy Saudat ta sanar Mata da abunda ke faruwa, itama farin ciki ne fal zuciyar ta, duk da tasan mahaifiyar shi batada hali Amma shi ya fita daban a cikin su.
Dan Haka tace wajan yayan su zai turo Kuma zata sanar mishi, Nan take tanbaya yaushe zasu turo yace Nan da kwana biyu.
Bai wani dad'e ba ya Kama hanyar gida, baiyi wata wata ba ya sanar da daddy shi, shima ya amince saboda ya yaba da hankalin Haseenah.
Mum d'inshi ce kawai da farko ta k'i yarda saboda tsoron Mummy, Amma daddy Haseen yace shi ba ruwan shi da wata Lauratu, abunda d'an shi yake so shi zai mishi tunda shi kad'ai yake da shi a duniyar Nan.
Ba Dan mum ta so ba Haka ta yarda, Amma tasan ba makawa cin mutunci na Nan zuwa.
Da daddare Haseen ya shirya ya nufa wajan masoyiyar shi wato Haseenah, lokacin itama ta shirya cikin Riga da skirt na Atampa, ba k'aramin kyau tayi ba, a palour ta mishi masauki, Nan ta cika mishi snacks da exotic juice da ta had'a wa Ummah.
Seda ya gaida Ummah sannan ya rik'o hanun Aaman suka dawo palour, ba.a jima ba Haseenah ta shigo hanun ta d'auke da warmer Wanda ta dafa jealouf na couscous, Wanda yaji kayan had'i, zuba mishi tayi Nan ya fara ci, seda ya k'oshi sossai sannan ya dube ta yace" swtlov kamar dama kinsan banci komai ba"
Advertisement
Dariya kawai tayi ba tare da tace komai ba, Nan suka Fara hirar su, ita dai kunya ta Hana ta sake wa daga tace " umm ko Kuma tace a'a"
Amsar da take bashi kenan, duban ta yayi sannan yace" nidai Nanda wasu kwanaki duk wannan kunyar zata kau, Dan Nanda kwana d'aya Zan Kai kud'in aure"
Kunya ne ya kamata hakan ya sata sunkuyar da kanta.
Ganin batada niyar magana 'yan miskilan cinta sun motsa ya sashi wucewa wajan Ummah suka cigaba da hirar su.
Wajan k'arfe goma ya fito zai tafi, Nan suka had'u da Mummy ta fito kitchen, ganin kallon da take mishi ya sashi kau da Kai gefe ya nufa hanyar fita, kallon shi Mummy tayi shek'ek'e tace" ayi dai mugani, kwartan ci ya wuce waje har sai an shigo cikin gida, da kwana kayi ai inaga zaka fi samun abunda kake so"
Yau Haseen Yana cikin farin ciki, Dan Haka bashi da lokacin tsayawa mayar Mata da dogon magana, dubanta yayi yace" karki manta kallon uwa nake Miki, karki Bari in rufe ido inyi abunda Bai Dace ba"
Yana gama fad'in Haka ya sa Kai ya fice.
Ran mummy ya 6aci matuk'a, hakan ya sata bin shi da ashar Amma ko juyowa Bai yi ba.
Yau da misalin k'arfe 8 na dare yayun daddy Haseen suka Kai goron gaisuwa da kud'in auran Haseenah naira dubu d'ari.
Murna wajan Haseen ba'a magana Dan shi ji yake kaman ya mallaki Haseenah an gama.
Da daddare Abba ya shigo hanun shi d'auke da goro da carton na sweet da sauran tarkacen gaisuwa.
A palour ya tarar da Mummy da Saratu na zaune, mummy na ganin shi ta hau wangale Baki, waje ya nema ya zauna sannan ya tura Mata kayan gaban ta.
Janyo wa tayi ta dube shi fuska a sake tace" Abban su Dan kaga kwana biyu inacin goro shine zaka siyomin da yawa Haka?"
Kau da Kai yayi gaban shi na fad'uwa yace
" a.a na tanbayar auran 'yar ki ce aka had'o da sadaki"
Washe Baki Mummy ta Fara ta dubi Saratu tace" ke wanene kuka sasan ta Kuma Baki fad'amun in Fara shiri ba gashi har an kawo gaisuwa da sadaki"
Cikin rashin fahimta Saratu ta yamutsa fuska tace" Mummy Ni kuma?"
