《HASEENAH》PAGE 13&14
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
story nd written
by👇🏻
Aysher Abbakar (Meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
follow me on wattpad @Aysherabbakar
*long live pml*
*Dan Allah masu min magana ta private kan cewa in tura musu littafina daga farko suyi hak'uri suna tanbaya a group, in basu samu ba sannan sumin magana, wallahi tura novel daga farko yafimin typing wahala, nagode sossai Allah bar zumunci*
*Meerah novels group 1 nagode sossai da soyayyarku gareni Allah bar k'auna, ina yinku sossai da sossai, meerah heart u guys*
*13-14*
A hankali ta d'ago da idanuwanta dake faman mata zogi dan ganin waye, Haseen ta gani tsaye da farin handkerchief a hanunshi yana mik'a mata, ba musu ta amsa ta fara goge fuskarta.
tsugunawa yayi gaban ta sannan ya fara mata magana kamar haka " kiyi hak'uri ko ban tanbayeki ba nasan aikin mummy ce, ki k'ara hak'uri kan wanda kike yi, komai na duniya me wucewa ne, babu abunda yake tabbata banda ikon Allah, bazan hanaki kuka ba, nasan shi kad'ai ne ze rage miki zogi da rad'ad'in da kikeji, amma dan Allah ki rik'a ragewa kar ya zama miki damuwa kinji?"
gyad'a Mishi kai tayi ba tareda tace komai ba.
nan yace ta mik'e suje chemist a mata dressing d'in wajan.
cikin gida ta wuce tana d'ingisawa ta shiga ciki dan d'auko mayafin ta.
a wajan ta dawo ta sameshi, nan suka shiga mota suka fice a gidan, seda aka mata alluran TT saboda kwalbar sannan aka dressing k'afarta da goshin ta sannan aka bata anti biotics aka sallamesu suka kamo hanyar gida.
a tare suka nufo cikin palour, salatin da Mummy take yine yasasu tsayawa dukansu, dubansu tayi dukansu sannan ta kalli Haseen tace" gidan uban wa ta d'aukeka ta kaika?"
Advertisement
mamakine ya kama Haseen wato bama shi ya d'auketa ba itace ta d'auke shi.
d'aga murya tayi ta nufosu ta dubi Haseenah tace " dan ubanki bakiji abunda nake fad'i bane? nace gidan uban wa kika kaimun d'a?"
tsoro ne ya kama Haseenah nan ta fara 6ari, nufota Mummy tayi da nufin dukan ta, Haseen ne ya sha gabanta yace " haba Mummy, kiga jikin yarinyar nan duk rauni in baki tausaya mata ba ai bazaki k'ara mata ba"
" eh lallai fa, ka kare ta mana, saboda kar ka zagayo da daddare ta hanaka shiga ko? dan iska mara mutunci fetsararre"
tunda Haseen yake ranshi bai ta6a 6aci irinna yau ba, ba abunda ya tsana illa k'azafi, lokaci d'aya idonshi ya kad'a yayi ja, wani mummunan 6acin rai ya ziyarci zuciyarshi, hanunshi da k'afanshi ya hau rawa, ji yake kamar ya kifar da Mummy a wajan saboda 6acin rai, dubanshi Mummy tayi tace " ka bigeni mana da wannan rawar jikin da kake isheshshe, bigeni nace"
lokacin Saratu ta fito daga kitchen d'auke da plate ta yanyanka fruits, isowa wajansu tayi tace " Mummy ina ya kaita wai?"
"yawon iskancin su mana Saratu, inba hakanba ina zasuje da wannan uwar ranan?"
salati Saratu ta kama na munafurci tace" haba yaya Haseen yaushe ka fara bin k'azaman mata? ni wlhy ban....
bata k'arasa ba Haseen ya kife Saratu da wani wawan mari seda ta hantsila ta kifa a gefe, plate d'in hanunta ya fad'i gefe ya tarwatse, baiyi wata-wata ba ya bita da bugu ta ko ina, ihu take tana neman d'auki, Mummy kuwa kururuwa take tana janyoshi tana dukanshi, amma ko sauraronta beyi ba dukan Saratu yake sai kace mai fad'a da sa'ar shi, ganin yana neman hallaka mata 'ya ne ya sata fita da gudu tana k'wallawa mai gadi da driver kira.
Advertisement
da gudu suka nufota ganin yanda ta birkice ko d'an kwali babu akanta, ba abunda take cewa illa " zai kashe ta" tana nuna musu hanyar palour.
da sauri suka shiga dan ganin abunda ke faruwa, lokacin Saratu ko ihun bata iya wa, da k'yar suka ja Haseen suka fito dashi, Mummy kuwa sai kunduma ma iyayenshi ashar take, kallon Mummy yayi kawai yayi k'wafa ya fice, a saba'in ya figi motarshi ya fice a gidan.
ganin haka yasa Haseena sulalewa tayi side d'insu ta mai da k'ofa ta datse dan tasan in tsautsayi yasa ta fitowa yau to sunanta marigayiya.
da gudu Mummy ta nufa Saratu dake kwance shame-shame tana wayyo hanuna wayyo k'afata.
likita Mummy ta kira, nan ya iso ya fara duba ta, targad'e ne hanu da k'afa, da k'yar ta tsaya aka gyara ya nad'e wajan da bandage, nan danan zazza6i ya rufe ta, ya bata magunguna sannan ya tafi.
huci kawai Mummy keyi tama rasa wani mataki zata d'auka kan Haseen.
