《HASEENAH》PAGE 27&28
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
'''Dan Allah masu mun magana ta pc in tura musu novel dina suyi hakuri suna tanbaya a group, ina da matsalar network daga lokacin da nace kowa xan bishi in tura mishi in personal network dina yakan dad'e bai dawo dai dai ba, kuyi hakuri plx'''
*27~28*
Da gudu Saratu ta fito jin irin Kiran da Mummy ke Mata, duban ta tayi sannan tace" Ina wannan matsiyaciyar take?"
Ta nuna k'ofar d'akin su Haseenah.
Ta6e Baki Saratu tayi tace" na dai ga Haseenah ita da Yar Uwarta sun kamo Uwar an fita da ita da sauri, ban dai San menene ba"
Wani shewa Mummy ta saki tana fad'in" Haka akeso, Allah yasa tafiyar kenan"
Nan ta wuce ciki zuciyar ta fari tas, gani take yanzu Kap duniya Bata da wata damuwa, gida ya Zama nata, miji ya Zama nata Haka dukiyar shi ma daga ita sai 'yar ta.
Haka yau Mummy da kanta ta shiga kitchen ta zuba girki, tana gamawa ta fito musu dashi palour suka baje sai Kwasa suke suna Hira ita da Mum Haseen.
Can asibiti kuwa sai son barka ake, Hajiya Saudatu ne ta je har kasuwa ta tasa Abba a gaba suka shiga suka siya kayan abinci, da akwati gudu hud'u, da kanta ta shiga shagon Abba ta had'a kayan Umma akwati guda, sannan suka je baby care aka cika akwati biyu tam da kayan baby, d'ayan Kuma aka cikeshi da kayan shafe shafe sannan tace su taho asibiti.
Shi dai Abba ya rasa Gane kanshi, farin ciki yake ko bak'in ciki oho, Amma kana kallon shi kasan akwai abunda ke damun shi.
Advertisement
Haka suka k'arasa asibitin lokacin har Umma ta tashi, dangi duk sun zagaye ta, dad'i ne ya Kama Umma Dan rabon da taga dangi an taru a kanta tun auran ta.
Tunani take to dama me yasa suka guje ta? Wata zuciyar tace mata halin Mummy.
Abba ma da yazo yaga jaririn shi d'aukan shi kawai yayi ya zuba ma yaron Ido, can sai ya share k'walla, Mummy Saudat ta kula da hakan, duk yanda akayi tasan d'an uwanta Yana cikin wani mawuyacin hali, addu'a kawai yake buk'ata, Dan tasan ba Haka yake ba.
Ganin jikin Umma ya koma normal yasa Mummy Zuwaira ta buk'aci sallama, Haseen ne ya biya duka bill d'in sannan aka kwashi Kaya sai gida, Abba kuwa da sunan Abban Ummah yayi wa yaro hud'uba wato *Abdullahi*, Haseenah tace za.ana kiranshi (Aaman).
Dangin Ummah kuwa murna kaman ba gobe, Nan aka Kira Abban Ummah aka sanar dashi, Nan yace ga tukwicinshi Yana isowa.
Motoci biyar akayi duk 'yan raka Ummah gida ne.
Mummy da Mum Haseen da Kuma Saratu na tsaka da Hira sukaji horn d'in mota, kallon kallo suka Fara yi, can Mummy tayi tsuka tace" Abban su ne fa"
Jin motar ba guda d'aya bane ya sasu duka yin shuru Dan sauraron abunda ke faruwa.
Kafin su yunk'ura su tashi sukaji Muryar Mummy Saudat tana rangad'a gud'a, mutuwar zaune dukansu sukayi, Mummy Zuwaira ce ta Fara shigowa rik'e da Aaman a hanunta an nad'e shi cikin showel farare tas, sai Ummah dake biye da su, sai Kuma jama'ar da suka rufa musu baya anata San barka.
Ko kallon inda Mummy take Basu Yi ba, palour Ummah suka wuce, Nan aka Fara shigowa da akwatuna Wanda Abba ya siya, Nan fa hankalin Mummy ya tashi.
Haseen ne shigowan k'arshe rik'e da basket sun jero tare da Haseenah gwanin sha'awa.
