《HASEENAH》PAGE 27&28
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
'''Dan Allah masu mun magana ta pc in tura musu novel dina suyi hakuri suna tanbaya a group, ina da matsalar network daga lokacin da nace kowa xan bishi in tura mishi in personal network dina yakan dad'e bai dawo dai dai ba, kuyi hakuri plx'''
*27~28*
Da gudu Saratu ta fito jin irin Kiran da Mummy ke Mata, duban ta tayi sannan tace" Ina wannan matsiyaciyar take?"
Ta nuna k'ofar d'akin su Haseenah.
Ta6e Baki Saratu tayi tace" na dai ga Haseenah ita da Yar Uwarta sun kamo Uwar an fita da ita da sauri, ban dai San menene ba"
Wani shewa Mummy ta saki tana fad'in" Haka akeso, Allah yasa tafiyar kenan"
Nan ta wuce ciki zuciyar ta fari tas, gani take yanzu Kap duniya Bata da wata damuwa, gida ya Zama nata, miji ya Zama nata Haka dukiyar shi ma daga ita sai 'yar ta.
Haka yau Mummy da kanta ta shiga kitchen ta zuba girki, tana gamawa ta fito musu dashi palour suka baje sai Kwasa suke suna Hira ita da Mum Haseen.
Can asibiti kuwa sai son barka ake, Hajiya Saudatu ne ta je har kasuwa ta tasa Abba a gaba suka shiga suka siya kayan abinci, da akwati gudu hud'u, da kanta ta shiga shagon Abba ta had'a kayan Umma akwati guda, sannan suka je baby care aka cika akwati biyu tam da kayan baby, d'ayan Kuma aka cikeshi da kayan shafe shafe sannan tace su taho asibiti.
Shi dai Abba ya rasa Gane kanshi, farin ciki yake ko bak'in ciki oho, Amma kana kallon shi kasan akwai abunda ke damun shi.
Advertisement
Haka suka k'arasa asibitin lokacin har Umma ta tashi, dangi duk sun zagaye ta, dad'i ne ya Kama Umma Dan rabon da taga dangi an taru a kanta tun auran ta.
Tunani take to dama me yasa suka guje ta? Wata zuciyar tace mata halin Mummy.
Abba ma da yazo yaga jaririn shi d'aukan shi kawai yayi ya zuba ma yaron Ido, can sai ya share k'walla, Mummy Saudat ta kula da hakan, duk yanda akayi tasan d'an uwanta Yana cikin wani mawuyacin hali, addu'a kawai yake buk'ata, Dan tasan ba Haka yake ba.
Ganin jikin Umma ya koma normal yasa Mummy Zuwaira ta buk'aci sallama, Haseen ne ya biya duka bill d'in sannan aka kwashi Kaya sai gida, Abba kuwa da sunan Abban Ummah yayi wa yaro hud'uba wato *Abdullahi*, Haseenah tace za.ana kiranshi (Aaman).
Dangin Ummah kuwa murna kaman ba gobe, Nan aka Kira Abban Ummah aka sanar dashi, Nan yace ga tukwicinshi Yana isowa.
Motoci biyar akayi duk 'yan raka Ummah gida ne.
Mummy da Mum Haseen da Kuma Saratu na tsaka da Hira sukaji horn d'in mota, kallon kallo suka Fara yi, can Mummy tayi tsuka tace" Abban su ne fa"
Jin motar ba guda d'aya bane ya sasu duka yin shuru Dan sauraron abunda ke faruwa.
Kafin su yunk'ura su tashi sukaji Muryar Mummy Saudat tana rangad'a gud'a, mutuwar zaune dukansu sukayi, Mummy Zuwaira ce ta Fara shigowa rik'e da Aaman a hanunta an nad'e shi cikin showel farare tas, sai Ummah dake biye da su, sai Kuma jama'ar da suka rufa musu baya anata San barka.
Ko kallon inda Mummy take Basu Yi ba, palour Ummah suka wuce, Nan aka Fara shigowa da akwatuna Wanda Abba ya siya, Nan fa hankalin Mummy ya tashi.
