《HASEENAH》PAGE 17&18
Advertisement
*HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
*17-18*
Da sauri suka nufa wajan Dan ganin abunda ya faru, Haseenah suka gani tsugune a wajan Tana tattara glasses d'in da suka tarwatse, yayin da ruwan da ta zubo a ciki ya wanke sauran maganin da Mummy ta barbad'a, hankalin Mummy ba k'aramin tashi yayi ba, Nan taji wani gumin ba zata ya fara karyo mata, ji tayi kaman ta shak'e Haseenah saboda bak'in ciki, batasan lokacin da ta d'aga hannu ta daidaici bayan Haseenah ta sake mata wani tafi ba, gantsarewa Haseenah tayi saboda azaba, Nan Mummy ta cigaba da banbami tana fad'in
" shegiyar yarinya dak'ik'iya mara tunani tinkiya, wato duk yanda akayi da jaki sai yaci Kara, ku na Kula ba a abun arzik'i daku tunda Baku ga da ba,ja ki bani waje in wuce kafin insa k'afa in yi k'wallo dake"
Mummy ta k'arashe maganar had'e da bangaje Haseenah gefe.
Haseenah Bata Kula Mummy ba saboda tasan dalilin masifar, Umma ma komawa ciki tayi Haseenah Kuma ta cigaba da gyara wajan.
Mummy na komawa d'aki ta lalubo numbar Mum Haseen, tana d'agawa tace mata tazo tana neman ta, ba ta sake jiran abunda zata ce ba ta katse wayar.
Cikin minti goma kuwa saiga ta ta iso, Nan Mummy ta Bata labarin abunda ya faru ta d'aura da cewa " nifa wallahi malamin Nan inaga garin k'uli ya Bamu, Babu wani canji, kina ga na dama kunu na Kai wa matsiyaciyar ba kunya ba tsoron Allah ta tand'e, maimakon inga wani canji ita bacci ma takeji, mtwxxx"
Shuru Mum Haseen tayi ta kasa cewa komai, Mummy ce to sake dubanta a fusace tace" Dan ubanki kinma mayar Dani mahaukaciya kenan, nayi magana kinja kinyi shuru seka ce Wanda nake Miki tafsiri ko? In bazaki iyq komai akai ba tashi ki ficemun daga gida"
Advertisement
Waya Mum Haseen ta zaro ta Danna numbar abokiyar kasuwancin ta, tana d'agawa taji tace" dama yanzu nakeson kiranki Kan ansamu wajan bokan Nan ya za'ayi muje yau Dan inason ganinshi"
"Yauwa fad'uwa tazo dai dai da Zama, dama Kan maganan na kiraki yanzu ki biyo gidan Yaya ta sai mu wuce" Mum Haseen ta Bata amsa.
Lokaci d'aya Mummy ta saki murmushin jin dad'i tace " ko ke fa yanzu naji Batu Mana"
Suna ta zance saiga Hajiya Saudat ta iso, Nan ta Kira Mum Haseen suka fita suka shiga motar ta suka wuce, tafiya suke tun suna hango cikin gari har suka fice, wani kwana suka yanka Banda kukan tsuntsaye ba abunda ke tashi, sunyi kusan tafiyar awa d'aya cikin wanna jeji Amma ko bukka Basu gani ba, Nan fa hankalin Mummy ya fara tashi Amma tayi shuru Banda sak'e 2 ba abunda take, wani kwanar taga an sake yanka an d'au hanya, ga hanyar ba kyau sai bubbuga Kai suke suna gware, can Kan Mummy ya fara ciwo ta ga yamma tayi kusan k'arfe 5:45pm na yamma, gashi taga kaman duniyan zasu bari Amma har yanzu ba.a iso ba, ga uban gudun da Hajiya Saudat ke yi Kai kace sama zata tashi, can Mummy dai ta kasa daurewa tace " wai inane zamuje haka saikace tafiyar ya da shege? Tun Rana muke tafiya har yanzu ba'a iso ba Banga Kuma Ana da niyar tsayawa ba"
Harara Hajiya Saudat ta zabga mata sannan tace" Dalla Malama tsaya, ni da nake driving bance komai ba sai keda kike zaman banza? Wallahi ni inkika ce Zaki mun mita Allah tsakiyar dajin Nan Zaki sauka mun a mota"
Jin haka yasa Mummy Kama bakinta tayi k'wafa sannan tayi shuru.
