《HASEENAH》Page 7&8
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
story nd written
by👇🏻
Aysher Abbakar (Meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
follow me on wattpad @Aysherabbakar
*long live pml*
*7-8*
Aunty maimuna Mummy ta hango tsaye tana 'kare musu kallo, jikin Mummy ne ya hau tsuma saboda razanar da tayi, dan duk masifar Mummy to Aunty Maimuna tasha gaban ta, cikin 'karfin hali Mummy tace "ke kuma meya kawoki gidannan?"
ba tare da Aunty ta bata amsa ba ta 'karaso yanda suke ta janyo Saratu ta sharara mata mari sannan tace
" fansar marin 'yata da kikayi, kuma kikamun rashin kunya in mari uwarki"
shuru tayi ta rik'e kunci hawaye na zirara, Mummy ce ta fusata cikin tsiwa da tsawa da fara fad'in
" akanme zaki dake ta? ko kina tunanin ke kad'ai kika iya bala'i?"
dariya Aunty tayi sannan tace " ai ita Haseenar da kika sa aka bigeta baiwar uwar wani ko uban wani ce? da kike cewa ta cire kaya ta baki akwai sisin ki aciki ne? to inga uban da zai sake dukanta in k'yale"
ta duba Haseenah tace"wuce ki kama hanya ki tafi kafin in tattaka ki er banza me miskilancin tsiya da ruwan ciki, daga ke har uwarki na rasa wa kuka gado dan ba cikin danginmu ba"
sum sum Haseenah ta kama hanya ta fita, tana fita kuwa ta had'u da Haseen ya d'auketa ya ajiye ta a makaranta.
wunin ranan Mummy ta kasa sukuni tunda Aunty tazo, kai komo kawai take tsakanin palour da bedroom ta sak'a wancan ta kunce wannan duk mafita take nema wajan da zata d'au fansa akan Umma, ita yanzu burinta ta fitar da Umma a gidan ne ta salwantar da Haseenah.
Advertisement
can gefe kuwa Saratu ce take ta k'unk'uni kan marin da aka mata ita a dole Mommy taje ta rama mata.
ran Mommy ya dad'a 6aci jin k'ananan kukan da Saratu ke mata, hakan ya sanya daka matsa tsawa tace" wallahi in baki mun shuru ba senaci ubanki, shegiya da tun kafin zuwanta dakin ma Haseenah duka da ba.azo wannan fagen ba, gashi kinsa ancimun mutunci kan wa'yannan mayun mtwxxxx" taja tsuka ta barta wajan.
Aunty kuwa tana shiga wajan Umma nan ta tarar da ita zaune ta tasa abincin da Haseenah ta zuba mata ta zabga uban tagumi, nan itama ta hau ta da masifa kan shurun yayi yawa meyasa zata bari ana cutar da ita, ita dai Umma hak'uri tayita bata har ta samu ta sauko sannan suka fara tattaunawa.
'''WACECE HASEENAH'''
Haseenah 'ya ce ga Alhaji sani mai Atampa, Alhaji sani su uku ne a wajan mahaifiyarsu, maza biyu mata uku, Muhammad, sani, sai kuna autar su Hajiya Zuwaira, su 'yan asalin jihar Gombe ne, sun taso cikin wahalar rayuwa har Allah ya hore musu sukayi karatun boko cikin yardar Allah Alhaji sani ya had'u da ubangida na 'kwarai har shima ya samu ya bud'e mishi nashi shagon, haka Allah ya sanya mishi Albarka har ya fara fita kasashen k'etare yana shigo da yadika da Atampopi.
shiko Alhaji Muhammad wan shi karatu yayi na likitanci shima Alhmdlh.
Zuwaira kuwa auran wuri aka mata ta na da zama a Kano da yaranta uku.
wata rana Alhaji sani na zaune a shago wata matashiyar yarinya suka zo bara tare da wata dattijuwa, tunda ya 'daura idonshi kan yarinyar yaji ta kwanta mishi a rai, nan ya kudiri niyar taimaka musu, haka yayita bibiyarsu har ya gano gidan su da kuma asalinsu, nan ya hanasu fita bara ya ajiye musu komai wanda zasu buk'ata, nan har Allah yasa suka dai daita da wannan budurwa mai suna Hajara har Allah ya shige masa gaba aka d'aura musu aure, wannan budurwa ba wata bace kuwa illa mummy. anyi auransu da wata d'aya Allah yayiwa mahaifiyar mummy rasuwa.
Advertisement
Umma kuwa 'yar abokin baban Abba ce, saboda nutsuwa da hak'urin ta Mahaifin Abba yayi sha'awar had'a zuri'a da shi, lokacin da yayi magana da Abba bai fuskanci wata matsala ba nan aka fara maganar sa rana, lokacin da ya sanar da mummy kuma ba 'karamin tashin hankali ta d'aga ba tana fad'in gaba d'aya auran su shekara d'aya amma zaice ze mata kishiya, Abba ya rasa inda zaisa rayuwar shi, har 'yar rama ya farayi, ganin haka Hajiya Zuwaira wato 'kanwar Abba tazo har gida ta mata wankin babban bargo kuma tace inta ce zata musu rashin mutunci to angulu zata koma gidanta na tsamiya, jin haka ne yasa mummy ta saduda amma ta 'kudiri aniyar seta fitar da mummy kota tsiya kota arziki.
haka akayi biki aka gama komai amma Mummy ko lek'e babu tana 'kunshe a d'aki ita da 'kawayenta, wanda suke ta faman zugata da mata pampo kan karta kuskura da 'kuruciyar ta a cuceta, nan Mummy ta cika tayi fam.
