《HASEENAH》PAGE 17&18
Advertisement
*HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
*17-18*
Da sauri suka nufa wajan Dan ganin abunda ya faru, Haseenah suka gani tsugune a wajan Tana tattara glasses d'in da suka tarwatse, yayin da ruwan da ta zubo a ciki ya wanke sauran maganin da Mummy ta barbad'a, hankalin Mummy ba k'aramin tashi yayi ba, Nan taji wani gumin ba zata ya fara karyo mata, ji tayi kaman ta shak'e Haseenah saboda bak'in ciki, batasan lokacin da ta d'aga hannu ta daidaici bayan Haseenah ta sake mata wani tafi ba, gantsarewa Haseenah tayi saboda azaba, Nan Mummy ta cigaba da banbami tana fad'in
" shegiyar yarinya dak'ik'iya mara tunani tinkiya, wato duk yanda akayi da jaki sai yaci Kara, ku na Kula ba a abun arzik'i daku tunda Baku ga da ba,ja ki bani waje in wuce kafin insa k'afa in yi k'wallo dake"
Mummy ta k'arashe maganar had'e da bangaje Haseenah gefe.
Haseenah Bata Kula Mummy ba saboda tasan dalilin masifar, Umma ma komawa ciki tayi Haseenah Kuma ta cigaba da gyara wajan.
Mummy na komawa d'aki ta lalubo numbar Mum Haseen, tana d'agawa tace mata tazo tana neman ta, ba ta sake jiran abunda zata ce ba ta katse wayar.
Cikin minti goma kuwa saiga ta ta iso, Nan Mummy ta Bata labarin abunda ya faru ta d'aura da cewa " nifa wallahi malamin Nan inaga garin k'uli ya Bamu, Babu wani canji, kina ga na dama kunu na Kai wa matsiyaciyar ba kunya ba tsoron Allah ta tand'e, maimakon inga wani canji ita bacci ma takeji, mtwxxx"
Shuru Mum Haseen tayi ta kasa cewa komai, Mummy ce to sake dubanta a fusace tace" Dan ubanki kinma mayar Dani mahaukaciya kenan, nayi magana kinja kinyi shuru seka ce Wanda nake Miki tafsiri ko? In bazaki iyq komai akai ba tashi ki ficemun daga gida"
Advertisement
Waya Mum Haseen ta zaro ta Danna numbar abokiyar kasuwancin ta, tana d'agawa taji tace" dama yanzu nakeson kiranki Kan ansamu wajan bokan Nan ya za'ayi muje yau Dan inason ganinshi"
"Yauwa fad'uwa tazo dai dai da Zama, dama Kan maganan na kiraki yanzu ki biyo gidan Yaya ta sai mu wuce" Mum Haseen ta Bata amsa.
Lokaci d'aya Mummy ta saki murmushin jin dad'i tace " ko ke fa yanzu naji Batu Mana"
Suna ta zance saiga Hajiya Saudat ta iso, Nan ta Kira Mum Haseen suka fita suka shiga motar ta suka wuce, tafiya suke tun suna hango cikin gari har suka fice, wani kwana suka yanka Banda kukan tsuntsaye ba abunda ke tashi, sunyi kusan tafiyar awa d'aya cikin wanna jeji Amma ko bukka Basu gani ba, Nan fa hankalin Mummy ya fara tashi Amma tayi shuru Banda sak'e 2 ba abunda take, wani kwanar taga an sake yanka an d'au hanya, ga hanyar ba kyau sai bubbuga Kai suke suna gware, can Kan Mummy ya fara ciwo ta ga yamma tayi kusan k'arfe 5:45pm na yamma, gashi taga kaman duniyan zasu bari Amma har yanzu ba.a iso ba, ga uban gudun da Hajiya Saudat ke yi Kai kace sama zata tashi, can Mummy dai ta kasa daurewa tace " wai inane zamuje haka saikace tafiyar ya da shege? Tun Rana muke tafiya har yanzu ba'a iso ba Banga Kuma Ana da niyar tsayawa ba"
Harara Hajiya Saudat ta zabga mata sannan tace" Dalla Malama tsaya, ni da nake driving bance komai ba sai keda kike zaman banza? Wallahi ni inkika ce Zaki mun mita Allah tsakiyar dajin Nan Zaki sauka mun a mota"
Jin haka yasa Mummy Kama bakinta tayi k'wafa sannan tayi shuru.
