《HASEENAH》PAGE 11&12
Advertisement
[7/6, 10:37 AM] 💄Meerah💋: 🌸 *HASEENAH*🌸
story nd written
by👇🏻
Aysher Abbakar (Meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
follow me on wattpad @Aysherabbakar
*long live pml*
*11-12*
girgiza kai Mummy tayi alamar 'kwafa sannan saratu ta dubeta tace " Mummy kigani harda wani rufe k'ofa?"
" ah duk makircin da suke k'ullawa Allah zai tona musu asari"
nan suka gama bambamin su suka kama hanya kowa tayi wajanta.
washe gari ma da wuri Haseenah ta gama aikinta, ta ajiye wa Umma komai na buk'ata ta saka uniform d'inta ta fito, harta fito sekuma ta dawo ta dubi Umma tace " Umma zan kulle k'ofar ta baya, inace ba abunda zaki buk'kata?"
gyad'a kai kawai Umma tayi dan ita bacci ma take ji, nan Haseenah ta fita tasa key ta kulle k'ofar.
tsaye kawai Mummy tayi tana kallon ikon Allah, har Haseenah zata wuce setaga Alamar mutum a tsaye, a razane ta juyo nan sukayi ido hud'u da Mummy, rusinawa tayi ta gaida Mummy, basar da gaisuwar Mummy tayi sannan ta dubeta tace " munafuki ko a ruwa yake sai yayi gumi, wani makircin kuke k'ullawa ne wai, uwar taki ina taje da kika kulle k'ofar?"
cikin sanyi tace " umm tana ciki bataje ko ina ba"
" to meye na kulle wajan? saboda kuna tare da mayu ko? to bani makullin"
ta k'arasa maganar tana mik'a hannu wa Haseenah, ja da baya Haseenah ta fara yi Mummy na binta.
sallamar Haseen ne yasa Mummy juyawa tana kallon shi, aiko nan Haseenah ta fita waje aguje , k'walla mata kira Mummy keyi amma ina itakam tayi nisa.
nan Mummy ta fara zage zage, Haseen ne yake tanbayarta meya faru, nan ta hau sababi tana fad'in " dan uban yarinyar nan har zata fice ta kulle k'ofar uwarta sekace zamu cinyeta, to wallahi yau sena ci ubanki a gidannan"
Advertisement
abun dariya ya bawa Haseen amma ya nok'e yace " to Mummy dan Allah meye dan sun kulle k'ofa sekace taki suka kulle?"
a zuciye ta dubeshi tace " zanci ubanka, ina ruwanka, wato kaima goyon bayansu kake ko? to wuce ka koma yanda ka fito bana buk'atar zamanka a gidannan"
dariya yayi yace" kefa Mummy halina dake masifa wallahi"
bata sake kulashi ba ta koma side d'inta, ya dad'e tsaye a wajan daga bisani shima ya kama hanya ya fita.
lokacin da aka tashi su Haseenah a makaranta ta dawo gida, tsayawa tayi a bakin gate tana lek'e ko zata ga Mummy, ganin ba kowa wajan ne yasa ta fara shiga da sand'a, harta kai bakin palour zata bud'e taji muryar Mummy na fad'in " sannu da dawowa shugaban munafukai"
gaban Haseenah ne ya shiga bugun tara-tara dan tasan yau me k'wacenta wajan Mummy sai Allah.
ahankali ta fara tafiya har ta kai wajan Mummy sannan ta tsuguna a gabanta, janyota Mummy tayi ta sake mata dundu a tsakiyar baya, ta had'a ta cakumo wuyar hijabinta kai kace dambe zatayi da sa'ar ta, wani wawan mari ta d'auketa dashi a jejjere guda uku, hanunta na rik'e da wuyarta sannan tace" ni sa'ar ubanki ne da zanna kiranki har ki kwasa da gudu?"
cikin kuka Haseenah ta fara girgiza kai, Mummy ta cigaba da cewa" ko zaki iya fad'a mun irin mugun halin da nake dashi da har zaki na kulle k'ofa sekace mayya?"
nan ma girgiza kai tayi, " wallahi na sake ganin haka ya faru kisa aranki na lahira seya fiki morewa, 'yar iskar banza karuwa"
tana gama fad'in haka ta wurga ta gefe, nan kanta ya bugu da centre table d'in tsakiyar palour, wani mummunan zafi ne ya ziyarce ta hakan ya sata sake wani irin ihu ta dafe wajan, jini tagani ya fara zuba hakan ya dad'a gigitata tana fad'in " wayyo Allah na"
Advertisement
ko ta kanta Mummy bata sake biba ta wuce abunta.