Dai dai wata tafkekekiyar kogi tayi parking sannan ta dubesu tace " ku fito mu tafi"
Nan fa Mummy da Mum Haseen suka hau kallon kallo Ana zare Ido, ganin Saudatu ta fara gaba Suka sa6a jaka suka bi bayan ta, tattara zani sukaga tayi ta cire takalmi da mayafi ta zuba cikin jaka, Suma da sauri suka cire nasu sukayi yanda tayi, shiga ta fara yi Suma cike da tsoro suka bi bayanta, Kama hanun juna sukayi suna shiga a hankali, haka ruwan ya hauro har kwankwanson su suna tafiya cike da tsoro, ita dai Mummy duk ta karaya ba yanda ta iya ne kawai Amma ta gama sadaukar da rayuwa yau zata bar duniyan, kusan minti talatin suna Abu d'aya daga bisani suka Kai bakin kogin suka fice.
Advertisement
Lokacin kuwa yamma sossai ta kawo Kai Dan ankusa Kiran magriba, Nan suka Chiro takalma suka sa da mayafan su, wani uban dutse suka ga Hajiya Saudatu ta nufa Nan suka fara Hawa da Nishi da wayyo Allah, da Mummy taga mayafin zai Zama mata Kaya Nan ta cire taci d'amara dashi daka ganta kaga 'yar k'auye sak, Hawa suke suna k'arawa, duk gumi ya jik'asu ga yunwa ga k'ishir ruwa, da k'yar suka k'arasa Hawa Nan suka hango bukka, wata ajiyar zuciya duka sukayi, Basu kaiga sauke numfashi ba sukaji wata mummunar murya tana fad'in " karku 6ata mun lokaci"
Ihu Mummy ta saki tana fad'in" wayyo Aljanu"
Dariya taji Muryar ta sake yi seda dajin ya amsa sannan cikin tsawa taji ance" ki rufa Mana baki"
Toshe bakin ta tayi da duka hannayen ta tana furta " wallahi nayi"
Dukansu seda abun ya Basu dariya ganin yanda Mummy ta koma cikin seconds, Nan suka fara takawa a hankali har suka Isa bakin k'ofar bukkar.
Basu Ankara ba suka sake jin wannan Muryar tace" auta shigo min dasu"
Cikin abun da baifi k'iftawar Ido ba sukaji kaman anyi patali da su, sai ganin su sukayi gaban wannan boka mai Kama da aladen jeji, kyarma Mummy ta fara yi ita da Mum Haseen, ganin ya tsare su da Ido ne ya sasu nutsuwar dole.
Sunkuyawa Hajiya Saudatu tayi kamar Mai sujada sannan ta fara rafka mishi kirari Kai da kaji kasan tsuran sa6o ne kawai da barin Kan tafarkin Allah (S.W.A) *Allah ya tsare Mana imaninmu ameen*
Ganin yanda ta durk'ushe yasa Suma suka yi, shi Kuma ya hau yashe hak'ora Yana fad'in
" buk'atar ku ta biya"
D'agowa sukayi Nan ya dube su duka yace " nasan damuwarku"
nuna Mummy yayi yacigaba da cewa " ke akan abokiyar zamanki da Kuma mijinki ne, Amma kashetan da kikeso kiyi bazai yuwa yanzu ba, farkon abunda zakiyi shine shiga tsakaninta da mijinki ya Dena Kula ta"
Da sauri a razane Mummy ta dube shi jin abunda yace, maimaita wa take a ranta, gyad'a Kai yayi yace" hak'ika Yana kula ta Dan Nan bada dad'ewa ba Zaki ga sakamakon had'uwar da suke Nanda wasu 'yan watanni"
Cikin rashin fahimta Mummy tace" wani irin sakamako kenan?"
Girgiza Kai yayi yace" ba a bani Daman fad'an hakan ba, Amma inkika bi hanyoyin da na fad'a Miki ke da kanki Zaki fahimta abunda nake nufi"
Da sauri tace " ayi duk abunda ya Dace boka"
Seda ya gama wasu dube duben shi sannan sukaga an cillo wa kowa k'ulli gaban su, Mummy ya fara kallo yace" wannan k'ullin ki nemi inda kikasan ko yaushe Yana tsallakawa ki binne a wajan, wannan garin Kuma ki barbad'a mishi a abinci daga 'yar har uwar zai tsanesu, wannan Kuma inkin fara al'ada ki kwa6a da jini ki sake tusawa a gaban ki, Kuma kisan duk hanyar da zakibi ya yi kwanciyar aure dake lokacin buk'atar ki ta gama biya sai Kuma ta gaba"
Nan dukansu ya musu bayani, murna ne fal zuciyar Mummy Nan ta kwaso bunch na dubu d'add'aya guda uku ta dire mishi.
Nan suka fice suka d'au hanya, duk tsoron hanya da Mummy keyi duk sai taji ya kau, gudu kawai suke zabgawa lokacin har an dad'e da idar da sallar isha'i, sun k'ure kid'a irinna 'yan matan bariki sai shewa suke, Basu Ankara ba suka hango wash manyan mutane kowannen su d'auke da......