Dai dai wata tafkekekiyar kogi tayi parking sannan ta dubesu tace " ku fito mu tafi"
Nan fa Mummy da Mum Haseen suka hau kallon kallo Ana zare Ido, ganin Saudatu ta fara gaba Suka sa6a jaka suka bi bayan ta, tattara zani sukaga tayi ta cire takalmi da mayafi ta zuba cikin jaka, Suma da sauri suka cire nasu sukayi yanda tayi, shiga ta fara yi Suma cike da tsoro suka bi bayanta, Kama hanun juna sukayi suna shiga a hankali, haka ruwan ya hauro har kwankwanson su suna tafiya cike da tsoro, ita dai Mummy duk ta karaya ba yanda ta iya ne kawai Amma ta gama sadaukar da rayuwa yau zata bar duniyan, kusan minti talatin suna Abu d'aya daga bisani suka Kai bakin kogin suka fice.
Advertisement
Lokacin kuwa yamma sossai ta kawo Kai Dan ankusa Kiran magriba, Nan suka Chiro takalma suka sa da mayafan su, wani uban dutse suka ga Hajiya Saudatu ta nufa Nan suka fara Hawa da Nishi da wayyo Allah, da Mummy taga mayafin zai Zama mata Kaya Nan ta cire taci d'amara dashi daka ganta kaga 'yar k'auye sak, Hawa suke suna k'arawa, duk gumi ya jik'asu ga yunwa ga k'ishir ruwa, da k'yar suka k'arasa Hawa Nan suka hango bukka, wata ajiyar zuciya duka sukayi, Basu kaiga sauke numfashi ba sukaji wata mummunar murya tana fad'in " karku 6ata mun lokaci"
Ihu Mummy ta saki tana fad'in" wayyo Aljanu"
Dariya taji Muryar ta sake yi seda dajin ya amsa sannan cikin tsawa taji ance" ki rufa Mana baki"
Toshe bakin ta tayi da duka hannayen ta tana furta " wallahi nayi"
Dukansu seda abun ya Basu dariya ganin yanda Mummy ta koma cikin seconds, Nan suka fara takawa a hankali har suka Isa bakin k'ofar bukkar.
Basu Ankara ba suka sake jin wannan Muryar tace" auta shigo min dasu"
Cikin abun da baifi k'iftawar Ido ba sukaji kaman anyi patali da su, sai ganin su sukayi gaban wannan boka mai Kama da aladen jeji, kyarma Mummy ta fara yi ita da Mum Haseen, ganin ya tsare su da Ido ne ya sasu nutsuwar dole.
Sunkuyawa Hajiya Saudatu tayi kamar Mai sujada sannan ta fara rafka mishi kirari Kai da kaji kasan tsuran sa6o ne kawai da barin Kan tafarkin Allah (S.W.A) *Allah ya tsare Mana imaninmu ameen*
Ganin yanda ta durk'ushe yasa Suma suka yi, shi Kuma ya hau yashe hak'ora Yana fad'in
" buk'atar ku ta biya"
D'agowa sukayi Nan ya dube su duka yace " nasan damuwarku"
nuna Mummy yayi yacigaba da cewa " ke akan abokiyar zamanki da Kuma mijinki ne, Amma kashetan da kikeso kiyi bazai yuwa yanzu ba, farkon abunda zakiyi shine shiga tsakaninta da mijinki ya Dena Kula ta"
Da sauri a razane Mummy ta dube shi jin abunda yace, maimaita wa take a ranta, gyad'a Kai yayi yace" hak'ika Yana kula ta Dan Nan bada dad'ewa ba Zaki ga sakamakon had'uwar da suke Nanda wasu 'yan watanni"
Cikin rashin fahimta Mummy tace" wani irin sakamako kenan?"