Umma ko a d'aki sai sharar k'walla takeyi aranta tunani take wai yaushe zasu samu sassauci daga wannan wulak'anci da cin mutuncin ne wai, wata gefe daga zuciyarta ta bata amsa da fad'in " randa kuka bar duniya"
haka Haseenah ta tashi da k'yar taja jiki ta kama hanyar palour, key ta lalumo ta bud'e k'ofar ta shige ciki, kai tsaye bedroom ta shige ta fad'a kan gado, lokaci d'aya ta saki wani irin kuka mai ban tausayi, ta kwashi kusan minti talatin tana yi, mik'ewa tayi ta shiga toilet ta bud'e wani d'an akwati.ta ciro bandage ta nad'a a goshinta, sannan tayi wanka ta d'auro alwala ta fito, da k'yar ta iya yin sallah saboda wani irin ciwon kan da yake damunta, fitowa tayi ta shige kitchen d'insu ta yi jelouf na sphagetti da kifi sannan ta juye a flask ta fito d'auke da plate da spoon a hanunta, wajan Umman ta ta wuce sannan ta zuba mata ta tura mata gabanta ta koma can gefe ta zauna, nan Umma tace tazo suci tare, ba musu taje suka fara ci, sunci da d'an yawa kuwa suna gamawa ta kwashe komai ta mayar kitchen ta yi wanke-wanke ta goge sannan ta fito.
zamanta knan taji Mummy na k'walla mata kira, da k'yar ta mik'e ta fice, a palour ta sameta suna zaune ita da saratu tana kwance kan cinyar ta, ahankali take tafiya zata isa wajan Mummy ba tare da ta kula ba ta taka wani abunda taji ya shige mata cikian k'afa, azabar da taji yanzu ya ninka na d'azu, tsugunawa tayi awajan nan taga fasassun kwalabe ne wanda ya fashe, jini tagani na zuba a k'afanta, ko sannu babu Mummy tace " ki dauko parker da moper ki tattara wannnan glasees d'in tumbler daya fashe sannan ki goge wajan"
d'an kwalin kanta ta cire ta yaga shi gida biyu tayi zaman dirshan a wajan sannan ta runtse idonta ta zaro kwalban daya shiga mata k'afa sannan ta d'aure da d'an kwalin, hawaye na xuba haka ta tattara komai ta goge.
zuciyarta wani irin zafi da zogi yake mata, maimakon tayi side d'insu kawai setayi hanyar fita daga palour, wajan parking lot d'insu tabi taje wajan flowers d'insu ta 6uya a bayan motar Abban ta ta had'a kai da gwiwa ta fashe da kukan bak'in ciki.
kuka take har kamar numfashin ta zau d'auke, idonta sun kad'a sunyi ja sun kumbura, ga bugun goshinta ga wani azaba a k'afarta.
kuka take tun muryarta na fita har ya dishe ta fara sambatu ita kad'ai sekace zararriya.
ganin inuwan mutum a gabanta yasata d'ago jajayen idonta dan ganin waye?......
for comments only 08144932304
Advertisement
- In Serial55 Chapters
The Terrarian's Reincarnation
Guy dies in his sleep and gets reincarnated into a fantasy world. Pretty standard stuff. Nope! The 'guy' is a Terraria player and the body he's reincarnated into is that of his endgame character. “Who needs a Hero’s Journey, I have a pink cat sword! And a whole bunch of resources! Imma build a house!” Warning - it may be a little slow paced, but it’ll speed up later on. This world and main character's abilities are partially based on Terraria, Copyright Re-Logic. Sexual Content tag is there so I have options open for the future.
8 300 - In Serial15 Chapters
Legacy (vrmmo game)
Is currently being rewritten. Darius is a guy with no friends because the friends of his friends don't like him and so he has no friends. Legacy, a vrmmo game, is the first of its kind to actually look like the fantasy games kids dream of. Darius gets the game, planning to just have fun and maybe get some friends. Unfortunately, he's the protagonist, so yeahhhh shit's gonna happen He chooses the mage class which is often ridiculed for its low health and high MP costs. And he somehow becomes the top player within the game... There is gonna be fucking profanity because books where the protagonist is like "fiddlesticks" when they fuck up are stupid and targeted at kids that haven't gone thru puberty yet. And yes, there will be gore. Otherwise what's the point of these games? The cover is not mine and I don't own it okay I just got it off one of those sites rate this if you feel like it
8 190 - In Serial20 Chapters
Timberlake Tales
Try being the daughter of Justin Timberlake and Britney Spears. Not as easy as you think it is. Read to follow Andrea Timberlake and her many adventures of life in the spotlight. Thanks to everyone who has read my stories!!
8 169 - In Serial24 Chapters
Infinite Wishes
Daniel Nelvine Rosecrown, cough cough, i mean Kimy Shinguru, is just your ordinary super hardcore gamer, leaving his home to the outside world in order to replenish his food supply for another streak of nonstop gaming, suddenly dies a harsh death by arrows, just to meet god, whom said he killed him on purpose, and refused to give him life again on earth. God needed to transfer him to another world for an unknown reason, and as compensation, would not only make him younger and more OP, but grant him one wish, any wish. I truly do wonder what Kimy wished for...
8 231 - In Serial16 Chapters
hoodshii- Notti Osama
where a girl who was once from sugarhill , returns to see her brothers & meets her lover.
8 139 - In Serial22 Chapters
New Roommate
COMPLETED 😌💛Jake and the boys moved back to the Traphouse and they had one more empty room. Jake asked his childhood friend Y/N to move in. She agreed and moved in right away. Colby: what's the new girls name again?(This will contain screenshots of fake convos and IG posts. This story is already posted and finished on my IG)#1 on Colbybrockfan #2 on colbybrock
8 199