Advertisement
Wani zagi Mummy ta kutuntuma, lokaci d'aya tayi zubur ta mik'e ta fisge d'an kwali, Nan ta hau surfa masifa da zagi tana fad'in
"ba.a Isa a munafurce ta aci amanar ta ba, anje anyo ciki sannan za.a lank'aya wa mijin ta saboda anga yanada dukiya"
D'aya daga cikin 'yan uwan Umma ta lek'o tace" sai gashi kuwa aka haifo namiji Kuma ba"
Ihu Mummy ta sake tana fisge fisge, ganin zaninta na Shirin fad'uwa yasa Mum Haseen janta da k'yar sukayi ciki, tana tirjewa tana komai suka ja ta ita da Saratu suka turata d'aki suka kulle ta.
Dukda Haka bakin Mummy Bai mutu ba fad'i take" in dai da jini aka haifeta wallahi saita hallaka Ummah da d'an data Haifa.
Bata gama tsinkewa da Al amarin ba seda taji ana sake wani gud'an ganin galleliyar motar da Abban Ummah ya siya Mata, lek'awa Mummy tayi ta window Nan ta hango motar ko gama cire ledar jiki ba'a Yi ba, zaman dirshan Mummy tayi Kan tiles ta fashe da kukan bak'in ciki, ganin duk dangin shi sun cika wajan Mummy, gashi ta jiyo yanda ake ta yaba kayan akwati Wai Abba ne yayi Mata.
Kan uba, wallahi bazata yarda ba, ita za.a ciwa Amana, wannan karon ta d'au alwashi ko ta tsiya ko ta arzik'i ba bokan da zataje da kanta zata d'au mataki.
Ganinta kawai suke.
Kuka Tasha bana wasa ba, seda tayi Mai isarta sannan ta koma ajiyar zuciya.
Jin tayi shuru yasa Mum Haseen bud'e k'ofar ta shiga a hankali, Mummy ta hango gashin kanta a tsatstsaye sai kace mahaukaciya, Nan Mum Haseen ta Fara kwantar Mata da hankali, ta Bata shawara ta tashi su koma wajan boka.
Wani ashar d'in da Mummy ta k'unduma Mata ya sata Jan bakin ta tayi shuru, Mummy ta kalleta tace" ba wajan d'an iskan da Zan Kuma zuwa, da kaina da Kuma hanuna Zan d'au mataki"
Girgiza Kai Mum Haseen ta Fara yi tace" Yaya in hankali ya 6ata hankali ke Nemo shi, karkije ki aikata abunda zakiyi Dana sani daga baya, Haka Allah ya nufa ki d'au kaddara sai kiga Allah ya sauya Miki da mafi Alheri"
Tunda Mum Haseen ta Fara magana Mummy ta zuba Mata Ido take kallon ta Kai kace maganar ya shigeta ne, seda Mum Haseen ta yi shuru sannan Mummy ta dube ta tace " kin gama Dan ubanki? Munafuka kawai, dama nasan da saninki aka ci Amana ta, shiyasa naga Haseen bini bini Yana bin Mata kin kasa tsawatar mishi, ba ruwanki da damuwa ta dama nasan ba don Allah kike k'aunata ba, ki tashi ki ficemun a gida karna sake ganinki inba nice na nemeki ba"
Maganganun Mummy ya ta6a wa Mum Haseen zuciya, hakan ya sata mik'ewa ta d'au jakan ta ta fice a wajan, Haseen ta gani ya fito Nan tace ya ajiye ta a gida.
Tun da Mummy ta haihu kullum gidan shiga ake ana fita, Mummy kuwa ko fitowa Bata yi duk ta rame tayi bak'i ta fita a hayyacin ta, ta sak'a wannan ta kunce wannan duk ta rasa abin Yi.
Da Haka har yau akazo shagalin suna.
