《HASEENAH》Page 1&2
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
story nd written
by👇🏻
Aysher Abbakar (Meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
follow me on wattpad @Aysherabbakar
'''BISMLLAHIR-RAHMANIR RAHEEM'''
*Godiya ta tabbata ga Allah mai kowa mai komai, wanda ya bani ikon fara rubuta wannan littafi, wannan littafi ba nayi shi bane saboda wata ko wani, wani littafi kirkirarren labari ne dan isar da sak'on da yake kunshe cikin sa, ina me bada hak'uri cewa duk wanda wannan labari yayi dai-dai da rayuwarta/shi, to yayi hak'uri ba saboda shi nayi ba, da fatan zaku bani goyan baya, kuma ina rok'o duk wanda yaga nayi kuskure cikin wannan littafi to dan Allah a gyaramun, dan kowani d'an Adam ajizi ne, Allah yasa mu dace, ya bamu ikon cin duk wani jarabawar rayuwa.*
jinjina gareku k'ungiyata kuma abar alfaharina, kun taka rawar gani 'kwarai a rayuwata, wajan yimun gyara ko fad'an gaskiya bisa duk wani kuskure dana aikata, ina yinku.
*long live pml*
wannan littafin na sadaukar dashi ga duk wani wanda ya/ta fiskanci matsin rayuwa, Allah yasa mufi karfin zuciyarmu.
*1-2*
k'aran kwanuka da cokula kawai kake jiyowa daga cikin kitchen, jin abu yak'i k'arewa ya sani k'arasawa da sauri dan duba meke faruwa.
Wata matashiyar budurwa na hango wanda bazata wuce shekara sha hud'u ba sanye cikin wata kod'add'iyar dogon riga kai kace mai aikin gidan ne. kiran da naji ana k'wallawa ne ya sani razana da sauri na juya dan gani wani k'ato ne haka da wannan muryar? abun mamaki mace ce ingarma doguwa ga jiki ga k'iba kai kace 'yar wasan danbe ce, da sauri na matsa na raku6e dan ganin ta nufo yanda nake gadan-gadan.
runtse ido na kawai nayi dan sauraron abunda zai biyo baya, 'karan saukan marin da naji ne ya sani bud'e idona a razane dan ganin meke faruwa?
Advertisement
matar na gani ta shak'e wannan yarinyar kamar wacce zatayi dambe da sa'ar ta, daga hannu ta sake yi ta sharara mata wasu tagwayen mari lokaci d'aya sannan ta fara magana cikin dakakkiyar muryarta tace" haseenah, dan ubanki ba gyaran palour na na sakaki ba shine kikazo nan kika rashe dan kin mayar dani 'yar iska ko?"
cikin sheshshe'kar kuka tace"Mommy wlhy ba haka bane, dama inaso in 'karasa wa umma na wanke-wanke ne, batajin dad'i ne shiyasa"
salati ta kama yi tare da fad'in" jimun munafuka, wato saboda bani na haifeki ba shine bazaki mun abunda na saki ba ko? to ki barshi tunda ke ban isa da ke ba ai na isa da ubanki, shi zaizo yamun gyaran palour daga nan ya d'auramun girkin rana"
da sauri Haseenah ta tsame hanunta daga cikin sink d'in tace"yi hak'uri mommy wlhy zanje inyi ynxu"
Haseem ne ya k'araso da sauri dan shigowar sa kenan yaji hayaniya na tashi, ko bai tanbaya ba yasan Mommy da Haseenah ce, da murmushi ya k'araso ya dubi Mommy yace" ah mommy dama tunda naji hayaniya nasan da 'yar taki ce"
a fusace mommy ta dube shi tace" Allah yamun tsari na haifa wannan me kama da mayun, ai gwanda na koma ga Allah ban haihu ba, yarinya daga ita har uwarta munafukai, se anyi magana su fara k'ifi-k'ifi da ido sekace an barbad'awa kifi gishiri" ta k'arasa maganar tana d'aka wa Haseenah duka had'e da hankad'ata waje tace
" wuce shegiya kin tasa ni a gaba sekace wanda nake baki kalmar shahada"
da sauri ta wuce tana share hawayen bak'in ciki dan batasan me suka tsarewa mommy ba, dan tun tasowarta haka ta rayu cikin tsangamar mommy, sekace ba matar ubanta ba, to umman ta ma mommy bata bari ba ballan tana ita haihuwar yau.
Advertisement
Haseem ne ya kalli mommy duk ranshi a jagule ya sanyaya murya yace"haba mommy, dan Allah kina rangwanta ma yarinyar......
tsawa ta daka mishi tare da nuna shi da yatsa tace" kai ko uwarka kaga dai k'anwata ce ko? to batamun katsalandan a rayuwar gidana, shiyasa ma kaga duk munfi shiri da ita, saboda halinmu yazo d'aya, dan haka ka fita hanyata, inba haka ba wlhy zan sa6a maka".
sanin halin mommy ya sashi yin shuru ba tareda yace komai ba ya nufa hanyar waje yana mai Allah wadai da halin su mommy.
