《HASEENAH》Page 7&8
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
story nd written
by👇🏻
Aysher Abbakar (Meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
follow me on wattpad @Aysherabbakar
*long live pml*
*7-8*
Aunty maimuna Mummy ta hango tsaye tana 'kare musu kallo, jikin Mummy ne ya hau tsuma saboda razanar da tayi, dan duk masifar Mummy to Aunty Maimuna tasha gaban ta, cikin 'karfin hali Mummy tace "ke kuma meya kawoki gidannan?"
ba tare da Aunty ta bata amsa ba ta 'karaso yanda suke ta janyo Saratu ta sharara mata mari sannan tace
" fansar marin 'yata da kikayi, kuma kikamun rashin kunya in mari uwarki"
shuru tayi ta rik'e kunci hawaye na zirara, Mummy ce ta fusata cikin tsiwa da tsawa da fara fad'in
" akanme zaki dake ta? ko kina tunanin ke kad'ai kika iya bala'i?"
dariya Aunty tayi sannan tace " ai ita Haseenar da kika sa aka bigeta baiwar uwar wani ko uban wani ce? da kike cewa ta cire kaya ta baki akwai sisin ki aciki ne? to inga uban da zai sake dukanta in k'yale"
ta duba Haseenah tace"wuce ki kama hanya ki tafi kafin in tattaka ki er banza me miskilancin tsiya da ruwan ciki, daga ke har uwarki na rasa wa kuka gado dan ba cikin danginmu ba"
sum sum Haseenah ta kama hanya ta fita, tana fita kuwa ta had'u da Haseen ya d'auketa ya ajiye ta a makaranta.
wunin ranan Mummy ta kasa sukuni tunda Aunty tazo, kai komo kawai take tsakanin palour da bedroom ta sak'a wancan ta kunce wannan duk mafita take nema wajan da zata d'au fansa akan Umma, ita yanzu burinta ta fitar da Umma a gidan ne ta salwantar da Haseenah.
Advertisement
can gefe kuwa Saratu ce take ta k'unk'uni kan marin da aka mata ita a dole Mommy taje ta rama mata.
ran Mommy ya dad'a 6aci jin k'ananan kukan da Saratu ke mata, hakan ya sanya daka matsa tsawa tace" wallahi in baki mun shuru ba senaci ubanki, shegiya da tun kafin zuwanta dakin ma Haseenah duka da ba.azo wannan fagen ba, gashi kinsa ancimun mutunci kan wa'yannan mayun mtwxxxx" taja tsuka ta barta wajan.
Aunty kuwa tana shiga wajan Umma nan ta tarar da ita zaune ta tasa abincin da Haseenah ta zuba mata ta zabga uban tagumi, nan itama ta hau ta da masifa kan shurun yayi yawa meyasa zata bari ana cutar da ita, ita dai Umma hak'uri tayita bata har ta samu ta sauko sannan suka fara tattaunawa.
'''WACECE HASEENAH'''
Haseenah 'ya ce ga Alhaji sani mai Atampa, Alhaji sani su uku ne a wajan mahaifiyarsu, maza biyu mata uku, Muhammad, sani, sai kuna autar su Hajiya Zuwaira, su 'yan asalin jihar Gombe ne, sun taso cikin wahalar rayuwa har Allah ya hore musu sukayi karatun boko cikin yardar Allah Alhaji sani ya had'u da ubangida na 'kwarai har shima ya samu ya bud'e mishi nashi shagon, haka Allah ya sanya mishi Albarka har ya fara fita kasashen k'etare yana shigo da yadika da Atampopi.
shiko Alhaji Muhammad wan shi karatu yayi na likitanci shima Alhmdlh.