For comments 08144932303
Advertisement
- In Serial19 Chapters
Until You Do It Right
The world ended on December thirty-first of the year two thousand and twenty, precisely at the stroke of midnight. The human race began to be systematically exterminated by the spawn of the System. We were given a chance to defeat them, to take back our place at the top of the food chain. We failed. The first to perish were those who bravely rebelled. The soldiers. The defenders. One by one, they fell. In their final moments, they begged for aid. Nobody replied. The next to succumb were those who feebly cowered. The deniers. The leeches. Together, they fell. In their final moments, they cried out into the darkness. Countless voices replied in kind. The last to decline were those who shamelessly ran. The deserters. The cowardly. Alone, they fell. In their final moments, they whimpered quietly. There was nobody left to answer. The final human to die was a survivor. A runner. As he died, he begged for salvation. His prayers were answered. He was offered a chance to save himself, along with all of humanity, and he took it. This is his story. “I sat in the dark and thought: There’s no big apocalypse. Just an endless procession of little ones.”― Neil Gaiman, Signal to Noise. I am absolutely new to writing and will take any and all constructive criticism. Please give feedback, it is greatly appreciated. I will update the tags as they change, and I hope that you enjoy this little story I'm writing! Quick warning: Seamus is intentionally a flawed character, and this story is going to explore those flaws and perhaps even change a few of them. I do not agree with all of his actions, but it is what it is.
8 250 - In Serial30 Chapters
Caninstinct
Shiro believes he's been sent to the wrong school.Rormund Academy: home to only the best of the best. A school where only the wealthiest, smartest and most athletic students of the world reside. An establishment so exclusive even its name remains elusive to the public. Shiro exhibits none of these qualities, having more in common with a sheet of plywood than with royalty.Regardless, he intends on spending the last of his school years as planned; as a normal schoolboy and nothing more.Until they see the scars on his back. Biweekly updates with long word counts. Don't say you weren't warned.
8 113 - In Serial131 Chapters
Stardust Universe
Set in an alternative world where magic and modern soceity coexist. Infinitum Energy became the main source of energy to most things in this world. This energy can be found anywhere but especially on many of these people. They call these people, wizards. Besides having the basics of magic, each wizard also has their own unique ability which differs from others. Some may inherit from their family, and some may also inherit from an ancient race way before the dawn of wizards. Several months have passed since the end of his magic high school and Cyclone White, one of the few young wizards that has inherited the unique ability of a dragon after some slight setbacks now faces a brand new challenge in the form of university life. Enrolling into Infinity Academy leads to him encountering a whole different set of new friends, foes and even in between. How will the extroverted introvert overcome all of these new challenges? Join White as he uncovers the many mysteries of the world filled with Infinitum Energy.
8 145 - In Serial12 Chapters
The New Magnolia: Red Fungus, White Spore
The art for this cover was drawn by StarsColdNight whose account you can find on DeviantArt and BookCoversRealm for some great and splendid artwork at fair prices. Rillia flees from the Red Mountain Ant Colony and her country of Wassergras, hoping to find and explore the Primeval World, a legendary and untamed world she has only read about. However, after a surprise storm nearly drowns her, she is saved by Jason, a shrunken human with little memory of his past life. He is the first in a series of new allies she meets along with Melsil, the mushroom swordsman and Vesha the crawfish. A storm is brewing in Wassergras of political intrigue, prejudice and schemes within schemes that threaten to tear apart their world. Rillia must put her traveling plans on hold as she and her newly made friends work to defeat this threat—one that has been waging since the dawn of the world between the forces that created it.
8 186 - In Serial37 Chapters
Lost Things
"In this disordered continent, where everyone seeks to be the heroes of their own tales, there are still some rooms for smaller stories to breathe." "Past, present, and future—keep your eyes open, and see where they lead you to." This story follows three housemates’ lives: Carson Calding, Virgil Barion, and John Salore—onto their adventures of finding Carson’s past, Virgil’s present, and John’s future. Despite their clashing backgrounds and circumstances that forced them together, they’re definitely going to find the things they had lost, for sure. Each entire chapter will be updated biweekly. There'll be three smaller parts per each chapter. Note that this story was written to be an interactive one, with polls at the end of each parts deciding on what happens next. Though, the polls for this story won't be available on Royal Road updates. (I also upload this in Arcane Odyssey forum, and it's currently the only place where I open the polls and use the poll results from.)
8 255 - In Serial13 Chapters
He Never Loved Me (#Wattys2019)
This life is what I made it, I messed up, It's universal couldn't help it. But this broken heart I fell is the worst. It's like having broken ribs, no one can see, but it hurts every time I breath.
8 171