Ganin suna son cika mishi kunne yasa Abba cewa" ba fa ita nake nufi ba, Haseenah nake nufi, itace Haseen d'an wajan k'anwar ki ya tura da kud'in aure"
Tun kafin ya Kai aya Mummy ta zabura ta mik'e, k'afa ta saka tayi patali da goro da mintin, Nan ya watse a palour, girgiza Mummy ta hau yi tana fad'in
" Ni za.a mayar k'aramar yarinya aci Amana ta? Ni za'a tozarta a garin Nan, har za.a had'a Baki da 'yar uwata aci Amana ta? Wallahi indai Ina raye kasa a ranka ba'a ta6a maganan auran Nan ba"
Advertisement
Mik'ewa Abba yayi ya wuce ciki.
Saratu kuwa kuka ta saka Dan Nan duniya ta mace Kan Haseen, sonshi take kamar ranta, itama Mummy ganin akwai 'yan chanji a hanun Haseen ya sa take da kudirin tana gama kau da su Ummah zata tursasa wa k'anwar ta lallai ta sa Haseen Auran Saratu, sai gashi ba zato ba tsammani ana k'ok'arin haramta Haka.
Birgima Saratu keyi tana fad'in" Mummy Dan Allah karki Bari ya aure ta, wallahi sonshi nake Kuma Dani yafi dacewa, Mummy in ban aure shi ba mutuwa zanyi"
Bige Mata Baki Mummy tayi tace" Dan ubanki Dena cewa Zaki mutu wallahi su zasu mutu ba ke ba, in dai Ina raye daga yau wannan magana ya Zama tarihi"
Ummah dai dake cikin d'aki tana jiyo hayaniya, amma Sam batasan abunda ke faruwa ba, saboda itama Haka kawai taji gaban ta na fad'uwa ga wani irin bugawan da zuciyan ta keyi.
Hakan ya sata Kiran Haseenah daka d'akin ta ita da Aaman tana mishi wasa.
Fitowa tayi da sauri ta zauna gaban Ummah tace gani" k'ura Mata Ido Ummah tayi na wasu mintina sannan ta umarce ta ta d'auko Mata Aaman.
Ba musu ta d'auko shi, mik'a hannu tayi ta kar6e shi ta rungume shi jikinta, sai hawaye, hakan yasa Haseenah fashewa da kuka itama ta rungume Ummah, cikin kuka Haseenah ta Fara cewa" Ummah na ki fad'amun me yake faruwa, Mai yasa ki kuka?"
Shuru ba amsa sai kuka, gashi ta rungume su kaman zata mayar dasu cikin ta, sai saukar ajiyar zuciyar ta kawai kake ji, hakan ya dad'a d'aga hankalin Haseenah.
Sun kai kusan minti talatin a Haka sannan Ummah ta sassauta rik'on da ta musu, Kama hanun Haseenah tayi ta saka cikin na Aaman ta matse, sannan ta dubeta cikin hawaye tace
" Haseenah ko bana Raye ga amanar ki da na Aaman na damk'a a hanunki da Kuma Wanda ya halicceku, ki kare mutuncinki ki rik'e kanki da k'anin ki, karki yarda ki maimaita irin rayuwar da kikayi a baya, ki kasance Mai 'yan ci da girmama na gaba da ke, ki kasance me biyayya da Kuma hak'uri Kan duk wata rayuwar da Kika samu kanki a ciki, daga k'arshe inason Koda bayan Raina a kullum kikasance kina tunawa Dani, ki kasance Mai yimun addu'a da neman gafarar ubangiji, ki Kuma ji tsoron Allah, ki bawa k'aninki irin tarbiyar Dana Baki, inda hali mafi da wannan"
Tana kaiwa Nan kuka ya k'wace Mata, Haseenah ma kukan take, ganin Haka yasa Aaman fashewa da kuka shima.
