《HASEENAH》PAGE 11&12
Advertisement
[7/6, 10:37 AM] 💄Meerah💋: 🌸 *HASEENAH*🌸
story nd written
by👇🏻
Aysher Abbakar (Meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
follow me on wattpad @Aysherabbakar
*long live pml*
*11-12*
girgiza kai Mummy tayi alamar 'kwafa sannan saratu ta dubeta tace " Mummy kigani harda wani rufe k'ofa?"
" ah duk makircin da suke k'ullawa Allah zai tona musu asari"
nan suka gama bambamin su suka kama hanya kowa tayi wajanta.
washe gari ma da wuri Haseenah ta gama aikinta, ta ajiye wa Umma komai na buk'ata ta saka uniform d'inta ta fito, harta fito sekuma ta dawo ta dubi Umma tace " Umma zan kulle k'ofar ta baya, inace ba abunda zaki buk'kata?"
gyad'a kai kawai Umma tayi dan ita bacci ma take ji, nan Haseenah ta fita tasa key ta kulle k'ofar.
tsaye kawai Mummy tayi tana kallon ikon Allah, har Haseenah zata wuce setaga Alamar mutum a tsaye, a razane ta juyo nan sukayi ido hud'u da Mummy, rusinawa tayi ta gaida Mummy, basar da gaisuwar Mummy tayi sannan ta dubeta tace " munafuki ko a ruwa yake sai yayi gumi, wani makircin kuke k'ullawa ne wai, uwar taki ina taje da kika kulle k'ofar?"
cikin sanyi tace " umm tana ciki bataje ko ina ba"
" to meye na kulle wajan? saboda kuna tare da mayu ko? to bani makullin"
ta k'arasa maganar tana mik'a hannu wa Haseenah, ja da baya Haseenah ta fara yi Mummy na binta.
sallamar Haseen ne yasa Mummy juyawa tana kallon shi, aiko nan Haseenah ta fita waje aguje , k'walla mata kira Mummy keyi amma ina itakam tayi nisa.
nan Mummy ta fara zage zage, Haseen ne yake tanbayarta meya faru, nan ta hau sababi tana fad'in " dan uban yarinyar nan har zata fice ta kulle k'ofar uwarta sekace zamu cinyeta, to wallahi yau sena ci ubanki a gidannan"
Advertisement
abun dariya ya bawa Haseen amma ya nok'e yace " to Mummy dan Allah meye dan sun kulle k'ofa sekace taki suka kulle?"
a zuciye ta dubeshi tace " zanci ubanka, ina ruwanka, wato kaima goyon bayansu kake ko? to wuce ka koma yanda ka fito bana buk'atar zamanka a gidannan"
dariya yayi yace" kefa Mummy halina dake masifa wallahi"
bata sake kulashi ba ta koma side d'inta, ya dad'e tsaye a wajan daga bisani shima ya kama hanya ya fita.
lokacin da aka tashi su Haseenah a makaranta ta dawo gida, tsayawa tayi a bakin gate tana lek'e ko zata ga Mummy, ganin ba kowa wajan ne yasa ta fara shiga da sand'a, harta kai bakin palour zata bud'e taji muryar Mummy na fad'in " sannu da dawowa shugaban munafukai"
gaban Haseenah ne ya shiga bugun tara-tara dan tasan yau me k'wacenta wajan Mummy sai Allah.
ahankali ta fara tafiya har ta kai wajan Mummy sannan ta tsuguna a gabanta, janyota Mummy tayi ta sake mata dundu a tsakiyar baya, ta had'a ta cakumo wuyar hijabinta kai kace dambe zatayi da sa'ar ta, wani wawan mari ta d'auketa dashi a jejjere guda uku, hanunta na rik'e da wuyarta sannan tace" ni sa'ar ubanki ne da zanna kiranki har ki kwasa da gudu?"
cikin kuka Haseenah ta fara girgiza kai, Mummy ta cigaba da cewa" ko zaki iya fad'a mun irin mugun halin da nake dashi da har zaki na kulle k'ofa sekace mayya?"
nan ma girgiza kai tayi, " wallahi na sake ganin haka ya faru kisa aranki na lahira seya fiki morewa, 'yar iskar banza karuwa"
tana gama fad'in haka ta wurga ta gefe, nan kanta ya bugu da centre table d'in tsakiyar palour, wani mummunan zafi ne ya ziyarce ta hakan ya sata sake wani irin ihu ta dafe wajan, jini tagani ya fara zuba hakan ya dad'a gigitata tana fad'in " wayyo Allah na"
Advertisement
ko ta kanta Mummy bata sake biba ta wuce abunta.
