《HASEENAH》PAGE 25&26
Advertisement
[7/17, 7:48 PM] 💄Meerah💋: 🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
*25-26*
Banda zare Ido ba abunda Abba keyi, Ummah kuwa hawaye kawai ke kwaranya, bak'in cikin ta d'aya yanda taga Mummy ta sasu gaba saikace Wanda tayi cikin shege?
Jijjiga shi Mummy takeyi tana magana da d'aga murya tana fad'in" kamun magana ko baka ganin abunda yake jikin ta ne?"
Girgiza Kai kawai yakeyi, ganin bashida niyar magana hakan ya dad'a fusata ta, ta koma Kan Umma ta d'auke ta da Mari had'e da cakume ta tace
" Ki fad'amun gidan uban da Kika samo wannan abun kunyar, in Kuma ba Haka ba wallahi sai na Tara Miki jama'a"
Ji tayi an hankad'e ta can gefe, sannan aka janyo ta aka Mata Mari biyu masu kyau, d'ip duhu ya ziyarci idanunta, wani haske taga ya wulga kamar walk'iya, Bata Ankara ba ta sake jin wasu tagwayen Marin, jiri taji ya kwashe ta ji kake dim Mummy ta fad'i k'asa,tayi zaman 'yan bori, Bata gama dawowa dai-dai ba ta tsinkayi Muryar Mummy Saudat, wato babbar yayar su Abba tana fad'in" kaji mun 'yar iska kasheta zakiyi? Zaki shak'e Mata ki sata gaba kina zazzaga Mata ruwan bala'i, kina tanbayarta aina ta samu ciki? Bata da miji ne? Ko kuma iskanci da neman sheganta mutum?"
A razane Mummy ta d'ago ta dubi Abba Dan gasgata abunda Mummy Saudat tace, sunkuyar da Kai yayi k'asa alamar rashin gaskiya.
Nan ko Mummy ta tuma tace " wallahi Nima seka mun cikin Nan munafiki kawai, inba munafunci ba yaushe kake zagawa ban saniba, sai anyi magana kayi ta k'ifta idanu sai kace an maka k'arya"
Advertisement
Dariya Mummy Saudat ta saka tace" Aiko ya kamata ya Miki cikin, zoki kwanta ya Miki"
Nan Mummy ta birkice lokaci d'aya ta fita hayyacin ta tace sai anje an zubar.
Ana cikin Haka saiga Mummy Zuwaira, tun daga gate take jin ihun Mummy, da sauri ta shiga Dan ganin abunda ke faruwa, jin ba.asi yasa Rai 6ace ta dubi Mummy tace " Lauratu na rantse da girman Allah daga Rana Mai kamar ta yau, ko ciwon ciki 'yar uwata tayi wallahi saina sa an d'aure ki, in Kuma yatsunki ya ta6a jikinta wallahi sai kinyi Dana sanin Zama a raye"
Sannan ta dubi Umma tace" kekuma tunda kin Zama Saratu uwar asara, karki fasa ruwan ciki"
Tana gama fad'in Haka tasa Kai ta tafi zuciyar ta duk Babu dad'i.
Hajiya Zuwaira ma Haka ta gama masifeta Amma ji take lokacin ma take da niyar aiwatar da abunda take shiri.
Komawa d'aki tayi ta figi gyalenta da mukullin motarta ta fice, Bata tsaya ko Ina ba sai gidansu Haseen, daga waje ta sa aka Kira mata ita, tana fitowa suka figi motor suka d'au hanyar gidan boka.
Gudu take kawai kamar zata tashi sama, Banda ajiyar zuciya ba abunda take, can saita bugi sitiyarin motor da hanunta ta Kai duka wa iska.
Tsoro da firgici kawai zaka dubi Mum Haseen kasan tana ciki ganin kamar mutuwa zasuyi irin gudun da sukeyi, gashi tayi tanbayar duniya Amma ko kallonta batayi ba.
