《HASEENAH》PAGE 11&12
Advertisement
[7/6, 10:37 AM] 💄Meerah💋: 🌸 *HASEENAH*🌸
story nd written
by👇🏻
Aysher Abbakar (Meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
follow me on wattpad @Aysherabbakar
*long live pml*
*11-12*
girgiza kai Mummy tayi alamar 'kwafa sannan saratu ta dubeta tace " Mummy kigani harda wani rufe k'ofa?"
" ah duk makircin da suke k'ullawa Allah zai tona musu asari"
nan suka gama bambamin su suka kama hanya kowa tayi wajanta.
washe gari ma da wuri Haseenah ta gama aikinta, ta ajiye wa Umma komai na buk'ata ta saka uniform d'inta ta fito, harta fito sekuma ta dawo ta dubi Umma tace " Umma zan kulle k'ofar ta baya, inace ba abunda zaki buk'kata?"
gyad'a kai kawai Umma tayi dan ita bacci ma take ji, nan Haseenah ta fita tasa key ta kulle k'ofar.
tsaye kawai Mummy tayi tana kallon ikon Allah, har Haseenah zata wuce setaga Alamar mutum a tsaye, a razane ta juyo nan sukayi ido hud'u da Mummy, rusinawa tayi ta gaida Mummy, basar da gaisuwar Mummy tayi sannan ta dubeta tace " munafuki ko a ruwa yake sai yayi gumi, wani makircin kuke k'ullawa ne wai, uwar taki ina taje da kika kulle k'ofar?"
cikin sanyi tace " umm tana ciki bataje ko ina ba"
" to meye na kulle wajan? saboda kuna tare da mayu ko? to bani makullin"
ta k'arasa maganar tana mik'a hannu wa Haseenah, ja da baya Haseenah ta fara yi Mummy na binta.
sallamar Haseen ne yasa Mummy juyawa tana kallon shi, aiko nan Haseenah ta fita waje aguje , k'walla mata kira Mummy keyi amma ina itakam tayi nisa.
nan Mummy ta fara zage zage, Haseen ne yake tanbayarta meya faru, nan ta hau sababi tana fad'in " dan uban yarinyar nan har zata fice ta kulle k'ofar uwarta sekace zamu cinyeta, to wallahi yau sena ci ubanki a gidannan"
Advertisement
abun dariya ya bawa Haseen amma ya nok'e yace " to Mummy dan Allah meye dan sun kulle k'ofa sekace taki suka kulle?"
a zuciye ta dubeshi tace " zanci ubanka, ina ruwanka, wato kaima goyon bayansu kake ko? to wuce ka koma yanda ka fito bana buk'atar zamanka a gidannan"
dariya yayi yace" kefa Mummy halina dake masifa wallahi"
bata sake kulashi ba ta koma side d'inta, ya dad'e tsaye a wajan daga bisani shima ya kama hanya ya fita.
lokacin da aka tashi su Haseenah a makaranta ta dawo gida, tsayawa tayi a bakin gate tana lek'e ko zata ga Mummy, ganin ba kowa wajan ne yasa ta fara shiga da sand'a, harta kai bakin palour zata bud'e taji muryar Mummy na fad'in " sannu da dawowa shugaban munafukai"
gaban Haseenah ne ya shiga bugun tara-tara dan tasan yau me k'wacenta wajan Mummy sai Allah.
ahankali ta fara tafiya har ta kai wajan Mummy sannan ta tsuguna a gabanta, janyota Mummy tayi ta sake mata dundu a tsakiyar baya, ta had'a ta cakumo wuyar hijabinta kai kace dambe zatayi da sa'ar ta, wani wawan mari ta d'auketa dashi a jejjere guda uku, hanunta na rik'e da wuyarta sannan tace" ni sa'ar ubanki ne da zanna kiranki har ki kwasa da gudu?"
cikin kuka Haseenah ta fara girgiza kai, Mummy ta cigaba da cewa" ko zaki iya fad'a mun irin mugun halin da nake dashi da har zaki na kulle k'ofa sekace mayya?"
nan ma girgiza kai tayi, " wallahi na sake ganin haka ya faru kisa aranki na lahira seya fiki morewa, 'yar iskar banza karuwa"
tana gama fad'in haka ta wurga ta gefe, nan kanta ya bugu da centre table d'in tsakiyar palour, wani mummunan zafi ne ya ziyarce ta hakan ya sata sake wani irin ihu ta dafe wajan, jini tagani ya fara zuba hakan ya dad'a gigitata tana fad'in " wayyo Allah na"
Advertisement
ko ta kanta Mummy bata sake biba ta wuce abunta.
Umma ko a d'aki sai sharar k'walla takeyi aranta tunani take wai yaushe zasu samu sassauci daga wannan wulak'anci da cin mutuncin ne wai, wata gefe daga zuciyarta ta bata amsa da fad'in " randa kuka bar duniya"
haka Haseenah ta tashi da k'yar taja jiki ta kama hanyar palour, key ta lalumo ta bud'e k'ofar ta shige ciki, kai tsaye bedroom ta shige ta fad'a kan gado, lokaci d'aya ta saki wani irin kuka mai ban tausayi, ta kwashi kusan minti talatin tana yi, mik'ewa tayi ta shiga toilet ta bud'e wani d'an akwati.ta ciro bandage ta nad'a a goshinta, sannan tayi wanka ta d'auro alwala ta fito, da k'yar ta iya yin sallah saboda wani irin ciwon kan da yake damunta, fitowa tayi ta shige kitchen d'insu ta yi jelouf na sphagetti da kifi sannan ta juye a flask ta fito d'auke da plate da spoon a hanunta, wajan Umman ta ta wuce sannan ta zuba mata ta tura mata gabanta ta koma can gefe ta zauna, nan Umma tace tazo suci tare, ba musu taje suka fara ci, sunci da d'an yawa kuwa suna gamawa ta kwashe komai ta mayar kitchen ta yi wanke-wanke ta goge sannan ta fito.