For comments 0814493230
Advertisement
- In Serial14 Chapters
The Broken System
What will you do if you go to a new world and face the thing you have never expected before? What will you do if you are just a guinea pig in a stasis pod? Or your loved one was killed, right in front of you? Or you traded as a slave to the point you wished you just die? Is it reality or just another nightmare? how it can be so vivid? ...LoadingTHE BROKEN SYSTEM
8 119 - In Serial42 Chapters
The Lone Prospect
New rules. New girl. New home. Ex-military and werewolf, Gideon Vonrothe is looking for a place to belong. His first and last hope for a pack to call his own is the Heaven’s Heathen’s Motorcycle Club. Being the new prospect isn’t going to be easy. Rebels with a cause, the members of the Heaven’s Heathens motorcycle club regularly risk life and limb to rescue those in need, all to protect their greatest secret, that they’re all werewolves. Now a new member has petitioned to join the pack… The Heaven’s Heathens are supposed to be a big bad motorcycle club, a brethren of tough as nails hard asses. Formed out of necessity after the Cascading War, the Heaven’s Heathens have the reputation of being the toughest sons of bitches in Colorado. Their membership filled with those that have little use for society’s rules and pay lip service to laws outside their own. Insular and hierarchal, a new member can throw off the entire group. And they’re Gideon VonRothe’s last hope for a life that feels familiar or else he’s resigned to go back to the family farm. He doesn’t know anything about the Heathens, or motorcycle clubs. He doesn’t even own a motorcycle. An outsider, ex-military and unsuspecting sucker, Gideon is the latest victim of the Club’s brotherhood appeal. Vice President Savannah Barker knows better. The Club is a bunch of party loving, thrill seeking adrenaline junkies with a nose for mischief. Their idea of playing hard is a good brawl and involves the words trigger happy lunatics. Her Grandfather, Brand, President of the Club is the worst of the lot. It’s the officers’ jobs to keep the rest of the world from find out that they’re more than a group that loves motorcycles and explosions. They’re werewolves. The Club is the pack and the pack is a family with siblings that squabble. Their outlet is Heaven Has Mercy, private security for hire. No wars. No assassinations. Before the new prospect can change the rankings, Brand sends the ignorant Gideon on a rescue mission under the supervision of Savannah and her team. Soon the bets are flying on if Gideon has what it takes and how long this lone prospect is going to last. The routine snag and drag turns complicated when it turns out the client lied, and an attack on their home turf makes some believe that the new Prospect is involved. The Heathen’s have a responsibility to the man they rescued and their reputation is on the line. Is this a new beginning or the beginning of the end for the Heaven’s Heathens?
8 184 - In Serial78 Chapters
The Golden Princess
The Third Princess Renner Theiere Chardelon Ryle Vaiself is one of the treasures of Re-Estize; The Golden Princess herself. She is also a calculating psychopath, tactful manipulator, and rotten to the core. Follow her, her lover and obsession Climb, and the scheming nobles of the Kingdom as she plots a secure and quiet life for her future. This is an Overlord / オーバーロード fanfiction.
8 430 - In Serial15 Chapters
The Aspect of Fire
Wilhelm woke up and was immediately confused, even before he opened his eyes. Through some twist of fate the data-entering grunt was pulled into another world, one containing terrifying people wielding magic powers beyond what he thought possible, and - somehow comparatively less horrifying - actual monsters. The only saving grace is that through his transference, he has become one of those terrifying people, and he's not sure how he feels about it yet. Oh, and he landed on a boat. Branded a Sylum for the way others unlucky enough to be pulled across the fabric of space tended to go insane after arrival, he will need to navigate a land unlike his own in seemingly every way except for the flaws, all while attempting to maintain his morality, and more importantly, his sanity. With his crew at his side and disconcertingly dangerous magic proportionate to his physical ability, it will not be easy.
8 142 - In Serial7 Chapters
LARRY STYLISON FROM THE BEGINNING
This story is about how harry and louis first meet at the xfactor and that they start to get feelings for each other what do you think will happen will they tell each other their feelings for each other or stay secret for a while
8 71 - In Serial28 Chapters
DERAILED✔️
Nadia Suleiman modibbo is who you can define as a beautiful, shy, loving and caring young lady with a painful past.What happens when she's thrown into a conditioned marriage with the arrogant Abdallah Ahmad who is a successful young CEO and also the only son to one of the most powerful politician in the country.04/05/2014 is the day Nadia's life took an abrupt turn. what happens when she finds out that Abdallah might be related to her past?Secrets will be revealed, hidden truths will be unravelled, but will love still prevail?DERAILEDBy@zinat Abdulkadir ✍️📖Highest rankings#1in Arewa#1 in Hausafulani.#1 in Abdallah.#2 in Nadia#3 in Deen.#3 in painful memories.
8 211