Zuwaira kuwa auran wuri aka mata ta na da zama a Kano da yaranta uku.
wata rana Alhaji sani na zaune a shago wata matashiyar yarinya suka zo bara tare da wata dattijuwa, tunda ya 'daura idonshi kan yarinyar yaji ta kwanta mishi a rai, nan ya kudiri niyar taimaka musu, haka yayita bibiyarsu har ya gano gidan su da kuma asalinsu, nan ya hanasu fita bara ya ajiye musu komai wanda zasu buk'ata, nan har Allah yasa suka dai daita da wannan budurwa mai suna Hajara har Allah ya shige masa gaba aka d'aura musu aure, wannan budurwa ba wata bace kuwa illa mummy. anyi auransu da wata d'aya Allah yayiwa mahaifiyar mummy rasuwa.
Advertisement
Umma kuwa 'yar abokin baban Abba ce, saboda nutsuwa da hak'urin ta Mahaifin Abba yayi sha'awar had'a zuri'a da shi, lokacin da yayi magana da Abba bai fuskanci wata matsala ba nan aka fara maganar sa rana, lokacin da ya sanar da mummy kuma ba 'karamin tashin hankali ta d'aga ba tana fad'in gaba d'aya auran su shekara d'aya amma zaice ze mata kishiya, Abba ya rasa inda zaisa rayuwar shi, har 'yar rama ya farayi, ganin haka Hajiya Zuwaira wato 'kanwar Abba tazo har gida ta mata wankin babban bargo kuma tace inta ce zata musu rashin mutunci to angulu zata koma gidanta na tsamiya, jin haka ne yasa mummy ta saduda amma ta 'kudiri aniyar seta fitar da mummy kota tsiya kota arziki.
haka akayi biki aka gama komai amma Mummy ko lek'e babu tana 'kunshe a d'aki ita da 'kawayenta, wanda suke ta faman zugata da mata pampo kan karta kuskura da 'kuruciyar ta a cuceta, nan Mummy ta cika tayi fam.
bayan an watse Mummy ta tada rashin arziki, seda Abba yayi mata barazanar saki sannan ta hak'ura, kiran 'kanwar ta tayi a waya wato Mahaifiyar Haseen, nan ta d'auketa ta kaita wajan wani malami kan a salwantar da Umma, yace hakan bazai yuwu ba dan akwai tsari ajikinta sossai, Mummy ba wani yarda tayi ba nan 'kanwarta ta bata shawarar a mayar da Abba mijin tace, hakan kuwa akayi tunda ga lokacin sai abunda Mummy tace yakeyi, tsoronta yake kamar itace mahaifiyar shi.
da haka Mummy da Umma suka samu ciki a tare, duk wata hanya sunbi dan zubar da cikin amma abu ya gagara, haka har lokacin haihuwar su tayi, Mummy ce ta fara haihuwar saratu, bayan sati d'aya Umma ta Haifi Haseenah, nan Mummy ta hana Abba yin komai sai dangin Abba ne suka mata komai.
tun daga wannan lokacin Umma da d'iyarta suke cikin tsangwama da wahala, dan kafin Haseenah ta girma Umma ce kewa Mummy komai, haka suka taso a wahale har Haseenah ta fara wayo, tun tana aiki Mummy na dukanta har ta koya na dole, haka kuma har yanxu Umma ce kawai ta samu sauk'in aiki yanzu Haseenah take fama.
da Abba yayi yunk'urin 'daukar me aiki Mummy tace sam bata yarda ba ai ga Haseenah, ba yanda ya iya haka ya hak'ura.
wannan knan..