Sulalewa Haseenah tayi ta Kira Mummy Zuwaira a waya ta sanar Mata ga Umma nata kuka.
Nan tasa aka bawa Umma waya, tamata tanbayar duniya Umma tace ba komai, hakan yasa tayi Mata nasiha har sunyi sallama sai Ummah tace" Yaya ga amanar Haseenah da Aaman na bar miki, Koda bana Raye ki kula mun da tarbiyar su.
Tana kaiwa Nan ta katse wayar gaba d'aya.
Hankalin Mummy Zuwaira ba k'aramin tashi yayi ba, gashi k'arfe kusan Sha d'aya na dare ne ba zata iya driving ba, Kuma daddy su Umaimah baya gari.
Haka ta kwanta tunani fal zuciyar ta, Allah Allah take asuba tayi ta nufa gidan Ummah.
Nan ko Umma na rungume da Aaman har yayi bacci a hanun ta, ita Kuma ta k'ura mishi Ido tana sharar hawaye, Haseenah ma zaune take a gefen Ummah ita ma kukan take, ganin k'arfe d'aya ya yi yasa Ummah duban Haseenah tace" ki tashi ki je ki kwantar da Aaman, kema ki kwanta Nima baccin nake ji"
Ba musu Haseenah ta d'auke shi ta kaishi d'akin shi ta tofa mishi addu'a sannan ta koma d'akin ta jikinta a sanyaye ta ja bargo ta kwanta.
Ummah ma mik'ewa tayi harta shiga d'akin ta sai Kuma ta fito, wajan Aaman ta sake komawa ta zuba mishi Ido sannan ta fito ta lek'a Haseenah ma, takai kusan minti biyar Nan tsaye ganin Haseenah na k'ok'arin juyowa ta bar wajan da sauri.
Alwala Ummah ta Fara yi ta hau sallah , tana yi tana kuka, tun tana yi a tsaye har ta zauna.
Nan bacci ya d'auke ta Kan sallayar.
Ana Kiran sallan asuba ta mik'e taje ta d'auro alwala ta dawo ta tada sallah Dan Bata tashi Haseenah ba Dan wani lokacin ma Haseenah na rigata tashi.
Abunda bata sani ba shine yau Haseenah ta makara.
Tana zaune Kan sallaya tana addu'o I, bud'e k'ofar su taji anyi an gangaro da Abu Mai Kama da k'arfe, kafin tayi yunk'urin juya wa an cillo ashana.
Warin gas Ummah ta Fara ji mik'ewar da zatayi kuwa Nan gas d'in yayi bindiga, kafin kace meye wuta ya Kama ko Ina.
Salatin Ummah shiya tada Haseenah daga barci, da sauri ta duro Dan ganin abunda ke faruwa.
Bud'e k'ofar da zatayi kuwa kaman jira ake wuta ya Kama d'akin Haseenah....
*Innalillahi wa inna ilaihir rajiun*
Hope u enjoyed d page, plx vote nd drop ur comments. 😍😘❤
Advertisement
- In Serial29 Chapters
Cultivating Earth [Hiatus]
[This fiction is on indefinite hiatus. I'm currently acting as a 24-hour caregiver for my step-father who had a massive heart attack. I apologize for disappearing so quickly, but sometimes that's just life. I'll return as soon as possible. Sorry everyone!] Zhao Gang, after hundreds of thousands of years cultivating, has finally reached the penultimate threshold. He is ready to ascend to the level of True Immortal. Driven by the need for a place his enemies won't find him, Zhao Gang puts together an audacious plan. He has developed a revolutionary new formation which will allow him to ascend while on even the lowest planes. To avoid drawing attention, he has to choose a plane that is relatively desolate, however. He chooses Earth. Fast forward three thousand years. Zhao Gang discovers what his work has wrought - a cultivation-free culture that has delved the deep mysteries of creation - he can't help but think how this tiny little planet devoid of natural energy could affect the course of all creation. There's only one problem. For that to happen, he has to succeed in cultivating Earth. Notes: Chinese names should be ignored in the social context - they don't mean anything. Sorry for slaughtering such a beautiful tradition. This novel starts off slower than most. If the slow-roll isn't your thing, you might want to give this a pass. If it's not for you, I understand. Also, releases may be broken up into smaller chunks. The goal is 5k words, but definitely more than 4k. If you see a short release, be aware that more is probably coming. I'll be honest and say that I'm struggling with each new scene, if only because I want to balance the scope of vision with good pacing. I hope the work I put into it is worthwhile.
