《HASEENAH》PAGE 21&22
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
*21-22*
Hanyar side d'in Abban ta ta nufa Nan taji muryarshi na fad'in " Kika kuskura Kika taka k'afarki cikin wajan Nan wallahi sai jikinki ya Gaya Miki"
Juyawa tayi ta fasa ta shiga wajan su, palour ta zube ta rusa kuka, Umma tana jinta Amma ta kasa tashi Dan Bata ma San me zata ce Mata ba.
Sai kawai ita ma ta fashe da kukan.
Zuciyar Mummy kuwa fal farin ciki sai wani rawan Kai takeyi.
Haka rayuwa ta kasance wa su Haseenah dukan su sun rame ga Umma cikinta ya shiga wata biyar, ba wadataccen abinci, makaranta ma a k'afa Haseenah ke tafiya, ga Haseen tunda ya jibgi Saratu Mum d'inshi tace yazo ya bada hak'uri yace ba zaije ba shikenan ya d'auke k'afar shi.
Ga Umma Zuwaira tayi tafiya Bata zo ba, hakan yasa duk suka koma abun tausayi, ko fitowa Basu Isa suyi ba indai Abba Yana palour daga ita har Umma Babu Mai sukuni.
Yau ko abincin da zasu ci Babu, ganin hankalin Umma ya tashi yasa Haseenah saka hijabi ta fice ba tare da tasan inda zata nufa ba.
Tana fita zuwa k'ofar gate d'insu ta nema waje ta zauna gefen flower gidan nasu, had'a Kai da gwiwa tayi kawai saita hau kuka, horn d'in mota taji Nan tak'i d'ago wa, Dan tsoro take Kar Abban ta ne ya dawo Dan Yana ganin ta tasan ba makawa duka da zagi ne zai biyo baya.
Kashe motar tayi taji an d'ago ta, wa zata gani? Umma Zuwaira ta gani k'anwar Umman ta, dubanta Hajiya Zuwaira tayi tace" me kikeyi anan meya faru?"
Advertisement
Girgiza Kai Haseenah tayi ba tare da tace komai ba, janta tayi sukayi cikin gidan, Kai tsaye d'akin su ta nufa, Nan ma ta tarar Umma na kukan, salati ta Kama yi tana fad'in "me Zan gani yau? Me yake faruwa sai kace marasa lafiya duk kun fita a hayyacin ku?"
Dukkan su Babu Mai magana, mik'ewa Hajiya Zuwaira tayi ta wuce kitchen da nufin d'auko ruwa, Nan taga wayam ba komai a kitchen d'in, hasali ma Babu alamar yau anyi amfani da kitchen d'in.
Bata ce komai ba ta fito ta dubi Haseenah tace " zo muje ki rakani"
Nan Haseenah ta mik'e tabi bayan ta, Basu tsaya ko Ina ba sai kasuwa, buhun shinkafa ta siya biyu, indomie carton biyar, spaghetti carton biyar,macroni carton biyar,cous cous carton biyar, Maggi da sauran kayan spices kowanne carton, mangyad'a da manja ko wanne jarka, Naman da kifi ta sissiya Suma, ta siya musu kayan Miya da yawa ko wanne aka markad'a suka siya Sabin bokiti aka juye ciki, Nan aka cika boot tam, Nan suka shiga ciki Nan ta siya wa Haseenah uniform na school da na islamiya da yadin hijab guda biyar da dogayen riguna, Umma ma ta siya Mata atampopi, ta bada d'inki sannan ta siya musu omo dasu sabulu da Mai, seda aka cika har bayan seat sannan ta tsaya shagon waya ta siya k'arama ta had'a da sim suka tafi.
Kai tsaye gida suka wuce, Nan ta saka driver ya rink'a shiga da Kaya, ya d'auko na k'arshe kenan Nan Haseenah da Hajiya Zuwaira suka bi bayan shi, zai wuce kenan Mummy ta daka mishi tsawa tace" gidan ubanwa zaka Kai ko ba wajena aka ce ka kawo ba?"
Daga waje taji ance " gidan uban matambayi, ko kinyi aika ne Kika ga ba.a kawo Miki ba?"
