《HASEENAH》PAGE 17&18
Advertisement
*HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
*17-18*
Da sauri suka nufa wajan Dan ganin abunda ya faru, Haseenah suka gani tsugune a wajan Tana tattara glasses d'in da suka tarwatse, yayin da ruwan da ta zubo a ciki ya wanke sauran maganin da Mummy ta barbad'a, hankalin Mummy ba k'aramin tashi yayi ba, Nan taji wani gumin ba zata ya fara karyo mata, ji tayi kaman ta shak'e Haseenah saboda bak'in ciki, batasan lokacin da ta d'aga hannu ta daidaici bayan Haseenah ta sake mata wani tafi ba, gantsarewa Haseenah tayi saboda azaba, Nan Mummy ta cigaba da banbami tana fad'in
" shegiyar yarinya dak'ik'iya mara tunani tinkiya, wato duk yanda akayi da jaki sai yaci Kara, ku na Kula ba a abun arzik'i daku tunda Baku ga da ba,ja ki bani waje in wuce kafin insa k'afa in yi k'wallo dake"
Mummy ta k'arashe maganar had'e da bangaje Haseenah gefe.
Haseenah Bata Kula Mummy ba saboda tasan dalilin masifar, Umma ma komawa ciki tayi Haseenah Kuma ta cigaba da gyara wajan.
Mummy na komawa d'aki ta lalubo numbar Mum Haseen, tana d'agawa tace mata tazo tana neman ta, ba ta sake jiran abunda zata ce ba ta katse wayar.
Cikin minti goma kuwa saiga ta ta iso, Nan Mummy ta Bata labarin abunda ya faru ta d'aura da cewa " nifa wallahi malamin Nan inaga garin k'uli ya Bamu, Babu wani canji, kina ga na dama kunu na Kai wa matsiyaciyar ba kunya ba tsoron Allah ta tand'e, maimakon inga wani canji ita bacci ma takeji, mtwxxx"
Shuru Mum Haseen tayi ta kasa cewa komai, Mummy ce to sake dubanta a fusace tace" Dan ubanki kinma mayar Dani mahaukaciya kenan, nayi magana kinja kinyi shuru seka ce Wanda nake Miki tafsiri ko? In bazaki iyq komai akai ba tashi ki ficemun daga gida"
Advertisement
Waya Mum Haseen ta zaro ta Danna numbar abokiyar kasuwancin ta, tana d'agawa taji tace" dama yanzu nakeson kiranki Kan ansamu wajan bokan Nan ya za'ayi muje yau Dan inason ganinshi"
"Yauwa fad'uwa tazo dai dai da Zama, dama Kan maganan na kiraki yanzu ki biyo gidan Yaya ta sai mu wuce" Mum Haseen ta Bata amsa.
Lokaci d'aya Mummy ta saki murmushin jin dad'i tace " ko ke fa yanzu naji Batu Mana"
Suna ta zance saiga Hajiya Saudat ta iso, Nan ta Kira Mum Haseen suka fita suka shiga motar ta suka wuce, tafiya suke tun suna hango cikin gari har suka fice, wani kwana suka yanka Banda kukan tsuntsaye ba abunda ke tashi, sunyi kusan tafiyar awa d'aya cikin wanna jeji Amma ko bukka Basu gani ba, Nan fa hankalin Mummy ya fara tashi Amma tayi shuru Banda sak'e 2 ba abunda take, wani kwanar taga an sake yanka an d'au hanya, ga hanyar ba kyau sai bubbuga Kai suke suna gware, can Kan Mummy ya fara ciwo ta ga yamma tayi kusan k'arfe 5:45pm na yamma, gashi taga kaman duniyan zasu bari Amma har yanzu ba.a iso ba, ga uban gudun da Hajiya Saudat ke yi Kai kace sama zata tashi, can Mummy dai ta kasa daurewa tace " wai inane zamuje haka saikace tafiyar ya da shege? Tun Rana muke tafiya har yanzu ba'a iso ba Banga Kuma Ana da niyar tsayawa ba"
Harara Hajiya Saudat ta zabga mata sannan tace" Dalla Malama tsaya, ni da nake driving bance komai ba sai keda kike zaman banza? Wallahi ni inkika ce Zaki mun mita Allah tsakiyar dajin Nan Zaki sauka mun a mota"
Jin haka yasa Mummy Kama bakinta tayi k'wafa sannan tayi shuru.