8 80 - In Serial362 Chapters
Don't Feed The Dark
Something malevolent has awoken in Northeast Ohio. Former acquaintances, neighbors, loved ones-all at random-transform into flesh-craving monsters hell bent on devouring the living. Corpses are rising from their places of unrest. Nocturnal animal-man hybrids hunt in packs. The dead are awakening from within the living… By morning, the sun weeps over streets splattered blood-red as an unsettling silence soon follows, lulling the broken remains of society into believing the blood bath is over. Survivors gather to lick their wounds and salvage what is left of their ravaged lives as local governments struggle to maintain law and order. As a second wave approaches, a handful of survivors from all walks of life must put aside their differences and band together to escape the pending slaughter while storm clouds begin to gather from within their fragile community. Some who were once respectable in the eyes of society will devolve into madness while the despicable rise to the occasion in a world no longer respecting of persons. It is their world now. The dead are hungry and do not discriminate. ~~~ Don't Feed The Dark had officially ended. For further details refer to the last post in the series. Please vote for Don't Feed The Dark at topwebfiction to show your support and help more readers discover this series. Thank you in advance. ~~~
8 254 - In Serial15 Chapters
The Solipsist
Every novel needs a main character, and in this case, it's a young man named Jacob Bates. Jacob is your average guy who likes books, television, and long walks on the beach. One day, Jacob was diagnosed with a condition that made his body frail and weak. This drove Jacob to focus solely on his studies, ending up becoming a fairly capable guy, despite his condition. The road ahead was looking great! That's when a little scene occurred between Jacob's girlfriend and one of his male classmates. Jacob's mood was a little lower than dirt from thereon. His motivation to pursue his studies, gone. This event caused Jacob to fall into the death grip that is a job in retail. One day, while Jacob was mopping the cold floors of the grocery store he worked in, a strange blue screen appeared in front of him, notifying him that the world was going through a change. Now if this change was a good or bad thing, he didn't know. But there was one thing Jacob knew for certain. He didn't have to mop the floors anymore. Author's Note: (This is my first story, and I would be very thankful if grammatical errors were pointed out. I could also take a few suggestions in the comments if you would. This is less a planned production, and more a little project that I'm winging as it goes. I will try and be consistent with at least 2 chapters a week. Also, as I am a completely new author, the number of words per chapter may fluctuate. The minimum will be around 1000 words, while other chapters may be 2000-3000. It will hopefully only get better with time.)
8 120 - In Serial24 Chapters
Pokemon Castaway
A failed league challenger retires to live his days out in relative quiet until a lie and a storm lead him back to Unova to embark on a new journey.
8 165 - In Serial47 Chapters
Welcome To Demon School! Nagisa-kun
What if Iruma got replaced with Nagisa? What if Nagisa was half demon? What if Nagisa' father was Sullivan's biological child making Nagisa his biological grandchild? What would be the story if the silent androgynous assassin was to go to babyls?Find out in "Welcome to demon school! Nagisa-kun"I dont own Assassination classroom and Welcome to demin school! Iruma-kun or any of the images used.
8 456 - In Serial6 Chapters
Submissão Feminina
Nesses textos,pretendo introduzir minha concepção da submissão feminina ,suas características comportamentais e sua importância para o estado psicológico sadio de uma mulher sobre a perspectiva evolutiva.Sou um defensor da submissão feminina por parte de um homem na posição dominante,este tema é frequentemente abordado por diversas bases de conhecimento,mas muitos não a compreendem da forma devida e sua real importância.Entendo que cada base de conhecimento(pelo menos as que eu estudei,BDSM cristianismo e islamismo) que tem esta temática possui conhecimentos que podem ser combinados para o melhor aproveitamento da energia sexual e conjugal da fêmea submissa.Não uso de dogmatismos para enxergar a realidade.
8 106

