《HASEENAH》Page 7&8
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
story nd written
by👇🏻
Aysher Abbakar (Meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
follow me on wattpad @Aysherabbakar
*long live pml*
*7-8*
Aunty maimuna Mummy ta hango tsaye tana 'kare musu kallo, jikin Mummy ne ya hau tsuma saboda razanar da tayi, dan duk masifar Mummy to Aunty Maimuna tasha gaban ta, cikin 'karfin hali Mummy tace "ke kuma meya kawoki gidannan?"
ba tare da Aunty ta bata amsa ba ta 'karaso yanda suke ta janyo Saratu ta sharara mata mari sannan tace
" fansar marin 'yata da kikayi, kuma kikamun rashin kunya in mari uwarki"
shuru tayi ta rik'e kunci hawaye na zirara, Mummy ce ta fusata cikin tsiwa da tsawa da fara fad'in
" akanme zaki dake ta? ko kina tunanin ke kad'ai kika iya bala'i?"
dariya Aunty tayi sannan tace " ai ita Haseenar da kika sa aka bigeta baiwar uwar wani ko uban wani ce? da kike cewa ta cire kaya ta baki akwai sisin ki aciki ne? to inga uban da zai sake dukanta in k'yale"
ta duba Haseenah tace"wuce ki kama hanya ki tafi kafin in tattaka ki er banza me miskilancin tsiya da ruwan ciki, daga ke har uwarki na rasa wa kuka gado dan ba cikin danginmu ba"
sum sum Haseenah ta kama hanya ta fita, tana fita kuwa ta had'u da Haseen ya d'auketa ya ajiye ta a makaranta.
wunin ranan Mummy ta kasa sukuni tunda Aunty tazo, kai komo kawai take tsakanin palour da bedroom ta sak'a wancan ta kunce wannan duk mafita take nema wajan da zata d'au fansa akan Umma, ita yanzu burinta ta fitar da Umma a gidan ne ta salwantar da Haseenah.
Advertisement
can gefe kuwa Saratu ce take ta k'unk'uni kan marin da aka mata ita a dole Mommy taje ta rama mata.
ran Mommy ya dad'a 6aci jin k'ananan kukan da Saratu ke mata, hakan ya sanya daka matsa tsawa tace" wallahi in baki mun shuru ba senaci ubanki, shegiya da tun kafin zuwanta dakin ma Haseenah duka da ba.azo wannan fagen ba, gashi kinsa ancimun mutunci kan wa'yannan mayun mtwxxxx" taja tsuka ta barta wajan.
Aunty kuwa tana shiga wajan Umma nan ta tarar da ita zaune ta tasa abincin da Haseenah ta zuba mata ta zabga uban tagumi, nan itama ta hau ta da masifa kan shurun yayi yawa meyasa zata bari ana cutar da ita, ita dai Umma hak'uri tayita bata har ta samu ta sauko sannan suka fara tattaunawa.
'''WACECE HASEENAH'''
Haseenah 'ya ce ga Alhaji sani mai Atampa, Alhaji sani su uku ne a wajan mahaifiyarsu, maza biyu mata uku, Muhammad, sani, sai kuna autar su Hajiya Zuwaira, su 'yan asalin jihar Gombe ne, sun taso cikin wahalar rayuwa har Allah ya hore musu sukayi karatun boko cikin yardar Allah Alhaji sani ya had'u da ubangida na 'kwarai har shima ya samu ya bud'e mishi nashi shagon, haka Allah ya sanya mishi Albarka har ya fara fita kasashen k'etare yana shigo da yadika da Atampopi.
shiko Alhaji Muhammad wan shi karatu yayi na likitanci shima Alhmdlh.
Zuwaira kuwa auran wuri aka mata ta na da zama a Kano da yaranta uku.
wata rana Alhaji sani na zaune a shago wata matashiyar yarinya suka zo bara tare da wata dattijuwa, tunda ya 'daura idonshi kan yarinyar yaji ta kwanta mishi a rai, nan ya kudiri niyar taimaka musu, haka yayita bibiyarsu har ya gano gidan su da kuma asalinsu, nan ya hanasu fita bara ya ajiye musu komai wanda zasu buk'ata, nan har Allah yasa suka dai daita da wannan budurwa mai suna Hajara har Allah ya shige masa gaba aka d'aura musu aure, wannan budurwa ba wata bace kuwa illa mummy. anyi auransu da wata d'aya Allah yayiwa mahaifiyar mummy rasuwa.
Advertisement
Umma kuwa 'yar abokin baban Abba ce, saboda nutsuwa da hak'urin ta Mahaifin Abba yayi sha'awar had'a zuri'a da shi, lokacin da yayi magana da Abba bai fuskanci wata matsala ba nan aka fara maganar sa rana, lokacin da ya sanar da mummy kuma ba 'karamin tashin hankali ta d'aga ba tana fad'in gaba d'aya auran su shekara d'aya amma zaice ze mata kishiya, Abba ya rasa inda zaisa rayuwar shi, har 'yar rama ya farayi, ganin haka Hajiya Zuwaira wato 'kanwar Abba tazo har gida ta mata wankin babban bargo kuma tace inta ce zata musu rashin mutunci to angulu zata koma gidanta na tsamiya, jin haka ne yasa mummy ta saduda amma ta 'kudiri aniyar seta fitar da mummy kota tsiya kota arziki.