Umma ko a d'aki sai sharar k'walla takeyi aranta tunani take wai yaushe zasu samu sassauci daga wannan wulak'anci da cin mutuncin ne wai, wata gefe daga zuciyarta ta bata amsa da fad'in " randa kuka bar duniya"
haka Haseenah ta tashi da k'yar taja jiki ta kama hanyar palour, key ta lalumo ta bud'e k'ofar ta shige ciki, kai tsaye bedroom ta shige ta fad'a kan gado, lokaci d'aya ta saki wani irin kuka mai ban tausayi, ta kwashi kusan minti talatin tana yi, mik'ewa tayi ta shiga toilet ta bud'e wani d'an akwati.ta ciro bandage ta nad'a a goshinta, sannan tayi wanka ta d'auro alwala ta fito, da k'yar ta iya yin sallah saboda wani irin ciwon kan da yake damunta, fitowa tayi ta shige kitchen d'insu ta yi jelouf na sphagetti da kifi sannan ta juye a flask ta fito d'auke da plate da spoon a hanunta, wajan Umman ta ta wuce sannan ta zuba mata ta tura mata gabanta ta koma can gefe ta zauna, nan Umma tace tazo suci tare, ba musu taje suka fara ci, sunci da d'an yawa kuwa suna gamawa ta kwashe komai ta mayar kitchen ta yi wanke-wanke ta goge sannan ta fito.
zamanta knan taji Mummy na k'walla mata kira, da k'yar ta mik'e ta fice, a palour ta sameta suna zaune ita da saratu tana kwance kan cinyar ta, ahankali take tafiya zata isa wajan Mummy ba tare da ta kula ba ta taka wani abunda taji ya shige mata cikian k'afa, azabar da taji yanzu ya ninka na d'azu, tsugunawa tayi awajan nan taga fasassun kwalabe ne wanda ya fashe, jini tagani na zuba a k'afanta, ko sannu babu Mummy tace " ki dauko parker da moper ki tattara wannnan glasees d'in tumbler daya fashe sannan ki goge wajan"
d'an kwalin kanta ta cire ta yaga shi gida biyu tayi zaman dirshan a wajan sannan ta runtse idonta ta zaro kwalban daya shiga mata k'afa sannan ta d'aure da d'an kwalin, hawaye na xuba haka ta tattara komai ta goge.
zuciyarta wani irin zafi da zogi yake mata, maimakon tayi side d'insu kawai setayi hanyar fita daga palour, wajan parking lot d'insu tabi taje wajan flowers d'insu ta 6uya a bayan motar Abban ta ta had'a kai da gwiwa ta fashe da kukan bak'in ciki.
kuka take har kamar numfashin ta zau d'auke, idonta sun kad'a sunyi ja sun kumbura, ga bugun goshinta ga wani azaba a k'afarta.
kuka take tun muryarta na fita har ya dishe ta fara sambatu ita kad'ai sekace zararriya.
ganin inuwan mutum a gabanta yasata d'ago jajayen idonta dan ganin waye?......
for comments only 08144932304
Advertisement
- In Serial51 Chapters
A Poor Day For Digging Graves
A graveyard is no place to raise a child, yet raised there Caj Donovan was. Despite his noble birth, despite his parents’ innocence of any crime, he was orphaned not long after birth by order of the King. The King's Executioner has been dirtying his hands with politics that he has no business in. The King's Executioner is gambling for power. When his game takes everything from Caj a second time, the young undertaker realizes that if he wants to stop the madman, he will have to beat him at his own game.
8 130 - In Serial14 Chapters
The Challenge of Erros
The story follows the adventures of Darren Murphy and his ward Rhea as they combat against the mysteries of the world they live in. They travel the world of Artegen without knowing the plot they are involved in.
8 170 - In Serial47 Chapters
Shadow of Steel
Purple. Persecuted. Poisoned. Saya was a poor teenager raising her family on a farm. She knowingly poisoned herself by choosing the dangerous job of picking Malvaos, mysterious purple fruits. The greater the danger, the better the pay. Picking Malvaos for five years turned her purple. Ever since she got her hands on a broken purple staff, weirder and stranger things have happened. So much happened that she questioned if things would ever go back to normal again. She journeyed back to her hometown, Steel, Michigan, where nothing was the same. Adding to the mess that the new human inhabitants created, the Orcs were trying to take over the town. There was no way to turn it back to how it was but she was determined to fight for Steel, for humankind. Being purple isolated and hardened her but it gave her extra power. With the help of a Tengu, new friends, suspicious elves, and naughty fairies, she would learn how to use her powers to battle the Orcs. Unintentionally, it's like "Percy Jackson" meets "Stranger Things."
8 199 - In Serial9 Chapters
Bones
Raised from the dead by a master necromancer, the skeleton had no memories. Worse off, his master was killed by a visiting wyvern the very next moment. Now, confused and uncertain, his obligation gone, he wandered. Wandering, seeking for his purpose, all the while encountering all sorts of creatures. The reason why he was born into this world.
8 75 - In Serial12 Chapters
My Life As A Fire Hero!
Hayato is an ordinary schoolboy.....Until he and his friends got summoned to another world! They now act as the guardians of that world and they must take down the 10 leaders of evil!
8 118 - In Serial12 Chapters
Freshman
Jisung is a freshman at university. His friend Chan introduces him to his friends, among whom there is an intriguing boy, Minho.___This is my first story and English isn't my native language, so I'd be really happy to have your feedback. Thanks for reading ^^
8 82