'''CIFABAN LABARI'''
ganin kai komo bazai fishe da Mummy ba yasa ta d'au waya ta kira k'anwar tata wato Mahaifiyar Haseen ta bata labarin abunda ya faru, nan ta hauta da bala'i wai zaman me take yi da bazata d'au mataki akan ta ba, da taga wayar bazai mata ba nan ta sanar da Mummy kan ta shirya gata nan zuwa.....
for comments only 08144932303
Advertisement
- In Serial28 Chapters
Loose Screws
It started once my 'realisticly' Husband, a man that I love, come out from 3D and start stabbing me. And somehow that turn me into a 'Hero', A dimentional hopper, where I pop to each fictions world to gain power to beat up 'The Virus'. The Monster that will not stop eating the entire planet and the being itself until nothing is left behind. And scarily enough, The Virus will be coming to my planet soon. I just hope the Heroes in my planet is enough to stop them, as my power is still not strong enough to beat this unkillable Monster that are called 'The Virus'. Oh, and I also just hope that my clones is enough for me and my love life, call it Narcistic, but I like myself better that the real one now. [ This will be include a Naruto fictions and etc, an x-over to other world. ] Warning: Blood and Gore are included in some of the chapter,
8 769 - In Serial21 Chapters
Leather Liberation// Thomas Hewitt x reader
Y/n is a mask maker reopening her family business in Texas town Poth after years spent away in California. A rather unfortunate meeting with a cannibalistic family is about to change the way she sees her life.This is purely me using an obsession as writing practice. It's going to be dramatic af, and may contain errors. !!!CONTAINS!!!: Gore, murder, death, cannibalism, sexual content , vulgar laungage.
8 141 - In Serial18 Chapters
The First Primordial [DROPPED]
[Story dropped until further notice, I don't currently plan on restarting the story but will leave it as a possible option] During the Creation and before the inception of the Realms, there were 3 beings. Known as Primordials, beings even the God's knew little about that were rumoured to be myths or legends. Follow one of such beings that, given the unflattering name Arthur and the species of Demon, must figure out his place within the realms and find his fellow Primordials. Spending the beginning of creation within what will be called The White Realm then spending an unknown amount of time screwing around in the Demon Realm. Once he finally begins his story, he will be acquainted with a world full of grand vistas, religious nuts and floating rocks which will remove whatever little common sense he had remaining. Of course, there will be no shortage of trouble that will complicate things that (due to a poor ability in making good first impressions) will cause more than a few worlds changing events. These events include the destruction of a church and minor religion, including the death of that religion's God, messing with the reincarnated people and even introducing his own reincarnators along with the slight involvement of a war between the Demon Realm and the Creation Realm. Slow burn story; expect the story to be long with plot being introduced as it goes along. The story will include a main character with an actual mind and personality that will create, learn, and even destroy as the story progresses with an emphasis on what experiencing the other side of most novels, a perspective on that one whimsical god that brings the protagonist from one world to another that is only ever mentioned in the starting chapter. [PS- This will be my first time writing, so advice, tips and critiques will be appreciated. The release schedule is a bit iffy and unreliable but will mostly be every Sunday]
8 99 - In Serial12 Chapters
Vice Captain of Straw Hat Pirates
In the world of pirates, a young man reincarnates into a completely ordinary person's body. But coincidentally, he encounters Monkey D. Luffy. Hungry for adventures but also scared of death, he joins the Straw Hat Pirates as the vice-captain. ............ Straw Hats will follow the same routes with a lot of new changes.
8 145 - In Serial17 Chapters
No Phones In Class
Where Ryan gets detention for using his phone in class, but was it really such a bad thing?..
8 205 - In Serial27 Chapters
lovely | poetry
Sometimes my voice dies in my throat, buries itself beneath waves of crippling suffocation, burns itself out as cold hands tear at my laced skin. I have smiled while my eyes have cried and pleaded, my wrists numb, my lips wobbling and blue, and stars escaping this dark night that I'm trapped in. I long for a darkness that gives way to light. But I do feel the warmth of petals gathering and scattering in my cold bones, and imagine the touch and the sweetness of a kiss, and my heart rises to the surface of this sea and finds a sky painted by passing artists remaining far above our heads. I'm breathing out all the words I've kept locked under the pages of my breaking mind. And by doing so, I'm going to heal.TRIGGER WARNINGS: depression, anxiety, self harm, suicidal thoughts, OCD, panic attacks
8 114