haka akayi biki aka gama komai amma Mummy ko lek'e babu tana 'kunshe a d'aki ita da 'kawayenta, wanda suke ta faman zugata da mata pampo kan karta kuskura da 'kuruciyar ta a cuceta, nan Mummy ta cika tayi fam.
bayan an watse Mummy ta tada rashin arziki, seda Abba yayi mata barazanar saki sannan ta hak'ura, kiran 'kanwar ta tayi a waya wato Mahaifiyar Haseen, nan ta d'auketa ta kaita wajan wani malami kan a salwantar da Umma, yace hakan bazai yuwu ba dan akwai tsari ajikinta sossai, Mummy ba wani yarda tayi ba nan 'kanwarta ta bata shawarar a mayar da Abba mijin tace, hakan kuwa akayi tunda ga lokacin sai abunda Mummy tace yakeyi, tsoronta yake kamar itace mahaifiyar shi.
da haka Mummy da Umma suka samu ciki a tare, duk wata hanya sunbi dan zubar da cikin amma abu ya gagara, haka har lokacin haihuwar su tayi, Mummy ce ta fara haihuwar saratu, bayan sati d'aya Umma ta Haifi Haseenah, nan Mummy ta hana Abba yin komai sai dangin Abba ne suka mata komai.
tun daga wannan lokacin Umma da d'iyarta suke cikin tsangwama da wahala, dan kafin Haseenah ta girma Umma ce kewa Mummy komai, haka suka taso a wahale har Haseenah ta fara wayo, tun tana aiki Mummy na dukanta har ta koya na dole, haka kuma har yanxu Umma ce kawai ta samu sauk'in aiki yanzu Haseenah take fama.
da Abba yayi yunk'urin 'daukar me aiki Mummy tace sam bata yarda ba ai ga Haseenah, ba yanda ya iya haka ya hak'ura.
wannan knan..
'''CIFABAN LABARI'''
ganin kai komo bazai fishe da Mummy ba yasa ta d'au waya ta kira k'anwar tata wato Mahaifiyar Haseen ta bata labarin abunda ya faru, nan ta hauta da bala'i wai zaman me take yi da bazata d'au mataki akan ta ba, da taga wayar bazai mata ba nan ta sanar da Mummy kan ta shirya gata nan zuwa.....
for comments only 08144932303
Advertisement
- In Serial15 Chapters
Calandoris
A guy who played a sci-fi VRMMORPG was thrown in another world. And no, the other world doesn't have game mechanics. Nothing serious. Occasional updates, when I feel like it. Mature content.
8 98 - In Serial10 Chapters
Duality
“Listen closely for this is our oldest tale… In the beginning there was peace and knowledge throughout our land… The creatures of old roamed these lands… Evil had yet to spread through our land… A rift in the very fabric of reality formed… The land burned and melted as the creatures stepped through… As the most advanced civilization… We took the mantle to combat… By the time we were able to gather half the world had already been lain bare… The war covered the once peaceful land in death and destruction… During this time humanity's greatest light arose…” Monologued the old man, red in the face from passionately spewing his praises of a past he had no part of. Written by two authors, this novel covers the tale of a pair of protagonists in a wuxia world. Oh, and maybe an isekai or two. Our goal with this project is to make an engaging and entertaining story, while making a good attempt at a somewhat realistic wuxia setting. We’re aware of the oxymoron…
8 194 - In Serial12 Chapters
Underground Laboratory: Secrets
Hyle Labs was a government-funded project. Camellia's father was hired to create human weapons of war and armor. Anything that would help Valier win his war. Raven was a test subject. A scientists child used to create a human soldier who would fight continuously. After everything was destroyed Camellia seeks answers for the deaths of so many people, while Raven wants nothing to do with what was left of the underground laboratory. Still, the two find themselves working together along with Curtis, Camellia's bodyguard to find answers. Answers that have a lot to do with test subject Rose and how she survived despite being unable to survive. And while they manage to catch Rose, she isn't so lenient about giving them answers, risking her own life and theirs to keep her lips sealed. however, finding out that her father may be part of the reason the facility was wrecked in such a manner has her asking more questions than she thought.
8 265 - In Serial90 Chapters
Hide and Aizawa
"Please forgive your foolish brother… My unfortunate Lil Sis." This is a story of regret from an older brother, who in his previous life became the greatest source of sadness for her half-sister. And in this life, he would dedicate himself to ensure that his half-sister is able to walk and shine brightly in this gloomy world. *****
8 132 - In Serial19 Chapters
Five Elements Academy: A Tale Of Magic
Six years ago, monsters appeared on earth, out of nowhere, destroying cities and causing chaos around the world. The human were able to fight back, their weapons barely being able to kill the monsters, who seemed to come out from a fantasy world. And, although the monsters got stronger day by day, the humans have gained the Mages. However, the mages weren't older then 12 when they were found about, normal kids who had gained magical powers. And now, the first school to train and teach magic was created. The Five Elements Academy!
8 113 - In Serial72 Chapters
The Emancipation of Rhaegar
The story of a bastard and a Prince and everyone in between. Image: Yennefer and witcher by /cathbotsman on @DeviantArt *Characters are not set to follow GRRMs plotline* No characters apart from original characters, places, objects or major plots belong to me.
8 219