Haseen ne shigowan k'arshe rik'e da basket sun jero tare da Haseenah gwanin sha'awa.
Advertisement
Wani zagi Mummy ta kutuntuma, lokaci d'aya tayi zubur ta mik'e ta fisge d'an kwali, Nan ta hau surfa masifa da zagi tana fad'in
"ba.a Isa a munafurce ta aci amanar ta ba, anje anyo ciki sannan za.a lank'aya wa mijin ta saboda anga yanada dukiya"
D'aya daga cikin 'yan uwan Umma ta lek'o tace" sai gashi kuwa aka haifo namiji Kuma ba"
Ihu Mummy ta sake tana fisge fisge, ganin zaninta na Shirin fad'uwa yasa Mum Haseen janta da k'yar sukayi ciki, tana tirjewa tana komai suka ja ta ita da Saratu suka turata d'aki suka kulle ta.
Dukda Haka bakin Mummy Bai mutu ba fad'i take" in dai da jini aka haifeta wallahi saita hallaka Ummah da d'an data Haifa.
Bata gama tsinkewa da Al amarin ba seda taji ana sake wani gud'an ganin galleliyar motar da Abban Ummah ya siya Mata, lek'awa Mummy tayi ta window Nan ta hango motar ko gama cire ledar jiki ba'a Yi ba, zaman dirshan Mummy tayi Kan tiles ta fashe da kukan bak'in ciki, ganin duk dangin shi sun cika wajan Mummy, gashi ta jiyo yanda ake ta yaba kayan akwati Wai Abba ne yayi Mata.
Kan uba, wallahi bazata yarda ba, ita za.a ciwa Amana, wannan karon ta d'au alwashi ko ta tsiya ko ta arzik'i ba bokan da zataje da kanta zata d'au mataki.
Ganinta kawai suke.
Kuka Tasha bana wasa ba, seda tayi Mai isarta sannan ta koma ajiyar zuciya.
Jin tayi shuru yasa Mum Haseen bud'e k'ofar ta shiga a hankali, Mummy ta hango gashin kanta a tsatstsaye sai kace mahaukaciya, Nan Mum Haseen ta Fara kwantar Mata da hankali, ta Bata shawara ta tashi su koma wajan boka.
Wani ashar d'in da Mummy ta k'unduma Mata ya sata Jan bakin ta tayi shuru, Mummy ta kalleta tace" ba wajan d'an iskan da Zan Kuma zuwa, da kaina da Kuma hanuna Zan d'au mataki"
Girgiza Kai Mum Haseen ta Fara yi tace" Yaya in hankali ya 6ata hankali ke Nemo shi, karkije ki aikata abunda zakiyi Dana sani daga baya, Haka Allah ya nufa ki d'au kaddara sai kiga Allah ya sauya Miki da mafi Alheri"
Tunda Mum Haseen ta Fara magana Mummy ta zuba Mata Ido take kallon ta Kai kace maganar ya shigeta ne, seda Mum Haseen ta yi shuru sannan Mummy ta dube ta tace " kin gama Dan ubanki? Munafuka kawai, dama nasan da saninki aka ci Amana ta, shiyasa naga Haseen bini bini Yana bin Mata kin kasa tsawatar mishi, ba ruwanki da damuwa ta dama nasan ba don Allah kike k'aunata ba, ki tashi ki ficemun a gida karna sake ganinki inba nice na nemeki ba"
Maganganun Mummy ya ta6a wa Mum Haseen zuciya, hakan ya sata mik'ewa ta d'au jakan ta ta fice a wajan, Haseen ta gani ya fito Nan tace ya ajiye ta a gida.
Tun da Mummy ta haihu kullum gidan shiga ake ana fita, Mummy kuwa ko fitowa Bata yi duk ta rame tayi bak'i ta fita a hayyacin ta, ta sak'a wannan ta kunce wannan duk ta rasa abin Yi.
Da Haka har yau akazo shagalin suna.