zamanta knan taji Mummy na k'walla mata kira, da k'yar ta mik'e ta fice, a palour ta sameta suna zaune ita da saratu tana kwance kan cinyar ta, ahankali take tafiya zata isa wajan Mummy ba tare da ta kula ba ta taka wani abunda taji ya shige mata cikian k'afa, azabar da taji yanzu ya ninka na d'azu, tsugunawa tayi awajan nan taga fasassun kwalabe ne wanda ya fashe, jini tagani na zuba a k'afanta, ko sannu babu Mummy tace " ki dauko parker da moper ki tattara wannnan glasees d'in tumbler daya fashe sannan ki goge wajan"
d'an kwalin kanta ta cire ta yaga shi gida biyu tayi zaman dirshan a wajan sannan ta runtse idonta ta zaro kwalban daya shiga mata k'afa sannan ta d'aure da d'an kwalin, hawaye na xuba haka ta tattara komai ta goge.
zuciyarta wani irin zafi da zogi yake mata, maimakon tayi side d'insu kawai setayi hanyar fita daga palour, wajan parking lot d'insu tabi taje wajan flowers d'insu ta 6uya a bayan motar Abban ta ta had'a kai da gwiwa ta fashe da kukan bak'in ciki.
kuka take har kamar numfashin ta zau d'auke, idonta sun kad'a sunyi ja sun kumbura, ga bugun goshinta ga wani azaba a k'afarta.
kuka take tun muryarta na fita har ya dishe ta fara sambatu ita kad'ai sekace zararriya.
ganin inuwan mutum a gabanta yasata d'ago jajayen idonta dan ganin waye?......
for comments only 08144932304
Advertisement
- In Serial10 Chapters
Kyrio's Monster House (Dropped)
A man dies, gets a second chance by a random god and decides to play god. Note: Most chapters are in Alpha version, that means some grammar mistakes and missing tables.
8 147 - In Serial39 Chapters
The Bird and the Fool
Kesil is stranded very far indeed from his home. Despite a gift from the fair folk that allows him to understand and speak any language, he has very little idea of what’s going on around him (though he likes to pretend he does). But this doesn’t stop him from getting into trouble in the port city of Edazzo, in the ancient empire of Duri, and elsewhere, doing his best to find love, escape snares of ancient magic, and hopefully return home in the end.
8 71 - In Serial11 Chapters
World Conqueror
Imagine there is a world other then the world we know. Imagine in this world things happen which you wouldn´t understand in our world. Imagine in this world there is no daily danger because the USA and Russia might start a atomic war. And now imagine in this world there exists magic, what would you do? would you go insane and slaughter everybody on your way to power or would you remain silent and start training and in seclusion to get the power you want to slaughter everybody that harassed in that time with your newly gained power? Maybe you want to create a family and life happy until you die and let nobody know that you are a powerful being. In this world a baby is born into a happy and easy life, his family thinks he is a genuis after he gets 3 years old but why and why does he need to leave his family at age of 6? **************************************************************************************** In this story may be gore,sex,slavery and torture ~Dropped~
8 107 - In Serial25 Chapters
Sacrificed in Thirty Seconds
A somewhat unusual reincarnation story, where the main character is thrown into a new world and tries to survive. It is a combination of survival/adventure. I wrote it as a fast-paced, action driven story. If you like slice of life, or extensive descriptions, it is probably not for you. This is my first book here, I will not remove it, but do not expect anything special.
8 54 - In Serial35 Chapters
Here
⚠️ MATURE⚠️ This story contains strong use of language and mature scenes. If you are offended easily do not read. ________________________________________________I felt something tug my hair behind my ear and I snuggled my head deeper into the pillow. Suddenly I felt someone straddle my back. I gasped and my eyes flew open as I swung my hands forward to push myself up and whatever was on me off. I groaned as I fell back down to the heavy weight, someone was on top of me. The person grabbed my hands and held them above my head with a firm grip. "P-please let go of m-me" I choked out, tears starting to run down my face from fear. "You are so beautiful." A male voice whispered in my ear as he grabbed my bottom, squeezing it.I screamed but got cut off as he put his hand over my mouth, flipping my body around. He was now sitting on my middle section. He was wearing all black, I could tell that it was the man from earlier. He has a cloth mask on, opening for his eyes and mouth only. Cold brown eyes met my green ones and I whined in fear as he stayed deadly still, studying my face.My shirt had rode up past my belly button during the struggle and his eyes raked over my showing skin, lust filling them. I struggled, trying to move my legs and arms to get away but he was too strong. "If you scream again, I'm going to kill you." He growled. I groaned in response, tears running down my face. He slowly released his hand from my mouth and reached into his pocket pulling out a knife and zip tie. I figured that if I didn't scream I would want to die if this man took me so I did what I had to do. I let out a bloodcurdling scream loud enough to wake up the whole entire neighborhood.
8 81 - In Serial35 Chapters
3rd Generation OS Book
Different os,ts, fs on Kaira, Kairav and Akshara
8 161

