《HASEENAH》PAGE 27&28
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
'''Dan Allah masu mun magana ta pc in tura musu novel dina suyi hakuri suna tanbaya a group, ina da matsalar network daga lokacin da nace kowa xan bishi in tura mishi in personal network dina yakan dad'e bai dawo dai dai ba, kuyi hakuri plx'''
*27~28*
Da gudu Saratu ta fito jin irin Kiran da Mummy ke Mata, duban ta tayi sannan tace" Ina wannan matsiyaciyar take?"
Ta nuna k'ofar d'akin su Haseenah.
Ta6e Baki Saratu tayi tace" na dai ga Haseenah ita da Yar Uwarta sun kamo Uwar an fita da ita da sauri, ban dai San menene ba"
Wani shewa Mummy ta saki tana fad'in" Haka akeso, Allah yasa tafiyar kenan"
Nan ta wuce ciki zuciyar ta fari tas, gani take yanzu Kap duniya Bata da wata damuwa, gida ya Zama nata, miji ya Zama nata Haka dukiyar shi ma daga ita sai 'yar ta.
Haka yau Mummy da kanta ta shiga kitchen ta zuba girki, tana gamawa ta fito musu dashi palour suka baje sai Kwasa suke suna Hira ita da Mum Haseen.
Can asibiti kuwa sai son barka ake, Hajiya Saudatu ne ta je har kasuwa ta tasa Abba a gaba suka shiga suka siya kayan abinci, da akwati gudu hud'u, da kanta ta shiga shagon Abba ta had'a kayan Umma akwati guda, sannan suka je baby care aka cika akwati biyu tam da kayan baby, d'ayan Kuma aka cikeshi da kayan shafe shafe sannan tace su taho asibiti.
Shi dai Abba ya rasa Gane kanshi, farin ciki yake ko bak'in ciki oho, Amma kana kallon shi kasan akwai abunda ke damun shi.
Advertisement
Haka suka k'arasa asibitin lokacin har Umma ta tashi, dangi duk sun zagaye ta, dad'i ne ya Kama Umma Dan rabon da taga dangi an taru a kanta tun auran ta.
Tunani take to dama me yasa suka guje ta? Wata zuciyar tace mata halin Mummy.
Abba ma da yazo yaga jaririn shi d'aukan shi kawai yayi ya zuba ma yaron Ido, can sai ya share k'walla, Mummy Saudat ta kula da hakan, duk yanda akayi tasan d'an uwanta Yana cikin wani mawuyacin hali, addu'a kawai yake buk'ata, Dan tasan ba Haka yake ba.
Ganin jikin Umma ya koma normal yasa Mummy Zuwaira ta buk'aci sallama, Haseen ne ya biya duka bill d'in sannan aka kwashi Kaya sai gida, Abba kuwa da sunan Abban Ummah yayi wa yaro hud'uba wato *Abdullahi*, Haseenah tace za.ana kiranshi (Aaman).
Dangin Ummah kuwa murna kaman ba gobe, Nan aka Kira Abban Ummah aka sanar dashi, Nan yace ga tukwicinshi Yana isowa.
Motoci biyar akayi duk 'yan raka Ummah gida ne.
Mummy da Mum Haseen da Kuma Saratu na tsaka da Hira sukaji horn d'in mota, kallon kallo suka Fara yi, can Mummy tayi tsuka tace" Abban su ne fa"
Jin motar ba guda d'aya bane ya sasu duka yin shuru Dan sauraron abunda ke faruwa.
Kafin su yunk'ura su tashi sukaji Muryar Mummy Saudat tana rangad'a gud'a, mutuwar zaune dukansu sukayi, Mummy Zuwaira ce ta Fara shigowa rik'e da Aaman a hanunta an nad'e shi cikin showel farare tas, sai Ummah dake biye da su, sai Kuma jama'ar da suka rufa musu baya anata San barka.
Ko kallon inda Mummy take Basu Yi ba, palour Ummah suka wuce, Nan aka Fara shigowa da akwatuna Wanda Abba ya siya, Nan fa hankalin Mummy ya tashi.
Haseen ne shigowan k'arshe rik'e da basket sun jero tare da Haseenah gwanin sha'awa.