Haseenah kuwa shiga toilet d'in tayi ta fara aikin wanke wa, tana gamawa ta fito bedroom ta gyara ta mopping ta had'a burner na turaren wuta, hakama ta gyara palour sannan ta shiga kitchen d'in mommy dan had'a mata breakfast ita da 'yar lelenta wato saratu, chips ta soya musu sannan ta dama kunun gyad'a ta tafasa lipton, tana gamawa komai ta juye a flask ta gyara ko ina sannan ta fito, gajiya ne ya rufe ta gashi tabar ummanta can ba lafiya, kuma ko abinci bata girka musu ba.
kitchen d'insu ta koma ba tare da ta 'karasa wanke-wanken ba ta 'daura musu lipton ta musu d'umamen sauran tuwon jiya sannan ta fita da sauri ta nufa d'akin umman ta.
zaune ta sameta kan carpet ta jingina bayanta da gado tana mayar da numfashi a hankali, ajiyewa Haseena tayi sannan ta dubi umman tana mata sannu, abincin ta zuba musu nan suka ci . kowa shuru yayi cikinsu babu mai magana kowa da tunanin da yake a ransa.
haseena ne ta dubi umma sannan tace"umma ya zamuyi da maganan kud'in makaranta na, gashi jibi zamu fara exams"
shuru umma tayi daga bisani tace" ki d'au 'dankunne na kije kisiyar a shagon da mukaje dake na siya, saiki siya duk abunda zaki buk'ata da canjin bayan kinbiya school fees d'in".
jikin Haseena ne yayi sanyi duk taji ba dad'i, umma ta kula da hakan hakan ya sata cewa"ko bakiji abunda nace bane?"
ahankali ta mik'e ta saka hijabinta da d'au d'ankunnen ta fita, a gate sukayi kici6is da Haseem zaune kan mota, d'auke kai tayi kaman bata ganshi ba, ganin haka ya sashi 'kwalla mata kira, kaman bazata juya ba sekuma ta juyo tare da amsawa, gaidashi tayi sannan tayi shuru.
dubanta yayi sannan yace"ina zakije da safen nan?" shuru tayi batace komai ba, ganin batada niyan magana ne ya sashi saka hannu cikin aljihu ya ciro wata 'yar paper ya mik'a mata sannan yace "dama receipt na school fees d'inki ne gashi nan seki adana"
binshi tayi da ido ba tare da ta amsa ba, kama hanunta yayi ya saka mata sannan ya juya ya bud'e bayan motar shi ya ciro wata 'katuwar farar leda ya ajiye mata yace seki d'au wannan ki tafi da ita taki ce, tunda yau bakida niyar magana miskilanci ya motsa"
yana gama fad'in haka ya shiga motarsa yabarta nan tsaye.
ba yanda ta iya haka ta d'au ledar ta juya ta koma cikin gida.
a harabar gidan sukayi kici6is da mommy, sunkuyar da kai tayi gabanta na fad'uwa dan tasan ba makawa in mommy taga kayan hannunta to wani sharrin ne zai biyo baya.
hakan ya sata 'kara sauri dan gudun kar momny ta kula da abunda ta rik'o.
kaman daga sama taji andaka mata tsawa, ba makawa tasan mommy ce hakan yasa ta fara kyarma kaman zatayi fitsari, dubanta mommy tayi sannan tace......
for comments 08144932303
Advertisement
- In Serial35 Chapters
Heretic King
The world ends, game system is invoked, yada yada. After the system set by God causes Thomas Crowe to go crazy, he swears he will kill God, thus getting deemed a Heretic. How will the story go from there? Will he slay God or will he die trying to resist?Mature cause curse words will be used and sex scenes described.. More tags as the story develops.There is references and terms used from other stories. I will link the references If I feel it's not as obviousIf you can give me your opinions in the comments it's my first time writing and I'd love some feedback.Credits to Yang_God_Of_Games_And_Power for the cover!
8 213 - In Serial8 Chapters
Sacrifice
Michael Strong never had a very good life nor he thinks he has done anything special. But then, something comes his way. Something that will finally change everything that was bad. Something which will give him the meaning he always wanted. But every meaning requires a sacrifice...
8 196 - In Serial40 Chapters
The Mournful Path
[FINISHED]Arran Stormcleaver is dead. His ward and former student Yara runs away from home. Her grief and heartache from losing her only parental figure proving too much for her to deal with at home and on her own. Despite all this she continues to uphold her position in the Knights of Ash as a professional dragon huntress while travelling the road, all the while hoping that maybe the issue driving her will resolve itself. (CW: Harsh Language, Violence, themes of grief and depression)
8 56 - In Serial11 Chapters
The Condemned Child
Ten years ago, the parents of Shinsato Katsuro were brutally killed by an army of demons known as Shifters. Now, at sixteen, Katsuro is determined to enter the Celestial Military Academy, begin training for the war effort and ultimately save humanity from this perpetual, brutal conflict between humans and Shifters. With many different islands, cultures and factions to explore, Katsuro will have to work his hardest to unlock the truths behind the Runic stones, the Duobeast system and the Condemned Children, a special group of humans marked by the Prince of the Shifters before his mysterious disappearance. Studying hard and working out every day for years, Shinsato and his childhood best friend Naomi are finally prepared to set off on their sacred mission.
8 153 - In Serial6 Chapters
Shinome
Damian has the perfect family life. He never had problems with the way how his life was going. But it is said that circumstances can change very quickly. Damian will face ups and downs, and with new people entering his life, the plot of his life thickens. Damian will learn several lessons from what not to say to a girl to who he can trust. He better find a way to deal with life quick because as bumpy as his life seems at the present it won't get smoother. Note: I may cease to write newer chapters soon. This story was a test of certain ideas that I will be putting to use in a new book that I will be writing.
8 84 - In Serial51 Chapters
Marriage in Corrosive Love
If Shen Qingkong knew that Mu Linxuan married her just for her face similar to his first love, she wouldn't marry him no matter how much she loved him! This might be a wrong marriage, but how could she just give up her love for him so easily? Who would be the final winner in this corrosive love?... Welcome to read all of the realesed chapters of Marriage in Corrosive Love on Flying Lines.
8 354