wayarta ta zaro ta danna numbar k'anwar tata wato Mum Haseen, bugu biyu ta d'aga da fara'arta ta fara fad'in " yaya kardai kicemun aikin malamin nan yayi, an dace knan ko yaya"
Mum Haseen bata ankara ba taji Mummy tace " an dace da uwarki ko? saboda tsabar rashin tarbiya na d'anki, har gida yazo yayi yunk'urin kashemun yarinya kan wata karuwa, to wallahi daga ke harshi senayi maganinku"
tana kaiwa nan ta datse wayar, hankalin Mum Haseen ba k'aramin tashi yayi ba, mayafinta taja ta d'au makullin motarta ta d'au hanyar gidan Mummy.
da sauri-sauri ta shiga palour mum amma ba kowa banda k'aran AC da yake tashi.
hanyar bedroom d'inta ta nufa da niyar dubata ta can, muryar Mummy taji na fad'in " karki yarda ki shigamun d'aki,.ki kama hanya ki fitar a gida ynxu kinji na fad'a miki, inba so kike in rama dukan 'yata a kanki ba"
hak'uri Mum Haseen ta fara bata amma bata kula ta ba, sai ma shigewa da tayi ta barta nan tsaye, ganin haka yasa Mum Haseen rufa mata baya, ahankali ta shiga, Mummy ta hango zaune gefen Saratu ta zabga uban tagumi, yayinda ita kuma taketa rawar sanyi.
kuka Mummy ta fashe da shi ta kalli Mum Haseen tace" ki duba kiga cin mutuncin da Haseen yayi wa Saratu akan wancar yarinya, badan da maza a gidan nan ba wallahi kasheta yayi niyar yi"
cikin rashin fahimta Mum Haseen tace " wata yarinya kike magana ne kan Yaya?"
" wa kuwa inba Haseenah ba"
zaro ido waje tayi tace meya had'a Haseen da 'yar mak'iyarmu kuma ni Hajara?"
" ba fa wani abu bane, yawo ya d'auketa suka fita tun k'arfe biyu sai biyar suka shigo gidannan, dan kawai na tare su ina tanbaya ya hau rawa da jiki kaman zai bigeni, da Saratu tayi magana shine ya hauta da bugu ya huce akanta"
haushine ya kama Mum Haseen jin Mummy tace d'anta ne d'an iska, dan duk yanda ta kai ga rashin gaskiyarta ta san Haseen baya bin mata, ballan tana yabi Haseenah wanda da ganinta dukda son zuciyarsu tasan Haseenah bata yi kama da wannan yaran ba.
amma gudun 6acin ran Mummy yasa ta fara fad'a tana zage-zage, tana fad'in seta sa6a mishi kuma har nan zata sakoshi a gaba seya bada hak'uri, jin haka yasa Mummy ta fara saukowa.
seda ta tabbatar ta gama tsara Mummy sannan ta dubi Mummy tace" nikam yaya lauratu ya maganan maganin da boka ya baki? kin jaraba kuwa?"
harara Mummy ta zabga mata ta nuna Saratu da baki, nan suka fice a d'akin suka nufa bedroom d'in saratu.
Mummy ce ta dubeta tace"......
Advertisement
- In Serial14 Chapters
Heaven's Daughter
Every Immortal God in the Celestial Realm has to go through the stage of reincarnation into the human world at least once in their lives. The Celestial Emperor's daughter has always a been bookworm and has read countless of stories of the human world. This time, it is her turn to reincarnate and she is excited to experience it. What she does not know is that in the first reincarnation, memories are erased and she will live this life as a normal human with no prior memories of her life in the Celestial Realm. However, being the daughter of the Celestial Emperor and possessing a pure soul, Tian-er is naturally reborn into the human world with a high amount of karma. The result is that her ability (/power) thus grows at an astonishing fast rate. Watch as we follow the heaven's daughter - Tian-er as she travels in the human world as Zhao Zi Yue. This is a story for people who loves overpowered (OP) female main characters.
8 231 - In Serial9 Chapters
Yena
Yena never wished for the pressure from the status of being an awakened. She knew first-hand the hardships of the seemingly glamorous position and did everything she could to not walk that path. But when she find herself powerless with no means of escape, turning to her abilities is the only option Yena finds. Observe Yena as she grows stronger, protecting her family, discovering the mysteries of the system and unlocking the doctrines of the universe, finding out why her powers exist. Updates every Saturday 12:15 GMT
8 56 - In Serial23 Chapters
Scabbard
This is the tale of a man named Michael, or Mika for those who knew him in his last days. Michael was not a very interesting man, nor had a very interesting life, some would argue he didn't had a life at all, at least not up to the beginning of his journey on a strange new land. This is the story of how such a man helped shape a whole universe.
8 100 - In Serial13 Chapters
Another World's Trespasser
Is currently being rewritten : http://royalroadl.com/fiction/3164Once secluded from the rest of the world, working for the Phantom industries which leads in the development of technologies in the fields of medicine, agriculture, engineering and modern weaponry. The young and intelligent scientist Seth accidentally forces his way into another world after narrowly escaping death from the terrorists that launched a full scale assault against the main headquarters of Phantom industries.Come join his journey, as he sets off to find the reason behind the accidental transport and ultimately find his way back home.
8 136 - In Serial9 Chapters
langeweile
pupsfcvvvvvvvvvvv
8 124 - In Serial11 Chapters
TMNT X Reader Donnie [ complete ]
This is a TMNT x Reader your love in this story is Donnie. you get saved and spend time with his family learning a lot about your self. I try to update regularly hope you enjoy the story (030)
8 84