Dai dai wata tafkekekiyar kogi tayi parking sannan ta dubesu tace " ku fito mu tafi"
Nan fa Mummy da Mum Haseen suka hau kallon kallo Ana zare Ido, ganin Saudatu ta fara gaba Suka sa6a jaka suka bi bayan ta, tattara zani sukaga tayi ta cire takalmi da mayafi ta zuba cikin jaka, Suma da sauri suka cire nasu sukayi yanda tayi, shiga ta fara yi Suma cike da tsoro suka bi bayanta, Kama hanun juna sukayi suna shiga a hankali, haka ruwan ya hauro har kwankwanson su suna tafiya cike da tsoro, ita dai Mummy duk ta karaya ba yanda ta iya ne kawai Amma ta gama sadaukar da rayuwa yau zata bar duniyan, kusan minti talatin suna Abu d'aya daga bisani suka Kai bakin kogin suka fice.
Advertisement
Lokacin kuwa yamma sossai ta kawo Kai Dan ankusa Kiran magriba, Nan suka Chiro takalma suka sa da mayafan su, wani uban dutse suka ga Hajiya Saudatu ta nufa Nan suka fara Hawa da Nishi da wayyo Allah, da Mummy taga mayafin zai Zama mata Kaya Nan ta cire taci d'amara dashi daka ganta kaga 'yar k'auye sak, Hawa suke suna k'arawa, duk gumi ya jik'asu ga yunwa ga k'ishir ruwa, da k'yar suka k'arasa Hawa Nan suka hango bukka, wata ajiyar zuciya duka sukayi, Basu kaiga sauke numfashi ba sukaji wata mummunar murya tana fad'in " karku 6ata mun lokaci"
Ihu Mummy ta saki tana fad'in" wayyo Aljanu"
Dariya taji Muryar ta sake yi seda dajin ya amsa sannan cikin tsawa taji ance" ki rufa Mana baki"
Toshe bakin ta tayi da duka hannayen ta tana furta " wallahi nayi"
Dukansu seda abun ya Basu dariya ganin yanda Mummy ta koma cikin seconds, Nan suka fara takawa a hankali har suka Isa bakin k'ofar bukkar.
Basu Ankara ba suka sake jin wannan Muryar tace" auta shigo min dasu"
Cikin abun da baifi k'iftawar Ido ba sukaji kaman anyi patali da su, sai ganin su sukayi gaban wannan boka mai Kama da aladen jeji, kyarma Mummy ta fara yi ita da Mum Haseen, ganin ya tsare su da Ido ne ya sasu nutsuwar dole.
Sunkuyawa Hajiya Saudatu tayi kamar Mai sujada sannan ta fara rafka mishi kirari Kai da kaji kasan tsuran sa6o ne kawai da barin Kan tafarkin Allah (S.W.A) *Allah ya tsare Mana imaninmu ameen*
Ganin yanda ta durk'ushe yasa Suma suka yi, shi Kuma ya hau yashe hak'ora Yana fad'in
" buk'atar ku ta biya"
D'agowa sukayi Nan ya dube su duka yace " nasan damuwarku"
nuna Mummy yayi yacigaba da cewa " ke akan abokiyar zamanki da Kuma mijinki ne, Amma kashetan da kikeso kiyi bazai yuwa yanzu ba, farkon abunda zakiyi shine shiga tsakaninta da mijinki ya Dena Kula ta"
Da sauri a razane Mummy ta dube shi jin abunda yace, maimaita wa take a ranta, gyad'a Kai yayi yace" hak'ika Yana kula ta Dan Nan bada dad'ewa ba Zaki ga sakamakon had'uwar da suke Nanda wasu 'yan watanni"
Cikin rashin fahimta Mummy tace" wani irin sakamako kenan?"
Girgiza Kai yayi yace" ba a bani Daman fad'an hakan ba, Amma inkika bi hanyoyin da na fad'a Miki ke da kanki Zaki fahimta abunda nake nufi"
Da sauri tace " ayi duk abunda ya Dace boka"
Seda ya gama wasu dube duben shi sannan sukaga an cillo wa kowa k'ulli gaban su, Mummy ya fara kallo yace" wannan k'ullin ki nemi inda kikasan ko yaushe Yana tsallakawa ki binne a wajan, wannan garin Kuma ki barbad'a mishi a abinci daga 'yar har uwar zai tsanesu, wannan Kuma inkin fara al'ada ki kwa6a da jini ki sake tusawa a gaban ki, Kuma kisan duk hanyar da zakibi ya yi kwanciyar aure dake lokacin buk'atar ki ta gama biya sai Kuma ta gaba"
Nan dukansu ya musu bayani, murna ne fal zuciyar Mummy Nan ta kwaso bunch na dubu d'add'aya guda uku ta dire mishi.