Advertisement
Ido hud'u sukayi da Hajiya Zuwaira Nan Mummy ta had'e rai, Hajiya ta cigaba da cewa " ke Lauratu kiji tsoron Allah wallahi, nasan duk abunda kike, karki kuskura ki k'ureni wallahi ranan Mai k'wacen ki duk anguwan Nan Babu shi"
Tura d'an kwali Mummy tayi gaba ta cigaba da kad'a k'afa, Mummy tace" oho dai in kinji haushi ki d'auke ta ku tafi in Kuna son ta"
Dariyar takaici Hajiya Zuwaira tayi tace" Aiko kinsan cikin gatan ta aka d'auko ta, ba mabaraciya bace balle tayi rok'o, Kuma ke kanki kinsan da ubanta yanada masaniyar abunda yake faruwa wallahi da ba.a Kai wannan matsayin ba, shegiya da fuska kamar kashin makaho"
Haushi da bak'in ciki ne ya Kama mummy jin an ambaci kashin makaho, wato kashin uwarta kenan ko.
K'wafa tayi ta shige ciki ba tare da tace komai ba.
Duban Haseenah Hajiya Zuwaira tayi tace " wuce mu tafi uwar zurfin ciki"
Sum sum Haseenah ta d'au hanya Hajiya Zuwaira ta d'aka Mata duka tace " sai naci ubanki Kan wannan iskancin in ana Miki Abu Baki ramawa"
Ita dai batace komai ba suka shige ciki.
A store aka jibge musu komai, sannan Hajiya ta d'auko waya ta bawa Haseenah tace" ga wannan zanna kiranki saura kimun k'arya inzo har gida inci mutunci ki"
Kar6a tayi tare da godiya.
Kud'i ta d'auka naira dubu goma ta Basu tace su siya abunda Bata siya ba sannan tana Hawa mashin tana tafiya school Banda zuwan k'afa.
Nan har Hajiya Zuwaira ta tashi ta tafi Mummy ko lek'owa Bata sake yi ba.
Nan Haseenah ta dafa musu pepper soup na Kifi Nan sukaci, Dan rabon da suci sun manta ranan.
Mummy kuwa Haushi da bak'in ciki ne ya Kama ta, Dan Bata so hakan ba.
For comments 08144932303
Advertisement
- In Serial48 Chapters
Sacrificed to Summon a Shattered God
In a world overrun by demons, humanity is forced to survive in walled cities under the personal protection of their gods. When Derzina's city comes under attack, her goddess rushes to defend it only to be slain. Deprived of their guardian, the people of the city concoct a ritual to return her to them. However, the ritual requires a vessel to be offered to the goddess. Derzina, a lowly initiate, is chosen as the sacrifice for her goddess' resurrection. At least one new chapter will be posted every week. On hiatus.
8 232 - In Serial13 Chapters
Eczius
In a world of chaos and destruction where despair and the control of the Bonsan dominate, people have lost hope of living a safe life, the increasing of human slaves who were taken by the Bonsan, and the slaughter of the humans they dislike , a group from nothingness called "Orbikus" came out, a group of heroes have supernatural powers Called "Eczius", led by a boy who owns a rare Eczius called "Dioborikita", which can copy anyone's ability by touching him and can go through that force and develop it to reach its maximum power. This group has decided to attack the main base of the Bonsan and kill their leader to finish this bloody age, and they have already succeeded in reaching their leader but he managed to escape and promised to retaliate and to return to dominate them more than ever. This peace and security have lasted for years, generations, centuries, and Orbikus became a global organization and possessed a lot of powerful people where the spread of power became nothing strange with the advancement of technology. But as time passed the heirs of Dioborikita power disappeared and it is no longer inherited. It has not been shown for generations for unknown reasons, as a group of wicked powerful people appeared and became a new enemy next to the basic enemy the Bonsan. The events of this novel will be in the age of our hero "Akihiro"...
8 81 - In Serial6 Chapters
Looking For A Place Called Home
Maddie is a young girl who lives on an orphanage. She only wants a family to adopt and be there for her. Will she ever find a home?
8 156 - In Serial10 Chapters
One Direction bromances (oneshot)
So this is a collection of One Direction oneshot bromances. Available: Nouis, Zarry, Zouis, Narry, Lirry, Lilo, Ziall, Ziam, Niam, Larry.
8 83 - In Serial105 Chapters
Y'all loved the first one, the hits keep coming! All your HXH boys in absurd situations. Warning: I don't do boring! Enjoy!
8 196 - In Serial11 Chapters
Severus Snape x Reader
Y/N and Severus have been a couple in secret for about 3 years, now that you work in potions with him, you no longer have to hide it!
8 128