Haka suka k'araso bakin kogin, Nan suka tsunduma ciki, suna fita suka hau tsauni, saboda bushewa da zuciyar Mummy tayi ko tsoro Babu a idonta balle zuciyar ta.
Suna gama Hawa suka tsaya yanda sukayi ranan.
Jim kad'an sai gasu tsugune gaban boka.
Dariyar da ya rink'a yi ne ya dad'a 6atawa Mummy Rai har Yana wani shid'ewa.
Ji take kamar ta tashi ta shak'e shi Amma ba hali.
Advertisement
Seda yayi me isarshi sannan ya tsagaita ya dubesu, kafin ya furta wani Abu Mummy ta cilla mishi bandir d'in dubu d'add'aya harna dubu d'ari biyar, sannan tace" boka asan yanda za.ayi a salwantar da matar Nan da abunda yake cikin ta, bana buk'atar ganinta a raye, damuwata in koma in samu tayi hauka ita Kuma 'yarta ta shiga duniya ta Fara yawon karuwanci"
Boka yasan ko giyan wake yake sha hakan bazai yuwuba, Amma ganin wannan k'udin da ke zube a gaban shi ya sa shi fad'in "an gama"
Ya nuna musu hanyar k'ofa yace "Zaku iya tafiya"
Nan suka kamo hanya murna fal zuciyar Mummy, yau tasan burin ta ya cika komai yazo k'arshe.
Can ko bayan dawowar Haseenah daga school ta tarar Umman ta tsugune a palour tana rik'e da cikin ta.
Da gudu ta k'arasa yanda take ta Kama ta tana Kiran sunan ta, ganin ba zata iya d'agata bane ya sata d'auko waya ta Kira Hajiya Zuwaira, ba jimawa sai gata ta iso.
Kama ta sukayi suka fito da ita waje, dai-dai lokacin sai ga Haseen ya danno da motar shi sai kace an jefo shi.
Ganin an rik'o Umma ya sashi parking da sauri ya fito, harara Haseenah ta watsa mishi ta kau da kanta gefe.
Sakata sukayi a motar Hajiya Zuwaira sannan ta fice a guje ba tare da tako tsaya Haseenah ta shiga ba.
Ganin haka yasa Haseen shiga mota ya dubi Haseenah yace" ki taho mubi bayan su karsu 6ace Mana"
Ba don ta so ba ta shiga gaba ya rufa musu baya.
Kai tsaye labour room aka wuce da Umma, Hajiya Zuwaira sai Kai komo take.
Suna isowa ta dubi Haseenah tace" Ina kayan haihuwan"
Sunkuyar da Kai Haseenah tayi hawaye na k'ok'arin zubo Mata, sai a lokacin itama ta tuna da laifinta ne Ashe ita ya kamata ta siya.
Duban Haseen tayi tace" ku tsaya anan Kai da Haseenah, duk abunda ake buk'ata kayi Ni zanje in dawo"
Gyad'a Mata Kai kawai yayi sannan ita Kuma ta fice.
Addu'a kawai Haseenah keyi Allah fito Mata da Umman ta lafiya, Haseen ma hakan ne, ba.a dad'e ba Mummy Zuwaira ta dawo d'auke da basket, ba tare da tace musu komai ba ta wuce su.
Ciki kuwa Abu ya gagara, ganin Haka yasa Mummy Zuwaira Kiran mahaifin su ta sanar mishi halin da ake ciki, Dan a cewar likitotin Nanda minti talatin in Bata haihu ba C'S za.a mata.
Nan yace zai turo da addu'a a kawo musu.
Ko minti talatin ba.ayi ba saiga aika an kawo, Nan itama ta k'ara tofa nata sannan aka shiga wa Umma da shi.
Ko minti biyar kuwa ba.ayi ba Umma ta haifo yaronta kyakkywa, Kama da Umma suke sossai.
Seda aka gyara yaro sannan aka fito da shi, murna gun Haseenah da Mummy Zuwaira ba.a magana, Haseen kuwa sai kallon Haseenah yake Dan Bai ta6a ganin dariyarta ba, ko yaushe se dai murmushi.