Advertisement
Wani zagi Mummy ta kutuntuma, lokaci d'aya tayi zubur ta mik'e ta fisge d'an kwali, Nan ta hau surfa masifa da zagi tana fad'in
"ba.a Isa a munafurce ta aci amanar ta ba, anje anyo ciki sannan za.a lank'aya wa mijin ta saboda anga yanada dukiya"
D'aya daga cikin 'yan uwan Umma ta lek'o tace" sai gashi kuwa aka haifo namiji Kuma ba"
Ihu Mummy ta sake tana fisge fisge, ganin zaninta na Shirin fad'uwa yasa Mum Haseen janta da k'yar sukayi ciki, tana tirjewa tana komai suka ja ta ita da Saratu suka turata d'aki suka kulle ta.
Dukda Haka bakin Mummy Bai mutu ba fad'i take" in dai da jini aka haifeta wallahi saita hallaka Ummah da d'an data Haifa.
Bata gama tsinkewa da Al amarin ba seda taji ana sake wani gud'an ganin galleliyar motar da Abban Ummah ya siya Mata, lek'awa Mummy tayi ta window Nan ta hango motar ko gama cire ledar jiki ba'a Yi ba, zaman dirshan Mummy tayi Kan tiles ta fashe da kukan bak'in ciki, ganin duk dangin shi sun cika wajan Mummy, gashi ta jiyo yanda ake ta yaba kayan akwati Wai Abba ne yayi Mata.
Kan uba, wallahi bazata yarda ba, ita za.a ciwa Amana, wannan karon ta d'au alwashi ko ta tsiya ko ta arzik'i ba bokan da zataje da kanta zata d'au mataki.
Ganinta kawai suke.
Kuka Tasha bana wasa ba, seda tayi Mai isarta sannan ta koma ajiyar zuciya.
Jin tayi shuru yasa Mum Haseen bud'e k'ofar ta shiga a hankali, Mummy ta hango gashin kanta a tsatstsaye sai kace mahaukaciya, Nan Mum Haseen ta Fara kwantar Mata da hankali, ta Bata shawara ta tashi su koma wajan boka.
Wani ashar d'in da Mummy ta k'unduma Mata ya sata Jan bakin ta tayi shuru, Mummy ta kalleta tace" ba wajan d'an iskan da Zan Kuma zuwa, da kaina da Kuma hanuna Zan d'au mataki"
Girgiza Kai Mum Haseen ta Fara yi tace" Yaya in hankali ya 6ata hankali ke Nemo shi, karkije ki aikata abunda zakiyi Dana sani daga baya, Haka Allah ya nufa ki d'au kaddara sai kiga Allah ya sauya Miki da mafi Alheri"
Tunda Mum Haseen ta Fara magana Mummy ta zuba Mata Ido take kallon ta Kai kace maganar ya shigeta ne, seda Mum Haseen ta yi shuru sannan Mummy ta dube ta tace " kin gama Dan ubanki? Munafuka kawai, dama nasan da saninki aka ci Amana ta, shiyasa naga Haseen bini bini Yana bin Mata kin kasa tsawatar mishi, ba ruwanki da damuwa ta dama nasan ba don Allah kike k'aunata ba, ki tashi ki ficemun a gida karna sake ganinki inba nice na nemeki ba"
Maganganun Mummy ya ta6a wa Mum Haseen zuciya, hakan ya sata mik'ewa ta d'au jakan ta ta fice a wajan, Haseen ta gani ya fito Nan tace ya ajiye ta a gida.
Tun da Mummy ta haihu kullum gidan shiga ake ana fita, Mummy kuwa ko fitowa Bata yi duk ta rame tayi bak'i ta fita a hayyacin ta, ta sak'a wannan ta kunce wannan duk ta rasa abin Yi.
Da Haka har yau akazo shagalin suna.
For comments 08144932303
Advertisement
- In Serial472 Chapters
The Bloodline System
In a future timeline, the earth was visited by a species known as the Slarkovs.Having lost their home planet and in search of a new one, earth was the next habitable planet for them.Humans and Slarkovs made a deal with each other in return for the Slarkovs living on earth.The Slarkovs traded their technology and knowledge for a new home.They were similar to humans except for some of them who had slight differences so fitting into the society wasn’t a problem.Over the years Slarkovs and humans began to mate with one another and reproduce offsprings.This in turn created a new species known as the mixed-blood.Centuries later mixedbloods could tap into their bloodline and perform unimaginable feats.Gustav born into an age where bloodline determines everything, struggles to fit with a useless bloodline.His bloodline only grants him the ability to change his hair color, destroying his hopes and dreams for a great future.His fate is turned around when an unexpected situation leads to him finding a system that grants him the power to unlock and upgrade bloodlines by completing quests but he’s baffled by two quests with a five-year deadline. Success will grant him unimaginable rewards…But only one thing awaits him if he fails… Death!Follow Gustav on his interesting journey filled with unprecedented adventures, danger and death, maybe?