bayan an watse Mummy ta tada rashin arziki, seda Abba yayi mata barazanar saki sannan ta hak'ura, kiran 'kanwar ta tayi a waya wato Mahaifiyar Haseen, nan ta d'auketa ta kaita wajan wani malami kan a salwantar da Umma, yace hakan bazai yuwu ba dan akwai tsari ajikinta sossai, Mummy ba wani yarda tayi ba nan 'kanwarta ta bata shawarar a mayar da Abba mijin tace, hakan kuwa akayi tunda ga lokacin sai abunda Mummy tace yakeyi, tsoronta yake kamar itace mahaifiyar shi.
da haka Mummy da Umma suka samu ciki a tare, duk wata hanya sunbi dan zubar da cikin amma abu ya gagara, haka har lokacin haihuwar su tayi, Mummy ce ta fara haihuwar saratu, bayan sati d'aya Umma ta Haifi Haseenah, nan Mummy ta hana Abba yin komai sai dangin Abba ne suka mata komai.
tun daga wannan lokacin Umma da d'iyarta suke cikin tsangwama da wahala, dan kafin Haseenah ta girma Umma ce kewa Mummy komai, haka suka taso a wahale har Haseenah ta fara wayo, tun tana aiki Mummy na dukanta har ta koya na dole, haka kuma har yanxu Umma ce kawai ta samu sauk'in aiki yanzu Haseenah take fama.
da Abba yayi yunk'urin 'daukar me aiki Mummy tace sam bata yarda ba ai ga Haseenah, ba yanda ya iya haka ya hak'ura.
wannan knan..
'''CIFABAN LABARI'''
ganin kai komo bazai fishe da Mummy ba yasa ta d'au waya ta kira k'anwar tata wato Mahaifiyar Haseen ta bata labarin abunda ya faru, nan ta hauta da bala'i wai zaman me take yi da bazata d'au mataki akan ta ba, da taga wayar bazai mata ba nan ta sanar da Mummy kan ta shirya gata nan zuwa.....
for comments only 08144932303
Advertisement
- In Serial283 Chapters
The Mook Maker
There are many possible fates that can await those whisked away from our world to another. Some became heroes or villains, given the right power to forge their own destinies as they wished. Others, the powerless, became victims, doomed to perish, at the mercy of the cruel world filled with mystical powers they are unprepared for. A lone man that woke up alone under the alien sky was neither of those. He didn't get to choose what he was going to become - a disaster, an unwilling source of intelligent, yet violent monsters, slowly but steadily rising in numbers. Stranded in a foreign land, without even knowing the language, his creations may be the only company he would ever find. He wasn’t powerless. But was he really that much better off? It just took one wrong power.
8 363 - In Serial13 Chapters
Goblin Artist
Cover Art by the talented SocS (https://www.royalroad.com/profile/84137) Even if I grow in strength and somehow avoid dying during a hunt or some moronic tribal war, how long can I really expect to live? Twenty years? Ten? Is this my fate? To struggle to survive every day, only to die after a dozen odd years? Rhys awakes to find himself trapped in the body of a young goblin. In his previous life he was a successful artist, but now he faces a strange new world reduced to the most pitiful of dungeon dwelling monsters and with no survival skills to aid him. His only hope comes from a single sentence he hears during the advancement ceremony: “Some attributes exceed the limits of the current race.” Now his goal isn’t just to survive. He will push through the boundaries of his species to evolve further. The path ahead is long and arduous. Especially for a young goblin trapped in a small dungeon of a dying town. In order to succeed, he will have to forge bonds with those around him and rise to the challenges waiting for him. But will stepping further into the path of a monster really bring him closer to regaining his lost humanity?
8 137 - In Serial33 Chapters
The Silver Dagger
Rejected on her eighteenth birthday, Aiyana accepts that she'll never have a mate and focuses on her dream - to become a veterinarian and pack doctor. Everything is going as planned until a beautiful gray wolf with a near fatal injury is brought in for treatment where she works. He's stuck in wolf form and blind but she can't help liking him. Then someone tries to kill her and the alpha from her home-town sends protection in the form of the one person she'd hoped to never see again.
8 239 - In Serial11 Chapters
Roki
non ethusiastic, bored, no goals and no dreams. Kichiro wasnt feeling the life of being alive until he was dragged into a new world with dungeons and dragons by his beautiful childhood friend, the story will show the adventure of both of these young hearts as they face the greed of men and also the wrath of monsters. but along the way he may or may not met a few individuals that could make him melts physically and emotionally.
8 197 - In Serial15 Chapters
Chasing a Spikey Relationship
This fic has been dropped. There will be no more updates.Chase/Spike x ReaderFirst attempt at a real fanfic, please reveiw!You've been dating Chase for what feels like forever. What happens when only Spike can get you what you really want?A Chase/Spike fic as you've never seen them before!Rated semi mature for possible cursing, and mature themes in future chapters.I obviously do not own Lab Rats or any characters used in this fic. Please enjoy!
8 168 - In Serial29 Chapters
Football Girl
Ayanna Jones has always loved football. She loves playing it, she loves watching it. That's why her friends call her Football Girl.As she settles into a new life with new friends and a new school, she decides to try out for football.The guys on the team give her a hard time especially quarterback, Bryson Stiles. And the coach pushes her harder than the guys and treats her unfairly... But can she prove to them that she deserves to be part of the team?
8 199