Nan Mummy Zuwaira ta Kira gida ta sanar musu, bayan Nan ta Kira Mummy Saudat wato yayar Abba.
Kafin kace meye asibiti ya cika, Umma kuwa Bata ma San Mai yake faruwa ba saboda baccin wahalar da take.
Dai dai lokacin Mummy ta Danno hancin motar ta gida, da farin ciki ta shigo, ko parking me kyau ba tayi ba ta 6alle murfin motor ta shige ciki, ganin Haka yasa Mum Haseen rufa Mata baya.
Suna shiga side d'insu Haseenah ta Fara kalla, Nan taji shuru.
K'walla wa Saratu Kira ta Fara yi tana fad'in.....
For comments only 08144932303
Advertisement
- In Serial44 Chapters
The Wuxia Adventure of an Edgy Earthling with a System
Ten years ago, Earth was assimilated into a mysterious entity spanning multiple galaxies that called itself [The System]. Al was sixteen at the time, and by a series of fortunate events and many, many close calls, he managed to become a top ranker and vanquish the big boss. Then he died. Al woke up as a baby in an orphanage in the middle of the woods, and after a while he realised something: “Wait, isn’t this basically a wuxia world!?”
8 174 - In Serial8 Chapters
Through The Eyes Of The Beast
Kill, Hate, Steal, Destroy, Rape. In the eyes of humans, these acts can only be done in extreme excess by a monster. a creature of nightmares. as soon as a human begins to do so, they are no longer considered human but a beast. However, it is not all true. Not all "monsters" do such things. Most just dont give a damn. In a world of piracy, adventure, and injustice are rampant, a beast waits its turn for the spotlight. Those humans can squabble over their power and their women, but not even the strongest can stand to The King Of The Ocean! I WILL BE KING IN THE END! (First time doing a fanfic. It should be interesting. Current world is one piece) (also, I'm making this to be unique so please enjoy and give me more Ideas for my brain factory. Thank you for your time, views, and Reviews.)
8 113 - In Serial12 Chapters
Cultivation Sect in Great Age of Piracy
Zhang Ergou, Seventh Grand Master of Saint Devil Sect. He was betrayed and killed by his followed master-disciple. His vision darkens and started closed. Ding! [Congrats, Host receive divine god grade cultivation skill, Heavenly Time God Technique] A story about someone from Xuanhuang World reborn into One Piece World. P.S* cover, not mine, get from googling on the web.
8 378 - In Serial31 Chapters
Future untold
Nora has always bent the truth to get her way or to complete a mission, but this lie could ultimately erase Carry from existence.-Artwork custom made by me.-#1's dcuniversecaitlinsnowDcuoFlashfrost#2'sBarryAllenSnowbarry#3'sArrowverse
8 401 - In Serial23 Chapters
Save The Netherworld, Iruma-Kun!! || A WTDSIK Fanfiction
(This is a Welcome To Demon School, Iruma-Kun! Fanfiction)Iruma Suzuki. Age 8. Sold to a demon called Balam Shichiro because his parents wanted to be rich. Iruma hadn't had the best life with his original parents. From being arrested at just five because of them to nearly getting killed by a bear, he wished his luck would change. Then his parents sold him to a demon. Balam Shichiro. He thought he was dead, but Balam decides to take Iruma as his own son, raising him as a demon. Now, Iruma has more problems to deal with. From making sure nobody realized he was a human to trying to rank up, he had to do his best.Suddenly, a new villain arises in the demon world, and the Thirteen whose watched over the demon world for centuries, way longer than Iruma had been alive, start dissapearing, Now Iruma has to continue to rank up while also making sure his dad and his friends wasn't taken as well. Will Iruma be able to stay safe and rank up with his friends? Or will he be the next meal on the Demons plates?
8 61 - In Serial16 Chapters
basically a smut book 🤭......
8 114