8 9026 - In Serial7 Chapters
Under the Tower!
What is the pit, what is the calamity? With a pinch of planar warfare, mystery cults, demons, gods and immortals. All this and more in Under the Tower! a story told in parts! Part 1This part follows Andha Ild, a Fire mage, who gained his power from his family bloodline. When he lost his eye, he was rescued by a mysterious arcanist, to whom he becomes an apprentice. On top of learning the profession, he learns how after the calamity, families with magic bloodlines restricted both information and power from those without these bloodlines. One day while training under the tower, he was chased by a cloud of disembodied hands, until he found a strange giant pit in the ground. He knew that some demons and invaders were sealed in these pits. But those pits were clearly marked. This pit was not, yet, here he is safe from the cloud of hands. One day the pit tells Andha that he can make a wish, if he sacrifices his arm. Remembering that those with bloodlines restricted those without, he wishes for all humans on this plane to have a magic bloodline. What happens next? (Current Part!) {[(!!!SPOILER!!!)]} Part 2This part follows Igwe Ild the grandson of Andha Ild, a Metal mage and government employee, who is on the run from the government after he finds out what the government is doing behind closed doors, and leaking this info to the press. (plot for p2 is a work in progress) Part 3This part follows the life of two brothers who attend a school founded by Igwe Ild, one day on their day home from school they find that their parents have gone missing. Follow as they find the culprit! (P3 Plot work in progress) I am also posting this series on ScribbleHubMy ScribbleHub profile: https://www.scribblehub.com/profile/64160/elijahryne/
8 70 - In Serial14 Chapters
Star Gazer
When the mist rolls in, most would either head inside, or brave it's perils via familiar terrain. But what if that mist holds secrets beyond which most could comprehend, let alone traverse? Mia, unequipped as she was, found herself in that very situation, but as danger approached, another came in time to save the girl from the unknown. Luke was a victim of the mist just as she was, and the pair had now begun a journey in a world home to only one of them from which a destiny was soon to be forged. ~~~~~ Star Gazer is high fantasy adventure set in a massive world within which our maturing duo of protagonists will be challenged to uncover truths few are aware are hidden at all. Elements of LitRPG are scattered within and function more as elements of certain character's abilities to read others, rather than a progression system by which our heroes will rely on. Updates will begin daily during premier week, but will slow down to 3 times weekly until further notice. Thank you for any and all support!
8 131 - In Serial47 Chapters
DM • JB
//In which Justin Bieber DMS an Instagram famous model // @JustinBieber liked your photo @JustinBieber started following you @JustinBieber sent you a message
8 174 - In Serial11 Chapters
The Great Demon Slayer Gatsu-be
It is an age of Cultivation, and battle-weary Chi-Wei Nic moves to the village of West End, where he discovers that his neighbor is the eclectic grandmaster Gatsu-be Jai. As he and Gatsu-be become acquainted, Nic is thrown into a world full of demon killing parties, guild politics, and unrequited love. Gatsu-be, though at the height of his cultivation, yearns for the love of a woman who chose another man. Dai Zee, stuck in a loveless marriage and used only as a weapon, dreams of what could have been - and gets a taste for it after she is reacquainted with Gatsu-be through Nic. THIS IS NOT A DEMON SLAYER FANFIC! This is an adaptation of the 1925 masterpiece, The Great Gatsby, considered by critics to be one of the greatest novels ever written. It is a portrait of a prosperous wuxia society that's full of literary intrigue, resounding metaphors, and dazzling glimpses into the chi and ether usage of legendary martial heroes. The Great Gatsby entered the public domain on January 1st, 2021.
8 175 - In Serial23 Chapters
CRYBABY
❝ tears fall to the ground, you just let them drop ❞Park Chaeyoung's life in the YG dungeon isn't what you expected it to be.[ BOOK 3 OFTHE DOLLHOUSESERIES. ]ORIGINALLY PUBLISHED: 2017RE-PUBLISHED: 2020
8 156