Girgiza Kai yayi yace" ba a bani Daman fad'an hakan ba, Amma inkika bi hanyoyin da na fad'a Miki ke da kanki Zaki fahimta abunda nake nufi"
Da sauri tace " ayi duk abunda ya Dace boka"
Seda ya gama wasu dube duben shi sannan sukaga an cillo wa kowa k'ulli gaban su, Mummy ya fara kallo yace" wannan k'ullin ki nemi inda kikasan ko yaushe Yana tsallakawa ki binne a wajan, wannan garin Kuma ki barbad'a mishi a abinci daga 'yar har uwar zai tsanesu, wannan Kuma inkin fara al'ada ki kwa6a da jini ki sake tusawa a gaban ki, Kuma kisan duk hanyar da zakibi ya yi kwanciyar aure dake lokacin buk'atar ki ta gama biya sai Kuma ta gaba"
Nan dukansu ya musu bayani, murna ne fal zuciyar Mummy Nan ta kwaso bunch na dubu d'add'aya guda uku ta dire mishi.
Nan suka fice suka d'au hanya, duk tsoron hanya da Mummy keyi duk sai taji ya kau, gudu kawai suke zabgawa lokacin har an dad'e da idar da sallar isha'i, sun k'ure kid'a irinna 'yan matan bariki sai shewa suke, Basu Ankara ba suka hango wash manyan mutane kowannen su d'auke da......
For comments 0814493230
Advertisement
- In Serial1363 Chapters
VRMMO: The Unrivaled
Lu Chen used to be a ranker of the most popular VRMMO game, Spirit of Grief. After a car accident turned his dreams into dust, his disability left him incapable of escaping the pit of mediocrity he was thrown into. Helpless and defeated, his story ended.Two years later, the Eternal Moon Corporation launched a new VRMMO called "Heavenblessed", and Lu Chen stumbled into another terrible accident that left him in a complicated situation far beyond his ability to handle. That won't stop him from rising to the top, however. Not again.Come witness the rise of the sword-wielding zombie and the relationships he makes during his journey to the apex! For riches and bi- ahem, for career and love!He wields a demonic sword from Hell, he dons armor shining with Heaven's light. His boots stride across the sky as his helmet devours the souls of his enemies. On his left side sits the Goddess of Death. On the other, the Angel of Beauty.From the land of ice and death, a generation of Asura Kings rises, their roars reverberating throughout the world.Tremble in fear, noobs!
8 8158 - In Serial1353 Chapters
Refining the Mountains and Rivers
A young man's life changes when he stumbles upon a mysterious item. Qin Yu had never been a lucky person. Weak of body, bullied by his peers, and with only his friend as his family, he struggles day-by-day to live. But everything changes when he stumbles upon a little blue lamp. An immortal and demonic cultivating adventure.
8 3346 - In Serial2455 Chapters
Mortal Cultivation Biography
A poor and ordinary boy from a village joins a minor sect in Jiang Hu and becomes an Unofficial Disciple by chance. How will Han Li, a commoner by birth, establish a foothold for himself in in his sect? With his mediocre aptitude, he must successfully traverse the treacherous path of cultivation and avoid the notice of those who may do him harm. This is a story of an ordinary mortal who, against all odds, clashes with devilish demons and ancient celestials in order to find his own path towards immortality.
8 1057 - In Serial1503 Chapters
Dragon Prince Yuan
Destiny stolen at birth, the prince of the once mighty Great Zhou Empire, Zhou Yuan, has been plagued all his life by a fatal poison, forced to suffer powerlessly until one day when fate draws him into a mysterious domain where he meets a beautiful girl in green, a bizarre dog-like creature and an unfathomable old man in black.Join Zhou Yuan as he is thrust into the whirlpool of destiny while he seeks the pinnacle of cultivation.
8 1060 - In Serial677 Chapters
Ranker's Return
In the early days of the virtual reality game, Arena, meleegod was the strongest ranked player! He deleted his character and suddenly left. In order to restore his bankrupt family, he returned to Arena!"Do you want to create a character?"
8 1719 - In Serial1525 Chapters
Monarch of Evernight
Qianye rose from hardship but was felled by betrayal. From then, one man, one gun; he tread the path between Evernight and Daybreak and became a legend. Even if Evernight was destined to be his fate, he still intends to become the ruler who dictates.
8 22867