For comments 08144932303
Advertisement
- In Serial10 Chapters
When It Rains, It Pours
A train of thought compendium.I have them every now and then. Or to be more accurate, they have me. One offs. Shorts. Tales. Parables. Fables. And other weird things. This line has no schedule. No track number. No set destination. Sometimes it's an El. At other times, a space shuttle, taxi, caravan or fast moving treadmill. And every now and then it's a subway passing through underground caverns, littered with cobwebs. These sporadic ideas pop into my head at the weirdest of times. Some end in the middle. Some end with a fizzle. Some end with a bang.
8 186 - In Serial15 Chapters
One Eyed Wanderer
Saito Ushiba an average 17 years old High schooler decides to play a newly released virtual reality game developed by vision, the leading gaming company introduces "Grand Quest Online" changing the future of gaming, Saito ushiba joins Grand Quest Online on its first day of release as an unnamed player due to a glitch, whilst playing he goes through a series of events which turns the Saito ushiba into a living legend within the game and outside of the game. Note: Warning the description might be misleading Also, the Novel will not be too long, although I'm not sure how many chapters it will take for me to finish the story I am sure it will not exceed 150 chapters. Just wanted to let you know since I don't plan on writing long novels due to my preference.
8 338 - In Serial35 Chapters
Moonrise Over the Sky Cities
Living in his sister's mansion in the wealthy West District of Olympus-3, a Sky City, Sander wallows away his days in self-pity, disregarding the grim Earth of 2201 - which has suffered warring mage factions and devastation by monsters from the Chaos Realm.Five years have passed since his daughter died under mysterious circumstances, something he could neither solve, nor get his mind off to the present day. Everything changes, however, when he meets Scarlett - a Lunar Knight who whisks him away from his gloomy life after he discovers that she is battling the Chaos…
8 178 - In Serial31 Chapters
Descend
Elise Ellsworth awakens in Rambling University in the fall of 1954, her memories as shattered as her legs. She has suffered an accident, one which mirrored the allegedly accidental death of another student the term before. Authorities both of the campus and the nearby town deny any connection. Elise and the rest of the staff of the school’s newspaper take it upon themselves to solve the case — a case that is nearly ruined when Tarian Marek, a junior with a mysterious agenda, catches her trying to steal a dead student’s records. Surprisingly, he promises to help her. But making new allies is a dangerous game when anyone could be a killer … and anyone can be, when everyone in town has superpowers. [Now updated on the 2nd Tuesday of every month.]
8 118 - In Serial6 Chapters
Scar of Ifrit
Ifrit was once a world known for its magic and wonder, the fantastical beasts who inhabited its bountiful lands. That was before the people of Ifrit, understood how to harness the world's power. Though they could use the magic, they didn't yet know about the terrible effects magic casting would have on Ifrit. At the height of their power, everything came crashing down around them. A giant chasm opened up, splitting the planet in two. Daki was there when it happened. At an age too young to be alone, he was separated from his brother and the man who had rescued them both. Now it is up to him to find a way to reach the other side in order to meet up with them. He must find a way over, even if that means climbing down into the monster infested abyss.
8 69 - In Serial24 Chapters
I Want To Enjoy A Country Life!
⚠️𝐒𝐓𝐎𝐑𝐘 𝐍𝐎𝐓 𝐌𝐈𝐍𝐄⚠️~for offline purposes only~𝐀𝐮𝐭𝐡𝐨𝐫: Botamochi ぼた餅𝐓𝐫𝐚𝐧𝐬𝐥𝐚𝐭𝐨𝐫𝐬:Okubyou Desu and Wisteria TranslationsDescription:The protagonist - Kingdom's second son Aine - who is involved in an inheritance struggle with his two brothers, recalls the memories of his previous life in Japan where he lead an ordinary life. Aine loses his desire to fight for the inheritance and wishes to enjoy a country life, and that sort of Aine captivated his older brother and little brother.This is a story of hate that later turned into love...P/s: Story and Translations aren't mine, all credits goes to the author and translator
8 370