Nan suka fice suka d'au hanya, duk tsoron hanya da Mummy keyi duk sai taji ya kau, gudu kawai suke zabgawa lokacin har an dad'e da idar da sallar isha'i, sun k'ure kid'a irinna 'yan matan bariki sai shewa suke, Basu Ankara ba suka hango wash manyan mutane kowannen su d'auke da......
For comments 0814493230
Advertisement
- In Serial443 Chapters
The Rise Of A Porter
Do read my WSA 2021 novel **Alone: Tale of a Monster Hunter**.
8 902 - In Serial6 Chapters
Legends of Adora, This Halfryta's Garden
For six long generations war, waged in the lands of Adora Halfryta. It all began during the reign of 2nd Cleric. With the passing of the Temple's edict - The colonies across the continents of Halfryta, fought. In order to establish their own power, dominion, territories & place in history, for six generations honourable battle raged across these holy lands. In the face of the Holy Temple, and its' counter part Halfryta's Scions, it would be after the fighting that the lords of Halfryta fully emerged a third ruling faction. This happened when the fighting was brought to an end by 6th generation Scion, bearer of fire, Azure King Aohd Egan. Few non-human settlements remain in open sight near civilization after experiencing much indiscriminate torment. Peace came at a cost. Eight years since the end of The Lords' War: the divide between the Adora Temple, The Lords, and The Scions is clearer than ever. Now, King Aohd's son Marise Egan, the soon to be crowned, 7th generation scion of fire and his friends must find for themselves destiny is choice as is truth. The stench of chaos lingers still, and it is why the scions exist. Has a new age of order truly begun? Or will chaos tip the scales yet? Only The Goddess Halfryta knows.Follow the journey of 7th generation scions Marise Egan, Eurus Clover, Maralah Clover, and Fenris Benebarakk in their early youth as they learn and grow together at Adora Templum, the temple monastery and a home and school to believers and followers the Goddess Adora and her teachings, following their coronation as bearers of the scions’ duty learning live with their new-found powers.Journey with young Fenris as he settles the deep inner conflicts between his conscience and his obligation to his family and nation. Torn by the actions of his father, a powerful and violent king in support of seceding from the holy teachings – siding with the lords seeking to militarize the whole continental world on the heels of the Lord’s War. Fenris, a boy far too mature for his age tasked too early with drawing the line between personal duty, and destiny – while participating both in campaigns of war, and teachings of peace.
8 157 - In Serial13 Chapters
Abyssmal Downpour
Abysmall downpour is a story about a young civilian from a futuristic world, who undergoing everyday life finds himself in an unknown world as he wokes up one day.The protagonist (Karl Fenrir) tries every possible way to survive in a desolate world, where he may be the last of homosapiens !. Where evolution ,bought in various forms, is taking place at horrendous rates . Follow him on ride for answers leading to further questions. Truth is always laying front but couldn't be more hidden. As his two 'worlds' intermingle, what will the fate have in store for him?
8 150 - In Serial56 Chapters
Random COTE reaction ( On Hold)
This is not a normal reaction fanfic I added some things so basically its my auTimeline y1 vol 3 after island exam
8 248 - In Serial18 Chapters
Love Live! Revolution!
Idols are now illegal and the world seems empty. Yet, one boy alongside his childhood friends, You Watanabe and Miguel, wants to bring back the love that that has been taken away from the peoples' lives... Even if it means breaking the law. AU where members of μ's (Muse), Aquors, Nijisaki, and Superstar are included.
8 145 - In Serial25 Chapters
Metal Fight Beyblade Truth or Dare 2020!
Hi everyone! I hope you like this book!Just a typical day of bladers being tortured, bringing back their , and even the host's worst nightmares, in the form of truth or dare, run by the worst people in history.Disclamer: Only Lily (which is me), some truths , dares and some of the plot belongs to me Other Truths and Dares belong to readers and Characters and beys belong to MFBFrom Lily.CDon't forget to follow if you liked it !Disclaimer: I am not a writer, so i am so sorry if you spot a mistake.Bye!date: 17/5/2020Warning, some language inappropriate for young kids, please be careful.
8 208

